Thursday, 19 September 2013

HUKUNCE-HUKUNCEN SALLAR IDI BABBA DA LAYYA


HUKUNCE-HUKUNCEN SALLAR IDI BABBA DA LAYYA
Daga Auwal Zakari Ayagi Chairman Al’Azmiyyah Islamic Foundation Kano State
GSM: 08090987314 www.sautulazmiyyah.blogspot.com Email:auwalzakari@gmail.com

SALLAR IDI BABBA
Sallar Idil Dhuha (Sallar Idi Bbba) Sunnace mai karfi. Ubangiji Mai Girma da daukaka shi ya yi umarni da ayita cikin Littafinsa Mai Girma in da ya ke cewa: “Hakika mun baka Alkausara, kayi Sallah ga Ubangijinka, ka soke abin yankanka” (Suratul Kausar aya ta 1-2). Manzon Allah Alaihissalam ya yi ta kuma yayi umarni da yinta, yana fita don yin Sallar tare da Mata da kananan yara, Sallar tana kara Imani da tsoron Allah. Ana yin tane a ranar goma ga Zulhijja.
          Lokacin Sallatarta: Lokacin da ake Sallatar Idin  shine daga lokacin da Rana ya dago, ana so asaurari huduba yayin da aka kamala Sallar.
          Ladaban Sallar Idi: Ladubban Sallar idi sune kamar haka:
1.              Wanka da sanya sababbin tufafi ko mafiya kyau, tare da fesa turare, saboda hadisin da ke cewa: Manzon Allah ya umarcemu a ranakun idi biyu da musanya tufafi kyawawa, mu fesa turare mafi kamshi….,(Hakim)
2.              Yana daga Ladabanta canja hanyar da aka tafi yayin dawowa, Saboda Shugaba Alaihissalam  ya kasance yana canja hanya a ranar idi (Buhari)
3.              Yin Sallah a sarari ma’ana ba a cikin masallaci ba, sai dai idan da lalurar ruwa ko makamancin haka, to sai ayi a cikin masallaci.
4.              Taya juna farin ciki tare da fadin musulmi ga dan’uwansa, Allah ya karba agareni ya karba a gareka. Kamar yadda aka rawaito Sahabban Manzo sun kasance idan sun hadu da yan’uwansu suna fadin Allah ya karba garemu da gareka (TAKABBALALLAHU MINNA WA MINKA).
YANDA AKE YIN SALLAR IDI
Yadda ake yin Sallar Idi shine, mutane su fito izuwa masallaci yayin da rana tafito, sai liman ya tsaya don Salla batare da kiran Salla ko ikama ba, zaiyi Raka’o’i biyu, a raka’ar farko zai yi kabarbari guda bakwai, tare da kabbarar harama, mutanen da suke bayansa za su rika yin kabbara a duk yayin da yayi kabbararsa, sai ya karanta Fatiha da Suratul A’ala, a bayyane. A raka’a ta biyu, zai yi kabarbari guda shida tare da kabbarar tsayuwa, zai karanta Fatiha da suratul Jashiyati ko suratul Shamsi, idan yayi sallama sai ya tashi don yiwa mutane huduba. Bayan ya budeta da yabo da Allah, da godiya a gareshi, sai ya kwadaitar da mutane akan falalar yin Layya da bayyana musu hukumce-hukumcenta da yanda a ke yenta da kuma lokacin da ake yita, yayin daya kamala huduba sai mutane su taya junansu murna, sannan su koma zuwa gidajensu, ba za ayi sallar nafila ba bayan sallar Idi ko kafinta, sai dai in wanda sallar Idin ta kubuce masa ne, sai ya sallaceta raka’a hudu, saboda fadin Ibn Mas’ud Allah ya kara yarda a gareshi: “Wanda Sallar Idi ta kubuce masa ya sallaci raka’a hudu, amma wanda ya riski wani abu tare da Liman koda zaman tahiya ne to sai ya tashi bayan liman yayi sallama ya sallaci raka’a biyu.
