HASKEN RAYUWATA
Tarihin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam
Rayuwa, Darussa Da Qyawawan
Halaye
Wallafar
COMRADE AUWAL
ZAKARI AYAGI
(Barden Ayagi)
Haqqin Mallaka (M)
Auwal
Zakari Ayagi (Barden Ayagi)
Lambar Waya: 07038775781
Bugu Na Xaya 2026/1447
TSARAWA
DA BUGAWA
Al-Azmiyya Islamic
Foundation: No. 313 Al’Mustapha
House Kadawa Western Bypass AL’EEMAAN Medicine Store Building, Adjacent to Gwarzo Road Kano.
E-mail:
auwalzakari@gmail.com
www.sautulazimiyya.blogspot.co.uk/
GSM: 07038775781, 08023615685
SADAUKARWA
Na sadaukar da wannan
Littafi ga Mahaifana
Marigayi Alhaji Zakari Muhammad Usman Ayagi
(Allah ya gafarta masa) da Mahaifiyata Hajiya Rakiya Usaini Lawan (Inna) Allah
ya qara mata Lafiya, Amin.
Da
sunan Allah mai yawan Rahama Mai Jin qai, Tsira da Aminci su qara tabbata ga
shugaban halitta Annabi Muhammad Tsira da Aminci su qara tabbata a gareshi.
Da farko, ina miƙa godiya ta musamman ga
Allah Maɗaukakin Sarki,
wanda Ya bani ikon kammala wannan littafi cikin salama da nutsuwa. Shi ne Mai
bai wa bawa ƙarfin
tunani, hikima da nutsuwar zuciya, Ya kuma bayyana masa abin da zai amfane shi
da al’umma.
Godiya ta musamman ga
abokai, dalibai da dangi, waɗanda
a lokuta daban-daban suka ba ni shawara, goyon baya da addu’a. Hakan ya taimaka
matuƙa
wajen sauƙaƙa wannan rubutu, da bincike
da kuma tsara littafin yadda ya kamata.
Ina kuma godewa masu
karatu, waɗanda su ne ginshikin
dalilin rubuta wannan littafi. Idan aka sami kura-kurai a ciki, ina roƙon a sanar da ni domin
gyara. Idan kuwa aka samu daidai, ina roƙon Allah Ya sanya wannan
aiki cikin abin da ake rubutawa a mizani na ranar sakamako.
Allah Ya sanya wannan
littafi ya amfanar da kowa, ya kuma zamo hanya ta ƙarin ilimi da tsaftace
Imani.
Auwal Zakari Muhammad Ayagi
(Barden Ayagi)
22 ga Jumada Akhir 1447= 14/12/2025
–
Sadaukarwa………………………………………..
– Godiya……………………………………………..
– Ta’aliqi…………………………………………….
– Abubuwan da ke ciki………………………………
– Dalilin rubuta littafin………………………………
–
Gabatarwa………………………………………….
BABI NA 1: Nasabar Manzon Allah (SAW)
Nasabar
Manzon Allah Ta vangaren Mahaifinsa……...
Nasabar Manzon Allah Ta vangaren Mahaifiyarsa……...
BABI NA 2: Alkunyar Manzon Allah Da
Sunayensa
Alkunyar
Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam……...
Sunayen Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam……...
BABI NA 3: Haihuwar Manzon Allah
(SAW)
Tarihin
Haihuwarsa Salallahu Alaihi Wasallam……...
Abubuwan da suka faru yayin Haihuwarsa ……...
Haihuwarsa
da Alamomin da suka Bayyana…...
Alamomin Haihuwar Manzon Allah ……...
BABI NA 4: Rayuwar Annabi (SAW)
Daga lokacin Shayarwa Zuwa Aikoshi
Shayar
da Annabi a Gidan Mahaifiyarsa……...
Zuwansa Gidan Halimatus-Sa’adiyya……...
Tsaga
Qirjinsa Salallahu Alaihi Wasallam………………
Rasuwar
Mahaifiyarsa……...
Tarbiyya a Hannub Kakansa Abdulmutallib……..
Rayuwarsa
a Gidan Abi Talib……………
Aurensa
Dan Nana Khadija……...
Aikoshi da Saqo Salallahu Alaihi Wasallam……………
BABI NA 5: Koyarwar Annabi
Salallahu Alaihi Wssallam
Koyarwa
akan Ilimi da Tauhidi……...
Bin Koyarwar Annabi (SAW)……...
Koyarwar
Annabi a kan Sallah………………
Koyarwar
Annabi a kan Azumi……...
Koyarwar Annabi a kan Zakka da kyautatawa……..
Halayen
Annabi (Ahlaq)……………
Shugabanci
da Tsarin Siyasar Annabi (SAW)………..
BABI NA 6: Mu’ujuzojin Manzon Allah
(SAW)
Ma’amnar
Mu’ujiza……...
Babbar Mu’ujiza Alqur;ani Mai Girma……...
Mu’ujizojin
da Suka Faru tin Yana Qarami………………
Mu’ujizojin
Annabi a lokacin Annabta……...
Mu’ujizojin Taimakon Allah……..
Isra’I
da Mi’iraji……………
Mu’ujizojin
Waraka………..
BABI NA 7: Kiran Annabi Zuwa
Tauhudi a Makka
Shekaru
Uku a voye, Goma a Bayyane……...
Farkon wadanda suka amsa kira……...
Ayyukan
Annabi (SAW) a shekaru Goma………………
BABI NA 8: Hijirar Manzon Allah
(SAW)
Ma’amnar
Hijira……...
Dalilan yin Hijira……...
Zamansa
a kogon Thawr………………
Tafiyarsa
Daga Makka zuwa Madina……...
Shigar Manzon Allah Madina…….
Mahimman
Abubawan da suka faru Bayan Hijira…..
Mahummancin
Hijira a Musulunci………………….
BABI NA 9: Yaqoqin Manzon Allah
(SAW)
Adadin
Yaqe-yaqen Manzon Allah……...