HUKUNCE-HUKUNCEN LAYYA
MA’ANAR LAYYA: Al’udhhiyyati wato Layya a shari’ance tana nufin wata dabba da ake yankawa ranar Sallar Idi Babba don neman kusanci ga Allah madaukakin sarki.
HUKUNCIN LAYYA: Layya Sunna ce wajiba akan dukkan musulmin da Allah ya horewa, Allah ta’ala Yana cewa: Kayi Sallah ga Ubangijinka kuma kayi yanka. (Kausar:2) Akwai Hadisai masu yawa da sukayi bayani a kan layya, daga cik akwai fadinSa Annabi Alaihissalam wanda ya yi layya kafin sallar idi ya sake (Layyar) (Turmizi ya rawaito ya inganta shi).
FALALAR DA KE CIKIN LAYYA: Layya tana da falala maigirma, sabo da fadin Annabi Alaihissalam cewa: “Babu wani aiki dad an Adam zaiyi a ranar Idi da Allah yafiso fiye day a kwararar da Jini, (Layya) har zuwa karshen hadisin ibn majah. Da kuma fadinsa yayin da aka tambayeshi game da Layya Sai yace: Sunnar Baban ku Annabi Ibrahim ce, sai suka ce: mai ya ke garemu da ita, Sai Manzo Yace: ga dukkan gashin ta akwai (Hasna) Lada, sai sukace Ga buzun ta (Fata) sai yace ga dukkan gashin fatan akwai Lada.
HIKIMAR YIN LAYYA
ü  Neman kusanci ga Allah, domin fadin Allah maigirma da daukaka “Kayi Salla ka soke abin yankanka” (Suratul Kausar, Aya ta 2) da fadin sa cikin Suratul An’am Aya ta 162-163. Cewa: “Kace hakika Sallah tad a yankana da Rayuwata da mutuwata ga Allah suke ubangijin talikai, bashi da abokin tayayya.
ü    Raya Sunnar shugaban masu kadaita Allah Annabi Ibrahim Alaihis Salam, yayin da Allah yayi wahayi gareshi daya yanka dansa Annabi Isma’il, sai aka fansheshi da Rago, ya yankashi don sauyi daga dan nasa, Ubangiji yace: “Sai muka fansheshi da abin yanka mai girma” (Suratul Saafaat, Aya ta 107)
ü  Yalwatawa iyali ranar Idi, ta ciyar da talakawa da mabukata.
ü  Godewa Allah madaukakin sarki bisa horewar dabbobin Ni’ima garesu.
Layya tana wajaba kan wanda ya cika sharudda masu zuwa:
ü  Ya kasance da ba bawa ba, (namiji ko mace).
ü  Tana zama sunna kan mutum a kansa da iyayensa, idan talakawa ne, da Yayansa Maza idan ba su balaga ba, da yayan sa mata idan ba su yi aure ba.
ü  Kada ya kasance mahajjaci, domin shi mahajjaci, hadaya ce a kansa ba Layya ba.
ü  Ya zamaba matalauci ne ba. Ma'ana kada ya zama yana bukatar kudin yin layyar domin biyan wasu bukatu nasa. Amma idan zai iya cin bashi ya yi layyar, to ya yi, idan ya san zai iya biya, ba tare da takuruwa ba. Wasu malaman suka ce kada mutum ya ci ba shi domin yin layya.

DABBOBIN DA AKE YIN LAYYA DA SU
Dabbobin da akeyin layya da su akwai Rakumi, Sa, Rago da Taure, dakuma  matansu. Rago sai wanda ya shekara, Taure kuwa sai ya shiga shekara ta biyu. Sa kuma sai wanda ya kai shekaru uku. Shi kuwa rakumi sai ya kai shekara biyar.
A wajen layya,  Rago ya fi falala (sai tunkiya), sai Taure (sai akuya), Sai kuma Sa (sai Saniya), bayan Sa sai kuma saniya, Sannan Rakumi (sai taguwa).
A cikin kuma dukkan dabbobin da aka ambata anfifita mazansu a kan matansu, lafiyayyun su akan marasa Lafiya, wadanda suke iya yin barbara a kan fidiyayyun su, Sai dai idan fidiyayyun sun fi kitse ne sai a yi da su.
Sharuddan ingancin layya
1.     Dole ne a yi yankan da rana, bai inganta ba a yi Layya da daddare ba. Rana tana farawa ne daga ketowar alfijir, Amma  game da layyar sai liman (shugaba) ya  yanka nasa abin layyar sannan sauran jama’ar gari su yanka nasu, ba kawai da an wayi gari ba sai kowa ya yanka na sa ba, idan mutum yayi yanka kafin liman ya yanka nasa, layyarsa ba ta yi ba.
2.     Mai yin yankan dole ne ya zama Musulmi, yankan kafiri bai halatta ba, koda kuwa ma'abocin liittafi ne (Ahlul-kitabi)
3.     Ya halatta a yi gamayya a cikin layya idan dabbar layyar ta zama Rakumi ko Saniya. Sannan kuma kada adadin masu gamayyar ya wuce bakwai. Idan suka wuce bakwai, bai halatta su yi gamayya a dabba daya ba. Dalili a nan shi ne Hadisin Jabir (RA) da yake cewa: Mun yi layya tare Manzon Allah SAW) a shekarar Hudaibiyya, kowace taguwa mutane bakwai,saniya ma mutane bakwai (Muslim ya ruwaito).
4.    Dole dabbar layyar ta kasanceta kubuta daga cututtuka ko aibubbuka da sukea fili karara. Saboda Hadisin da Bara (RA) ya ruwaito dagaManzon Allah (SAW) ya ce: Manzon Allah (SAW) ya mike tsaye cikinmuyace: Dabbobi hudu bai halatta a yi layya da su ba. Mai ido daya wadda rashin idon ya fito fili. Marar lafiya, waddarashinlafiyarta ya fito fili, ko Gurguwa, waddan gurguntakarta fito fili, wadda ta karye kafa da kuma wadda bata da bargo (Abu Dauda ya ruwaito), da kuma Hadisin da aka ruwaito daga Aliyu (RA) cewa: Annabi (SAW) ya hanayin layya da dabba mai gutsurarren kunne da gutsurarren kaho (Abu Dauda ya ruwaito).
Haka nan ba za a yi da mai gutsurarriyar kafar gaba ko ta baya ba, ko marar ji ko mai warin baki,ko wadda ba ta yin kuka, ko marar bargo,komai gutsurarren bindi ko marar lafiyar da rashin lafiyarta yafito filiko mahaukaciya, ko madauwamin hauka, kogurguwa ko ramammiyar da ramarta tafito fili. Dukkan abubuwanda aka ambata a baya, idan masu sauki ne, babu laifi,