Jerin Yaqe-Yaqen Manzon Allah……...
Hikimar
Yaqe-Yaqen Manzon Allah………………
BABI NA 10: Matayen Manzon Allah
(SAW)
Matayen
Annabi da Matsayin su…………………….
Jerin Matayensa da Falalarsu……...
BABI NA 11: ‘Ya’yayen Manzon Allah
(SAW)
‘Ya’yayen
Manzon Allah Maza……...
‘Ya’yayen Manzon Allah Mata……...
Fadimatuz-Zahara
da Aurenta da Sayyadi Aliyu………
BABI NA 12: Ammomin Manzon Allah
(SAW)
Ammomin
Manzon Allah Maza……...
Ammomin Manzon Allah Mata……...
BABI NA 13: Masu Hidima Manzon Allah
(SAW)
Hadiman
Manzon Allah Maza……...
Mawaqan Manzon Allah Mata……...
Masu
Kiran Sallar Manzon Allah………
BABI NA 14: Siffofi da halayen
Manzon Allah (SAW)
‘Ya’yayen
Manzon Allah Maza……...
BABI NA 15: Wafatin Manzon Allah (SAW)
Farkon
Rashin Lafiyar Manzon Allah Maza……...
Wafatin Manzon Allah Mata……...
Darussa
daga Wafatinsa (SAW)………
Kammalawa……………………………………………
Rubuta wannan littafi na tarihin Manzon Allah Annabi Muhammadu ﷺ ya samo asali ne daga tsantsar
so da ƙauna ga shugaba, jagora, da abin
koyi a rayuwata.
Tsananin soyayyar da biyayyar da nake yi ga Manzon Allah ﷺ ya sanya ni ƙudur ci niyar da na rubuta
wani abu akan rayuwarsa, da kyawawan dabi’unsa, da darussan da al’umma zasu koya
a tarihin sa shugaba Alaihissalam.
Wannan littafi ba kawai tarihi bane, a’a akwai darussan da za’a koya cikin
tarihin shugaban mu Annabi ﷺ. Haka zalika wannan rubutu babban abin alfahari ne a gare ni da cewa na
rubuta wani abu kan masoyina Manzon Allah ﷺ, wanda soyayyar sa da koyarwarsa ta mamaye zuciyata.
Dalilin rubuta littafin ya haɗa da:
Yaxa sunan Manzon Allah ﷺ da koyarwarsa ga matasa da dukkan al’umma.
Koyar da darussa da kyawawan halayensa domin koyi da shi a rayuwar yau da kullum.
Gina
soyayya da biyayya ga Annabi ﷺ ta hanyar kalmomi da labarin
rayuwarsa ga Matasanmu dama dukkan Al’umma..
Rubutun wannan littafi ƙoƙari ne na musamman don nuna soyayya, girmamawa,
da alfahari da kasancewa cikin masu bada gudummawa wajen isar da rayuwar Annabi
ﷺ ga masu karatu.
Wassalamu Alaikum.
GABATARWA
Alhamdulillah, wannan littafi na rubuta shi ne domin bayyana rayuwa,
siffofi, kyawawan dabi’u, da koyarwar Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam
shugaba, jagora, masoyin zukatanmu. Tsananin soyayya da girmamawa da nake yi ga
shugaba Alaihissalam shi ya sanya ni ƙuduri na rubuta wannan
littafi, domin na yaxa rayuwarsa da darussan dake ciki, na shiriya, domin
ilmantar da al’umma musamman matasa da Mata.
Rubutun wannan littafi na tarihin rayuwar Ma’aiki Alaihissalam, baban
abin alfahari ne kasancewa ta marubucin da ya rubuta wani abu akan masoyi kuma
xan gatan Allah. Wannan littafi yana ɗauke da tarihi daga haihuwarsa, rayuwar Annabta, hijira, zaman
Madina, yaƙe-yaƙe, zuwa wafatinsa, har ma da kyawawan dabi’u
da siffofin da suka zama abin koyi ga dukkan Musulmi.
Ina fatan duk mai karatu zai sami shiriya da farin ciki, da karfafa
imani daga wannan littafi, kuma ya koyi yadda zai bi koyarwar Annabi ﷺ a rayuwar yau da kullum.
“Lallai haƙiƙa Manzon Allah ﷺ abin koyi ne
mafi kyau ga ku.” (Suratul Ahzab: 21)
Wassalamu
Alaikum.
Auwal
Zakari Ayagi
(Barden
Ayagi)
BABI NA XAYA
NASABAR MANZON ALLAH SALLAHU ALAIHI WASALLAM
Nasabarsa Ta Vangaren Mahaifinsa
Shine:
Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul-Muṭṭalib (ana kiransa da Shaybatul Hamd) ɗan
Hāshim (ʿAmr)
ɗan Abdu Manāf
(Al-Mughīra) ɗan
Qusayy (Zayd) ɗan
Kilāb ɗan
Murrah ɗan Kaʿb ɗan
Lu’ayy ɗan Ghālib
ɗan Fihr (wanda ya zamo shugaban Quraysh, shi ake kira
Quraysh) ɗan Mālik ɗan An-Nadr ɗan
Kinānah ɗan
Khuzaymah ɗan Mudrikah (ʿĀmir)
ɗan Ilyās
ɗan Muḍar
ɗan Nizār
ɗan Maʿadd ɗan
ʿAdnān.
Nasabarsa Alaihissalam da ta haɗa
har zuwa ga Annabi Ibrahim (AS)):
Adnān ɗan
Udd ɗan Muqawwam ɗan Nāḥūr ɗan Tayraḥ ɗan Yaʿrub
ɗan Yashjub ɗan Nābit ɗan Is’hāq ɗan Ibrāhīm
(Khalīlullāh) ɗan Āzar (Tāriḥ) ɗan
Nāḥūr ɗan
Sārūgh
ɗan Arghū
ɗan Fāliq
ɗan ʿĀbir (Hud AS ko Eber) ɗan
Sālih ɗan
Arfakhshad ɗan Sam ɗan
Nūḥ ɗan Lamk ɗan
Matushailah ɗan Idrees (Hannūkh – AS) ɗan Yard ɗan
Mahlā’īl ɗan
Qainan ɗan Anūsh
ɗan Shīth
ɗan Ādam
(AS).