saia yi layya da ita. Haka nan bai halatta yi layya da dabbar da kahonta ya karye yake yin jini ba. Ko wadda kashi daya daga cikin uku na bindinta ya gutsure. Amma idan wanda ya gutsure bai kai kashi daya cikin uku ba, babu laifi.
Haka nan  kuma wadda ta rasa hakora biyuko fiyeba domin yarinta ko tsufa ba. Amma idan hakori daya ta rasa, babu laifi. Haka nanidan fiye da kashi daya cikin uku na kunnenta ya tsage, ba a layya da ita.
Wadanan sune kadan daga cikin bayanan hukumce hukumce game da Sallar idi Babba da layya, abin da akaji na daidai daga Allah ne, na kuskure kuwa daga gareni ne.
Allah ya kara tsira da aminci ga shugaban halitta cikamakin Annabawa da ahalin gidansa, da sahabbansa da dukkan wadanda suka bishi da kyautatawa, A kulu kauli haza wa astagfirullaha li wa lakum, wassalamu alaikum warahamatullahi ta’ala wa barakatuhu.

Wednesday, 13 March 2013

BAYANI AKAN MATAN DA AKA HARAMTA AURENSU



BAYANI AKAN MATAN DA AKA HARAMTA AURENSU
Matan da aka haramta aurensu sun kasu kasha biyu (2).

1.       Wadanda aka haramta aurensu na har abada.

2.       Wadanda aka haramta aurensu zuwa wani lokaci.

WADANDA AKA HARANTA AURENSU HARAMCI NA HAR ABADA

Matan da  aka haramta aurensu haramci na har abada sun kasu kashi 3

a)      Wadanda aka haramta aurensu ta hanyar dangantaka.

b)      Wadanda aka haramta aurensu ta hanyar shayarwa.

c)       Wadanda aka haramta aurensu ta hanyar Surukuta.

a)      WADANDA AKA HARAMTA AURENSU TA HANYAR DANGANTAKA

Wadanda aka haramta aurensu ta hanyar dangantakasun kasu kashi bakwai (7) :-

        I.            UWA KO MAHAIFIYA:- wannan ta hada da wadda ta haifi mutum, ko ta haifi mahaifin mutum, ko ta haifi mahaifiyar mutum wato kakar mutum ta wajen uwa ke nan, ko ta wajen uba zuwa abinda ya yi sama.

      II.            ‘YA:- “yard a mutum ya Haifa ko ya haifi mahaifinta ko kuma mahaifiyarta, wato jikar mutum kenan ta wajen “da ko “ya izuwa abinda ya yi kasa.

    III.            ‘YAR UWA:- Abin nufi anan shine , wadda ta ke uwa “daya uba “daya, kokuma uwa “daya uba kowa da nasa, ko uba “daya uwa kowa da tasa. (‘kanwar mutum ko yayaryasa kenan).

    IV.            GWAGGWANKA:- wannan itace ‘yar uwar mahaifi( ma’ana yayarsa ko ‘kanwarsa),ko ‘yar uwar kakan mutum na wajen uwa ko na wajen uba da abinda ya yi sama.

      V.            YAKUMBONKA:-  wannan itace  yar uwar mahaifiya( ma’ana yarta ko “kanwarta). ko ‘yar uwar kakar mutum ta wajen uwa ko ta wajen uba da abinda ya yi sama.

    VI.            ‘YAR DAN UWANKA:- wannan itace ‘yar  yayanka(wanka) ko kaninka wanda kuke uwa “daya uba “daya ko uwa daya uba kowa da nasa, ko uba “daya uwa kowa da tasa.

  VII.            ‘YAR ‘YAR UWARKA:- abin nufi shi ne  ‘yar ya ko kanwar mutum wadda suke uwa “daya uba “daya, kokuma uwa “daya uba kowa da nasa, ko uba “daya uwa kowa da tasa.

Wadannan sune kashi bakwai na matayen da aka haramta aurensu ga mutum,haranci na har abada ta hanyar dangantaka kamar yanda ya zo a cikin Alkurani, a cikin Suratun Nisa’I aya ta ashirin da uku(23).

b)      MATAN DA AKA HARAMTA AURENSU TA HANYAR SHAYARWA.

Wadanda aka haramta aurensu ta hanyar shayarwa su ma sun kasu kashi bakwa (7):-

        i.            BABARKA TA SHAYARWA:- ma’ana wacce ta shayar da mutum,ko kakar mutum ta shayarwa        zuwa abinda ya yi sama.

      ii.            YAR UWARKA TA SHAYARWA:-  Ma’ana wacce aka shayar da mutum tare da ita lokaci daya ko kuma lokuta  daban-daban. Matukar dai wadda ta shayar da ita, ita ta shayar da kai, haramun ne ka aure ta.

Wadannan sune haramcinsu ya tabbata a cikin AlKurani Mai Girma a cikin Suratul Nisa’I aya ta ashirin da uku (23).

    iii.            YARKA TA SHAYARWA:-  Abin nufi anan shine ,”yar da matar mutum ta shayar da ita, ta zama “yar mutum kenan ta shayarwa. Domin haka haramun ne ya aure ta.

     iv.            GWAGGWONKA TA SHAYARWA:- Abin nufi anan shine; Yar uwar mijin matar da ta shayar da mutum, ta zama gwaggwon mutum ta shayarwa. Domin haka ya zama haramun mutum ya aure ta.

       v.            YAKUMBONKA TA SHAYARWA:- ma’ana ‘yar uwar matar da ta shayar da mutum, ta zama yakumbon mutum kenan. Saboda haka haramun ne mutum ya aureta.

     vi.            ‘YAR ‘DAN UWANKA NA SHAYARWA:- wannan na  nufin ‘yar wanda aka shayar da mutum tare dashi ko jikarsa. To haramun ne ya aure ta.

   vii.            “YAR “YAR UWARKA TA SHAYARWA:- ma’ana yar wacce aka shayar da mutum tare da ita ko kuma jikarta itama haramun ne ya aureta.

Wadannan kuma haramcinsu ya tabbata ne  a Hadisin da Bukhari da Muslim su ka ruwaito shi. Wanda Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama yake cewa: “ Shayarwa tana haramta abin da dangantaka take haramtawa”.

FADAKARWA

Malamai sun yi sabani a kan shayarwa da take haramta aure, amma zancen da ya fi inganci cikin zantuttukan malaman shine; haramcin baya tabbata sai in har yaron ya sha nonon sau biyar kuma ya shay a koshi ya saki . in an jima ko kuma wani lokaci na daban ya sake sha.sannan kuma ya zama lokacin ba zai iya cin wani abinci ya koshi ba sai nonon.

                Dadin dadawa , wannan haramcin ya takaita akansa  ne shi kadai da ya sha nonon. Baya hadawa da sauran danginsa ,kamar ‘kannensa ko yayyensa ko iyayensa. Su duk wannan haramcin bai shafesu ba.

WADANDA AKA HARAMTA AURENSU TA HANYAR SARAKUTA.

Matan da aka haramta su ta hanyar sarakuta su hudu ne(4):

                    i.            Mahaifiyar matar mutum ko kakarta: ta wajen uwa ce ko ta wajen uba da abinda ya yi sama, duk baya halatta mutum ya aure su.

                  ii.            Agolar mutum: abin nufi shine “yar matar mutum, wadda ta Haifa da wani mijin daban. Shin ta zo da ita gidansa ko bata zo da ita ba? Duk dai haramcin daya ne. Amma idan mutum bai sadu da uwar ba, “yar ta halatta ya aure ta.

                iii.            Matar ‘Dan Cikin Mutum Ko matar Jikansa: Sawaun na wajen “da ne ko na wajen “ya duk dai bai halatta ya aure taba.

                 iv.            Matar mahaifin mutum: Wannan ya hada da wanda ya haifi mutum ko kakansa na wajen uwa ko na wajen uba duk dai bai halatta a mutum ya auri matansu ba.kamar yadda ya zo a cikin Suratun Nisa’i, aya ta (23).

Duk wadannan suna haramta ne da zarar an daura aure, sai dai agola wadda ita sai an sadu da mahaifiyarta haramcin yake tabbata.

Wadannan da aka lissafa a sama sune suka haramta mutum ya aure su haramci na har abada , koda kuwa daga shi saisu ya rage a duniya.