1. Maxauka
a zuriyar Banu Hāshim
• Muhammad (SAW)
• Abdullāh
• Abdul-Muṭṭalib
• Hāshim
• Abdu Manāf
• Quṣayy
2. Asalin Quraysh: Fihr shi
ne Shugaban Quraysh gaba ɗaya.
3. Asalin Larabawa Adnāniyya: Daga Maʿadd
zuwa ʿAdnān
– shi ne uban Larabawan Arewa.
4. Nasaba zuwa Annabi Isma’il (AS): Adnān daga zuriyar Ismā’īl ɗan
Ibrāhīm
(AS).
Malamai sun ce: “Abin da ya tabbatar sahihi daga Manzon Allah shi ne
nasabarshi ta kai daga Muhammad zuwa Adnān. Bayan Adnān
ana dogaro ne da ruwayoyi na tarihi, ba duka suka kai matsayin sahihanci ba.”
NASABAR MANZON ALLAH (SAW) TA BANGAREN MAHAIFIYARSA – ĀMINAH
Muhammad
(SAW) ɗan Āminah
bint Wahb, ‘ya ga Wahb bn ʿAbd
Manāf, ɗan
Zuhrah bn Kilāb, ɗan
Murrah bn Kaʿb, ɗan
Lu’ayy bn Ghālib, ɗan
Fihr bn Mālik, ɗan
An-Nadr bn Kinānah, ɗan
Khuzaymah bn Mudrikah, ɗan Ilyās bn Muḍar,
ɗan Nizār
bn Maʿadd, ɗan Adnān
Daga
nan zuwa sama:
Adnān ɗan
Udd ɗan Muqawwam ɗan Nāḥūr ɗan Tayraḥ ɗan Yaʿrub
ɗan Yashjub ɗan Nābit ɗan Ismā’īl (AS) ɗan
Ibrāhīm
(AS) ɗan Āzar
(Tāriḥ) ɗan Nāḥūr ɗan Sārūgh
ɗan Arghū ɗan Fāliq ɗan ʿĀbir
ɗan Sālih
ɗan Arfakhshad ɗan
Sam ɗan Nūḥ
(AS) ɗan Lamak ɗan Matushailah ɗan
Idrees (Hannūkh) ɗan
Yard ɗan Mahlā’īl ɗan Qainan ɗan
Anūsh ɗan
Shīth ɗan
Ādam (AS).
MUHIMMAN BAYANAI GAME DA DANGIN MAHAIFIYARSA ĀMINAH (RA):
1. Ƙabilarsu
ta Zuhrah
• Āminah
tana daga ƙabilar Banū Zuhrah, ɗaya daga cikin manyan rassan Quraysh.
• Shi ma Kilāb bn Murrah uban su ne, wanda ya haɗa
nasaba da na Manzon Allah ta wajen mahaifinsa.
2. Kyakkyawan asalinta
Malamai
sun yi ittifaqi cewa dangin Banū
Zuhrah suna cikin mafiya daraja da ƙima
a Quraysh tun kafin Musulunci.
3. Dangantakar ta da Manzon Allah (SAW)
• Nasabar mahaifiyar sa da ta mahaifin sa sun haɗu
ne da:
Kilāb bn Murrah
Wannan yana nufin Annabi
Muhammad (SAW) da mahaifiyarsa suna da nasaba mai kusanci a cikin Quraysh.
BABI NA BIYU
ALKUNYAR MANZON ALLAH SALALLAHU
ALAIHI WASALLAM DA SUNAYEN SA TSARKAKA
ALKUNYAR MANZON ALLAH (SAW)
Manzon
Allah (SAW) yana da alkuniya guda biyu mafiya shahara:
1.
Abul-Qāsim (أبو القاسم)
Uban
Qāsim — saboda ɗansa
Qāsim wanda ya rasu tun yana ƙarami.
2.
Abū Ibrāhīm
(أبو
إبراهيم)
Saboda
yana da ɗa mai suna Ibrāhīm
daga ƙwarqwararsa Mariya tul-Qibṭiyya.
Sauran
alkunyoyi da malamai suka ambata:
Abū ʿAbdillāh – saboda sunansa Muhammad ɗan
Abdullāh
Abū Ṭāhir
– daga ɗa
mai suna Ṭāhir/Ṭayyib
Abū Ṭayyib
– wannan ma daga laƙaban ɗansa
Amma
mafi inganci kuma mafi shahara a hadisi shi ne: Abul-Qāsim.
Akwai
hadisi da Annabi (SAW) ya ce:
“Ku
sanya sunana amma kada ku sanya alkunyata.”
Domin
Abul-Qāsim na musamman ne a gare shi.
SUNAYEN MANZON ALLAH (SAW)
An
ambaci sunayensa da dama a Qur’ani da Sunnah. Mafi shahara su ne:
1. Muhammad محمد)
– Wanda
ake yawaita yabonsa.
An ambace shi a Qur'ani: “Muhammadun rasūlullāh.”
2. Ahmad (أحمد
– Wanda ya fi kowa godiya ga
Allah.
Annabi Isa (AS) ya yi busharar zuwansa da sunan Ahmad.
3. Al-Māhi (الماحي)
– Mai
gogewa — wanda Allah ya share kafirci da shi.
4. Al-Hāshir (الحاشر)
– Mai
tara mutane — domin mutane za a tattaro a kan tafkonsa a ranar kiyama.
5. Al-ʿĀqib (العاقب)
– Wanda
ya zo a ƙarshe, babu wani annabi bayansa.
6. Al-Muqaffā (المقفى)
– Mai
biyo bayan annabawa.