BANGARE NA 2 WADANDA AKA HARAMTA AURENSU ZUWA WANI LOKACI

Matan da aka haramta aurensu zuwa wani lokaci su goma (10) ne gasu kamar haka:

        i.            Hada tsakanin “yan uwa guda biyu: wadanda suke uba daya uba daya, ko kuma wadanda suke uba daya , uwa kowa da tasa. Ko kuma uwa daya uba kowa da nasa. Saboda ayar da ta zo a cikin suratun Nisa’I aya ta (23).

      ii.            Hada mace da “yar uwar mahaifinta ko “yar uwar mahifiyarta: Saboda manzon Allah Sallallahu alayhi wa sallama yace:” Kada a auri mace a hada ta da “yar uwar mahaifinta. Ko “yar uwar mahaifiyarta.(Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

    iii.            Matar da take da aure: ba za’a sake daura mata wani auren ba,har sai idan sun rabu da mijinta sannan ta yi idda. Saboda ayar da ta zo a cikin suratun Nisa’I. Aya ta (24).

     iv.            Mace mai idda (ta saki) ko takaba( ta mutuwar miji): su ma wadannan ba za’a daura musu aure ba har sai sun gama idda ko takaba kamar yadda ya zo a aya ta (235) a cikin suratul bakara.

       v.            Matar da aka sake ta saki uku: Ba za’a sake daura mata aure da mijin da ya sake ta ba, har sai idan tayi wani auren da wani mijin daban ya sadu da ita. Saboda abinda ya zo a cikin suraratul Bakara aya ta (230) da kuma hadisin da  wata mata ta zo wurin Manzon Allah Sallahu alaihi wa sallama ta fadama sa cewa tana son ta koma wajen tsohon mijinta da ya sake ta saki uku (3) amma miji na biyun bai sadu da ita ba.Sai manzon Allah sallahu alaihi wa sallama yace:” A’a sam ba za ta koma wajen na farkon ba . har sai na biyun ya sadu da ita kamar yadda na farkon ya sadu ita.(Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

     vi.            Mace ta biya: Baya halatta mutum ya auri mace ta biyar (5) alhalin yana da mata hudu har sai sun rabu da wata ko kuma wata ta mutu daga cikin matan sa . kamar yadda ya zo a cikin Suratun Nisa’I aya ta uku(3).

   vii.            Auren mazinaciya: Wasu daga cikin fakihai suna ganin baya halatta mutum ya auri mazinaciya har sai ta tuba ta yi istibrai, hujjarsu kuwa ita ce aya ta uku a cikin Suratun Nur.

 viii.            Auren baiwa ga “da: Mafi yawancin malamai sun ce baya halatta ga “da auri baiwa said a sharudda guda biyu(2).

 (a)  Tsoron fadawa zina

 (b)  rashin samun wadatar auren “yar kamar yadda aya ta ashirin da biyar(25) a cikin suratun Nisa’I ta nuna.

     ix.            Mai harama da aikin hajji:  Mafi yawancin fakihai sun tafi akan cewa aure baya halatta ga mai harama da hajji.Saboda manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama yace kada mai harama da hajji ya aura ko ya aurar.(Muslim ne ya ruwaito).

       x.            Auren macen da bata bin addinin sama:  Ma’ana wacce ba musulma ba, ba bayahudiya ba, ba kirista. To baya halatta ga musulmi ya aure ta har sai ta musulunta ko ta shiga addinin yadudanci mko kiristanci. Saboda ayar da take cikin suratul Bakara aya ta (221).

Wadannan sune wadanda aka haramta auren su amma ba haramci na har abada ba.Ma’ana da zarar matsalolin da lissafa sun gushe, to ya halatta a aure su. Wallahu ta’ala a’alam.

Wa Sallallahu wa sallama ala Nabiyyina Muhammadin wa ala ahlihi wa sahbihi wa man tabiahum bi ihsanin ila yaumiddin.

LITTAFAN NAZARI SUNE:

1.       AZZAWAJ NA DR. MUHAMMAD IBRAHIM HAFANAWI.

2.       MINHAJUL MUSLIM NA SHEIKH ABUBAKAR AL-JAZAIRI.