7. Nabiyyur-Rahmah (نبي الرحمة)
– Annabin
rahama.
8. Nabiyyut-Tawbah (نبي التوبة)
– Annabin
tuba da gafara.
9. Nabiyyu al-Malhamah (نبي الملحمة)
– Annabin
yakin kare adalci (ba zalunci ba).
10. Rasūlullāh, Nabiyyullāh
– Manzon Allah, Annabin Allah.
11. Al-Mustafa (المصطفى)
– Wanda
aka zaɓa.
12. As-Sādiq Al-Amīn (الصادق الأمين)
– Mai
gaskiya, amintacce.
(Wannan ya kasance lakabinsa tun kafin aiko shi da Manzanci).
BABI NA UKU
TARIHIN HAIHUWAR MANZON ALLAH (SAW)
Lokacin da aka haife shi: An haifi Manzon Allah
Muhammad (SAW) a Ranar Litinin, cikin Watan Rabi’ul Awwal, Shekarar da ake kira
“Shekarar Giwaye” (‘Āmul-Fīl), a cikin birnin Makka.
Shekarar Giwaye: Ita ce shekarar da Abrahah ya kawo giwaye
domin ya rusa Ka’abah, amma Allah ya halaka su da tsuntsaye kamar yadda Allah
ya ambata cikin Suratul Fīl.
Shekarar Haihuwar sa ta Miladiyya: Mafi yawan malamai sun ce:
a shekara ta 570 Miladiyya, wasu kuma suna cewa 571 CE.
Malamai sun yi sabani, An kawo ra’ayoyi da
dama, amma babu wani hadisi sahihi da ya tabbatar da takamaiman kwanan watan
haihuwarsa. Amma akwai shahararrun ruwayoyi guda huɗu:
(1) Ruwayar da ta fi shahara: 12 ga Rabi’ul Awwal
Wannan shi ne abin da yawancin malamai na fiƙhu da tarihin Musulunci suka ɗauka,
musamman a al’ummomin musulmi.
Amma ya samo asali ne daga ruwayar Ibn Ishaq
wadda ba ta kai matsayin sahihi ba.
Saboda haka 12 ga Rabi’ul Awwal ruwaya ce ta
tarihi, ba tabbataccen dalili na hadisi ba ne.
(2) Ra'ayin da ya fi ƙarfi a wurin masana: 8 ga Rabi’ul Awwal
Wannan ya fi kusanci da inganci, daga Ibn
Kathir da Ibn Hajar da Ibn Abdil Barr, wadanda su na daga cikin malaman da suka
ƙarfafa wannan kwanan.
(3)
Wasu malamai sun ce: 10 ga Rabi’ul Awwal
(4)
Ra'ayi mafi rauni: 2 ga Rabi’ul Awwal
Me yasa aka samu sabani?
Dalilai uku:
1. A
lokacin Jahiliyya ba a daidaita tsarin kalandar wata ba.
2. Babu
sahihin hadisi da ya ce ranar kaza aka haife shi.
3. Ibn
Ishaq (marubucin Seerah) bai tabbatar da kwanan rana da isnad mai ƙarfi ba.
Lokacin da aka haife shi cikin yini
Ruwayoyi sun nuna: An haifeshi Alaihissalam da
sassafe wato da (asubah). Ko kuma attsakar dare zuwa asuba.
KARIN BAYANI:
Hadisin da ya fi ƙarfi:
Abu Qatada ya ruwaito cewa Manzon Allah (SAW)
ya ce:
"Ana tambayarshi game da azumin Litinin,
sai ya ce:
'Wannan rana ce da aka haife ni, kuma rana ce
da aka sauke mani wahayi.'"
(Sahih Muslim)
Wannan shi ne hujjar gaskiyar ranar Litinin,
amma kwanan wata ba a fayyace ba.
Haihuwarsa Alaihissalam
Mahaifiyarsa Aminah bint Wahb ta haife shi a
gidanta na Banū Hāshim a Makka.
ABUBUWAN DA SUKA FARU YAYIN HAIHUWAR MANZON ALLAH (SAW)
1. An haife shi a ranar Litinin: Wannan shi ne
ingantacce sahihi, kamar yadda ya fada:
“An
haife ni a ranar Litinin.”
(Sahih Muslim)
2. Haske ya futo daga mahaifiyarsa (Aminah): Aminah
(RA) ta ruwaito cewa: “Na ga wani haske ya fito daga gare ni, ya haskaka mini
gidajen Shaam.”
(Ibn Sa’d, Ibn Ishaq – ruwaya mai karfi a
tarihi)
Ma’ana: Wannan alama ce ta cewa zai zama Annabi
ga duniya, hasken da zai watsu ya zarce Arabia har Sham.
3. Wutar masarautar Fāris ta mutu bayan shekaru 1,000 tana ci: A
masarautar Persia, akwai wuta mai suna Ātash
Bahram da take ci ba tare da ta an kasha ta ba na tsawon shekaru, amma A daren
haihuwar sa ta mutu gaba ɗaya.
Wannan ruwaya ce ta tarihi, malamai suka karɓa
domin ba ta yi karo da hankali ba.
4. Karyewar manyan tagogi 14 na fadar Kisra
(Sarkin Persia): Wani babban gini mai tagogi 14 ya kakkarye ba tare da wani abu
ya buge shi ba.
Malamai sun ce waɗannan
tagogi 14 suna nuni da sarakunan Persia 14, waɗanda
mulkinsu zai shuɗe kafin Musulunci ya rinjaye.
5. Kogin Samawah da ya bushe, sai ga ruwa ya
cika shi: Wani kogi ne a ƙasar
Persia wanda ya shekara yana bushe, sai gashi ya cika da ruwa a daren haihuwar
sa.
Wannan Ruwaya ce ta tarihi mai karɓuwa.
6. Gumakan Quraysh sun fadi ko sun rushe: A
cewar ɗan Abbas da wasu daga cikin Tabi’ai, gumakan
da Quraysh suke bautawa sun faɗi kasa a fadar sa. Wannan
alamar bacewar bautar gumaka ne , da bayyanar tauhidi.
7. An
haife shi yana wankakke kuma cikin tsabta
An ruwaito cewa: An haife shi cikin tsarki,
babu datti a jikinsa, kuma yana da alamar hatimin annabci a bayansa.
Ruwaya mai kyau (Ibn Hajar ya karɓa).
8. An haife shi ba tare da jini da kazanta ba
Malamai sun ce: “An haife shi ba tare da al’adar
haihuwa da jini ko kazanta ba.”
Wannan alama ce ta tsarkin Annabci.
9. An hanguo haske zuwa sama yayin hauhawar sa
Wasu suka ce: Haske ya yi sama zuwa sararin
samaniya a daren haihuwarsa.
Ruwayar tarihi ce.
10. Sheɗan
ya yi ƙara,
kuma an katse satar ji a sama da ƙasa,
A lokacin haihuwarsa: Aljannu ba su sake satar ji daga sama ba. Haske ya rufe
sama, kuma ƙasashen
gabas suka ga wani haske mai ban mamaki.
11. An kira shi da sunan “Muhammad” tun kafin
a zuwan shi. Kakan sa Abdu-lMuttalib ya yi mafarki yana ganin cewa: Za a haifi
yaro wanda zai shahara a duniya da sama.
Don haka ya sa masa suna Muhammad – “Abin
yabawa.”
HAIHUWAR MANZON ALLAH ﷺ DA ALAMOMIN DA SUKA BAYYANA A CIKINSA
A ranar da Allah Madaukakin Sarki ya kawo
fitilar halitta, Sayyidina Muhammad ɗan
Abdullah ɗan Abdul-Muṭṭalib,
duniya ta karɓi jariri wanda babu kamarsa cikin halitta da
kamala. Tun kafin a haife shi, alamomin Nnubuwa da tsarkinsa sun bayyana a
cikin Mahaifiyarsa, Sayyida Āmina
bint Wahb.
An Haife Shi a Tsarki da Kyau Mai Wuce Misali
Malamai da dama sun kawo riwayoyi game da
yanayin haihuwarsa, wasu sahihai ne, wasu raunana, amma duk suna nuni da cewa
haihuwar Annabi ﷺ ba ta yi kama da ta kowa ba.
1. Game da an haife shi da Kaciya (Shayi)
Wasu malamai sun rawaito cewa:
“An
haifi Manzon Allah ﷺ yana makutu — wato cikin
yanayin da al'aurarsa ta riga ta yanke kamar wanda aka yi masa kaciya.”
Wannan ra’ayi an kawo shi a cikin wasu
littattafan tarihin Annabi kamar:
• Dalā’il al-Nubuwwa na al-Bayhaqī
• Khaṣā’is al-Kubrā na Suyūṭī
Amma masana sun bambanta:
• Wasu sun ce wannan ba hujja sahihiya ba ce,
saboda a sahihan hadisai babu wannan tabbatacciyar magana.
• Wasu kuma sun ce koda kuwa bai kasance an haife
shi ne da kaciya ba, an yi masa kaciya ne a ranar bakwai kamar sauran ’ya’yan
Larabawa.
Saboda haka, a salon littafi, ana bayyana
haka:
“Daga
cikin alamu masu girma da aka nakalto a littattafan tarihin Annabi, akwai cewa
an haife shi a tsarkake, babu datti, babu ƙazanta,
har ma wasu sun rawaito an haife shi da kaciya, kamar wanda mala’iku suka yi masa tun daga
sama.”
2. Ya zo Da Kwalli a Idanunsa
Da yawa daga wasu malamai sun nuna cewa idanun
Annabi ﷺ tun
haihuwarsa suna da kyalli na musamman, kamar wanda aka shafa masa kwalli,
saboda tsarkin halittarsa da annuri da ke fizgarwa daga idanunsa.”
A hakikanin ilimi, abin da ya tabbata shi ne:
Idanun Annabi sun kasance masu sheƙi, baki masu kyau, suna burgewa ga mai kallo — kamar yadda sahihi ya zo a
Shamā’il Muhammadiyya.
3. Yazo Shafe Da Mai Da Kyalli a Jikinsa
Wannan kuwa tabbatacce ne cikin sifofinsa
(Shamā’il). An ce: Jikinsa yana fitar da ƙamshi mai dadi. Gashin kansa yana kyalli. Fuskar
sa tana walwali kamar wata xan daren sha huxu. Bakin sa da jikinsa suna fitar
da qamshi mai daxi fiye da turaren miski.
“Jikinsa ya kasance tamkar an shafe shi da mai
mai tsarki; yana sheƙi,
yana ƙamshi, yana kyalli. Duk
wanda ya zauna kusa da shi, sai kamshin Annabi ﷺ ya
lullube shi.”
ALAMOMIN HAIHUWAR MANZON ALLAH ﷺ
A lokacin da Aminah ta ji haihuwa ta gabato,
ba ta wahalta ba kamar yadda mata ke yi.
A ruwayar Aminah:
“Da
na haife shi, ﷺ
haske ya fito daga cikina ya haskaka min gidajen Busra a Sham.”
Nan take jaririn ya fito, tsaf, tsare, cike da
annuri. Babu ƙazanta
a jikinsa, babu jinin da ake gani a sauran jarirai. An karɓe
shi cikin tsarki da natsuwa.
Wasu riwayoyi sun ce:
An haife shi yana kwance da ƙafafunsa suna katse, kamar wanda aka yi masa
kaciya. Idanunsa suna kyalli kamar an shafa masu kwalli. Jikinsa yana sheƙi kuma yana fitar da ƙamshi. Mala’iku suka sauko suna murna da
haihuwarsa.
Fāṭimah
bint Asad (uwargidan Abu Ṭālib)
ta kasance daga cikin matan da suka taimaka Aminatau a lokacin haihuwar Shugaba
Alaihissalam.
An haife shi a cikin riga (wato al'amarin da
ba a saba gani ba), alamar kariya daga Allah.
Kakan sa Abdul-Muṭṭalib ya sa masa suna Muhammad, wanda bai saba
da shi a cikin Quraysh ba a wancan lokaci.
Bayan kwanaki bakwai, Abdul-Muttalib ya yanka abin
yanka har guda bakwai, ya kira mutane suka yi murna da haihuwarsa.
BABI NA HUXU
RAYUWAR MANZON ALLAH ﷺ A LOKACIN SHAYARWA ZUWA AIKO
SHI
Shayar da Annabi ﷺ
a Gidan Mahaifiyarsa
Bayan haihuwar Manzon Allah ﷺ a
Ranar Litinin, an bada shi ga matar da ta fara shayar da shi, wato Swaybah,
baiwar Abu Lahab kamar yadda yake a al’adar Larabawa.
Ita ce ta fara ba shi nono kafin a kai shi ga shahararriyar
mai shayarwa wacce duniyar Larabawa ta sani, wato Halimah bint Abu Zuwaib
as-Sa’diyyah daga ƙabilar Banū Sa’d.
Tsarinta mai hankali da nutsuwa ya bayyana tun
a lokacin da ta rungume shi, inda ta ce:
“Da
na ɗauke shi, na ji jikinsa kamar wani haske ne mai
sanyaya zuciya, kuma jinin nonona ya fara yawowa.”
Zuwansa Gidan Halimah Sa’diyya – Albarka Ta Farko
Kabilar Banū Sa’d ta yi suna a wajen
shayarwa da tarbiyya, kuma Halimah ce ta yi wa Annabi ﷺ
shayarwa na tsawon shekaru biyu.
Tun daga cikin kwanaki na farko, Halimah da
mijinta Harith suka lura cewa:
Rakumarsu ta fara zubar da madara fiye da da. Awakinsu sun komo daga kiwo sun cika
da kiba. Gidansu ya cika da albarka fiye da sauran gidajen makwabta.
Kamar yadda marubucin wannan littafi ta waqe wacce
ta Shayar Da Manzon Allah (SAW) wato Halimatussa'adiyya, a wata qasida mai
taken:
Halimatus-Sa'adiyya Ta Shayar Da Nura
Haltmatus-Sa Adiyya Ta
Rabauta A Duniya.
1. Farko Nasa Gwani Rabbana Mai Duniya
Wanda Yai
Malaika Can Cikin Samaniya
Yayi Ruwan
Korama Yai Babbarsu Maliya.
2. Bayan Nai Basmala Ga Khailikin Auliya,
Na Daxa
Yin Hamdala Ga Rabbana Shi Xaya,
Wanda Ya
Turo Mursalai Don Ceton Duniya.
3. Ya Rabbi qara Tsira Ga Khatimul Anbiya,
Wanda Yake
Shugaba ne Ga Dukkann Duniya,
Don Ya
Zamo Zuwansa Duniya Ta Shiriya.
4. A Yayin Haihuwarsa Shugaban Duka Anbiya,
Haske Sai
Ya Fece Ya Haske Duk Duniya
Ya Haska
Mana Nan Qasa Ya Haska Samaniya.
5. Bayan ‘Yan Kwanaki Da Haihuwar Nabiya,
Kamar
Yadda Can Ga Jamaár Makiyya,
In An
Haifa Musu Xa Sai Su baiwa Balarabiya.
6. Taje Da Shi Ta Shayar Tai Tayi Masa Tarbiya,
To Haka Ma
Ya Faru Ga Shugaban Anbiya,
Sai Aka
Nemo Xaya Taje Da Shi Ta Goya.
7. Ai Matan Bani Sa’ad Su Suka Zo Makiyya,
Don Neman
Shayarwa Su Samu Kuma Dukiya,
Sun Hawo
Kan Jakuna Sun Taho Gaba Xaya.
8. Sunzo Gun Amina Xayarsu Bayan Xaya,
Suna Yi
Mata Tambaya Xa Ne Ko Ko Xiya,
Mijinki
Yana Da Rai Ko Mun Samu Dukiya.
9. Sai Ta Furta Da Bakin Ta Tace Da Su Ku Tsaya,
Shi Wannan
Xa Na Wa Ya Zamo fa Maraya,
Kar Kusa
Ran Za Ku Samu Kuxi Da Yawan Tsiya.
10. Sai Nan Take Matannan Dukkanninsu Gaba Xaya,
Sai Suka
Sa Takalma Sunka Juya Da Baya,
Don Sun
San Ga Maraya Ba A Samun Dukiya.
11. Sai Wata Mata Tazo Kan Jaka Ramammiya,
Sam
Jakar Bata Gudu Duk Itace A Baya,
Matar
Ramammiya Jakar Ramammiya.
12. Kai Tafiyar Matannan Sai Kace Hawainiya,
Don
Tsananin Kasala Kana Ga Gajjiya,
Taje
Gurin Aminaa Ta na yi mata Tambaya.
13. Ko Kunsan Wacece Jakarta Ramammiya?
Ta Je Wajen Amina Tana Tayin Tambaya?
To
Wannan Ai Itace Halimas-Sa’adiyya.
14. Gata Fara Kyakyyawa A Tsawo Tsakatsakiya,
Me Fuska
Doguwa Kana Shiryayyiya,
Ga
Hakorin Fari Tas Yana Haske Walkiya.
15. In Har Tai Muku Murmushi Sai Kuga ‘Yar Walkiya,
Me Idanu
Fari Tas Halimatus-Sa’adiya,
Baqin
Idon Wulik Ne Na Halimatus-Sadiya.
16. Amina Tace Mata Da Gani Kin Sha Wuya,
Kina
Bidar Shyarwa Anan Garin Makiya,
Wallahi
Ni A Guna Sai Wannan Maraya.
17. Ga Shi Kuma Kin Sani In an xau Maraya,
In Har
Kun Gama Shayarwa Kun Dawo Makiyya,
Babu Kuxi
Masu Yawa Balle Kuma Dukiya.
18. Sai Nan Take Tace Mata Halimatus-Sa'adiya,
Zan Xaukeshi
Don Kauna Bawai Don Dukiya,
Ke Dai
Fadan Sunansa In Xauka In Goya.
19. Lokacin datan Nufo Shugaban Duka Anbiya,
Domin
Nufin Ta Dauka Ta’azashi Ga Baya,
Tana
Miqo Hannunta Sai Taga Yai Dariya.
20. Me Sauraro Saurara Don Yanzu Zaka Jiya,
Abubuwan
Mamaki Nan A Gunta Sa'adiya,
A Lokacin
Da Ta Dau Shugaban Duka Duniya.
21. A Nan Take Tai Qiba Halimatus-Sadiya,
Kamanninta ya Canja Halimatus-Sadiya,
Sai
Kyawunta Ya Qaru Haltmatus-Sadiya
22. Suna Zuwa Ga Jakarta Domin Fara Taffiya,
Sai
Jakar Tai Qiba Tana Ta Haniniya,
Tana
Tsalle Da Qara Tana Tayin Dariya.
23. A Sannan Bani Sa'ad Sun Wuce Ta Sa'adiya,
Tintini
Sunyi Nisa Sun Wuce Ta Sa’adiya,
Tana
Hawa Jakarta Sai Ta Fara Gudun Tsiya.
24. A Nan Take Tai ta Gudu Sai Kace Wata Walkiya,
Tana
tayin Sassarfa Tana Harbi Ta Baya,
Tana Ta
Qarin Sauri Kamar Tana Ninkaya.
25. Bani Sa’ad Sun Kace Ga Wata Nan Daga Baya,
Tazo Ta
Wucemu Sai Kace Wata Walkiya,
Sai
Sukace Wallahi Ba Wata Sai Sa’adiya.
26. Dabbobinta Sun Yi Qiba Sunyi Nono Sa’adiya,
Arzikinta Ya Karu Ya Zarce Duk Na Baya,
A Duniya
Da Lahira Ta Rabauta Gaba Xaya.
27. Sai Gashi A Bani Sa’ad Ba Kamarta Sa’adiya,
Wai Don
Mene Ta Samu Xaukakar Nan Sadiya,
Ta Samu
Don Ta Shayar Da Shugaban Anbiya.
28. Kana Ta Kaunace Kauna ta Gaba Xaya,
Ta
Kaunace shi Don Allah Ba Wai Don Dukiya,
Ya Zama
Lallai Mu Koyi HalimatuSa’adiyya.
29. Duk Mai Son Mustafa Da Zuciyarsa Daya,
Na
Rantse Rabbana Zai yaye masa Duk Tsiya,
Ya Sa
Shi A Aljanna Bashi Ba Shan Wuya.
30. Na Yi Roko Ya Allah Don Darajar Sa’adiya,
Ka
Arztrta Dukkanin Yan Kungiyar Azmiyya,
Da
Hakikanin Soyayya Ga Shugaban Anbiya.
31. Ya Allah Don Darajar Shugaban Duka Anbiya,
Ka
Arzurta Dukkanin Yan Kungiyar Azmiyya,
Da
Arziki Mai Yawa Wanda Babu Hisabiya.
32. A Nanne Zan Dakatar Da Begen Kuma In Tsaya,
Ni Auwal
Na Shirya Shugaban Al-Azmiyya
Wannan
Bege Gurinta Halimatus-Sadiya.
33. Allah Ka Karbi Wannan Bege Da Na Shirya,
Ka
Mikashi Gareta a Lahira Sa’adiya,
Har Ta
Kaimu A Ranar Ga Shugaban Anbiya.
Zaman Annabi ﷺ
a Tsakanin Banū Sa’d
Ma’aiki Alaihissalam ya shahara da hankali tun
yana ƙarami, ba ya yawan kuka,
gashi mai yawan shiru ga nutsuwa da hankali.
Tsaga Kirjinsa ﷺ (Shaqqu Ṣadr)
A lokacin da ﷺ yake ƙauyen Banū Sa‘d, inda ake shayar da shi
cikin albarka, wata rana yana wasa tare da ’yan uwansa a wajen kiwon dabbobi, sai wani al’amari
ya faru wanda ya girgiza zukatan qauyen, ya kuma ƙara
tabbatar da tsarkin Manzon Allah ﷺ tun kafin zuwan wahayi.
Yanda al’amin ya faru
Lokacin yana kusan shekaru huɗu,
Halimah Sa’diyya da mijinta sun barshi yana wasa a bayan gida tare da ɗan’uwansa
’Abdullāh. A
cikin kwanciyar hankali, sai wani abu ya bayyana cikin sauri kamar ɗigon
haske daga sararin sama.
Abdullāh ɗan
Halimah ya dawo da gudu yana kuka yana cewa:
"Wallahi wasu mutanen farare sun kama ɗan ƙanenmu Muhammad! Sun kwantar da shi, sun buɗe
kirjinsa!"
Halimah da mijinta suka firgita. Suka fita da
gudu kamar zuciyarsu za ta faso kirjin su, don zuwa suga wannan al’amari.
A ruwaya sahihiya, cikin Sahih Muslim, an
tabbatar da cewa: Mala’iku biyu ne suka zo, Suka kwantar da shi a ƙasa cikin tausayi, ba da azabtarwa ba. Suka buɗe
kirjinsa cikin tsabta. Suka fitar da wati ƙaramar
tsoka daga zuciyarsa.
Suka ce:“Wannan shi ne rabon shaidan da ke cikin zuciyarka.” Suka zubar da shi.
Suka ciro zuciyarsa suka wanke ta da ruwan
Zamzam a cikin kwano na zinariya.
Aka cika kirjinsa da: Haske da Hikima da Imani
da Tsarki da Albarka
Daga na sai suka mayar da qirjinsa nasa, suka
xinke shi, ba tare da wasu raunuka ko jini ba.
Halin da Annabi ﷺ Ya
Shiga
A lokacin da Halimah ta iso, sai ta tarar da
shi: Zuciyarsa tana bugawa
cikin natsuwa. Launin jikinsa ya ɗan
canza saboda girman al’amarin, Amma ba shi da wani ciwo ko rauni, fuskar sa
cike da annuri. Ya gaya mata abin da ya faru cikin kalma kaɗan
da nutsuwa.
Halimah sai ta fara kuka, saboda abin ya tsorata,
sai ta fara tunanin cewa ta mayar da shi ga mahaifiyarsa don tsoron kada wani
abu ya same shi.
Dalilin da yasa aka tsaga kirjin sa
Malamai sun yi bayani cewa: an tsaga kirjin sa
ﷺ ne
sabo da tsarkake zuciyarsa tun kafin zuwan wahayi, Allah ya
shirya zuciyar Annabi tun yana yaro, ya cire duk wani abu na rabon shaidan daga
zuciyar.
Jawabin Malaman Tarihi kan tsaga qirjinsa ﷺ
Ibn Hajar al-Asqalani ya ce:
“Wannan
al’amari gaskiya ne kuma ya tabbata a sahihan ruwayoyi, ba abin al’ajabi ba ne
ga darajar Manzon Allah ﷺ.”
Imam Nawawi ya ce:
“An
tsaga kirjinsa ne domin qara albarka a zuciyar, da karfafa Zuciyar, domin
nauyin risala da zuciyar zara xauka.”
Tasirin Al’amarin ga Halimah
Bayan wannan al’amari, Halimah ta tabbatar
cewa wannan yaro ba kamar sauran yara ba ne.
Ta ce a wata ruwaya:
“Daga
wannan rana, na san cewa Muhammad bawan
Allah ne, Allah ne yake kiyaye shi da kansa.”
Sai ta yanke shawarar mayar da shi ga
mahaifiyarsa Sayyada Aminah saboda tsoron kada wani abin almara ya sake faruwa
da shi a karkarar.
Wannan al’amari shi ne shaquṣ-ṣadri
na farko; akwai wasu da suka faru a lokacin aiko shi da kuma lokacin Isra’i da
Mi’raj
Rasuwar Mahaifiyarsa ﷺ
RASUWAR MAHAIFIYAR MANZON ALLAH ﷺ
Sayyida Aminah bint Wahb, mahaifiyar Manzon
Allah ﷺ, mace ce mai kamala, tsarki da natsuwa. Ta
haifi Annabi Muhammad ﷺ ne a Makkah, sannan ta yi
masa tarbiyya cikin ƙauna
da kulawa bayan rasuwar mijinta Abdullah, wanda ya rasu tun kafin haihuwar
Annabi.
Lokacin da Annabi ﷺ ya
kai kimanin shekaru 6, Aminah ta ɗauke
shi zuwa Madina don ziyarar dangin kakarsa ta ɓangaren
uba (Banū
Najjār), Kuma su ziyarta dangin
mahaifinsa. Sun zauna Madina kusan wata guda.
A hanyarsu ta dawowa, lokacin da suka iso Abwā’
(wani wuri ne tsakanin Makkah da Madina), Aminah sai rashin lafiya ya kamata, da
ciwon da ya yi tsanani sai ta gajiya ta kamata sosai, inda anan Allah yayi mata
rasuwa.
Manzon Allah ﷺ yana
da shekaru 6 kacal ya rasa mahaifiyarsa, ya zama maraya na hakika babu uwa ba
uba.
Wanda ya dawo da shi Makkah
Bayan rasuwarta Ummu Ayman (Barakah), baiwar Aminah,
ce ta dawo da shi Makkah, Sannan Kakansa Abdul-Muṭṭalib
ya rungume shi cikin tsananin ƙauna
yacigaba da rainon sa.
Tarbiyya a Hannun Kakansa Abdul-Muṭṭalib
Kakan sa ya rungume shi cikin ƙauna, ya riqa zaunar dashi a kan shimfixarsa
wadda ba a barin kowa ya zauna a kai.
Abdul-Muṭṭalib
ya ci gaba da rainon Annabi cikin girma da kulawa don ganin Annabi a matsayi na
mai albarka.
Ya ce: “Wannan ɗan
zai kai ga sabon matsayi mai girma.”
Sai dai bayan shekaru 2 shi ma Abdul-Muṭṭalib ya rasu.
Rayuwarsa a Gidan Abu Ṭālib
Daganan a sai ya koma rayuwa a gidan kawunsa
Abu Ṭālib, wanda shi ma ya ba shi
mahimmanci fiye da ’ya’yansa cikin kulawa da qauna.
Annabi ﷺ ya
tashi cikin halaye maisu kyau na Mutuntawa, yawan sadaka da girmama manya, ya
zamo mai gaskiya.
Duk wanda ya haxu da shi yana cewa:
“Muhammad
yaro ne mai kamala, nutsuwa, da gaskiya.”
A gidan Abu Ṭālib
ne ya fara aikin kiwon dabbobi, sannan ya tashi cikin halaye masu tsabta na
Larabawa.
Lokacin Samartakarsa da Sana’a
Aikin kiwo
Annabi Alaihissalam ya yi kiwon dabbobi a
Makka kamar yadda Annabawa da dama suka yi.
Kasuwanci
Annabi Alaihissalam ya bi Abu Ṭālib zuwa Sham, don ya koyi lasuwanci, ya zama
nagari, mai gaskiya da ruqon amana.
Duniya ta kira shi: “As-Ṣādiq al-Amīn” wato Mai Gaskiya Mai
Amanah.
Auren Manzon Allah ﷺ Da Sayyida Khadija
Sayyida Khadīja
bint Khuwaylid ta kasance mace mai daraja a garin Makkah, macece mai Girma, da tsarki,
da arziki, da mutunci. Duk wani dan kasuwa mai gaskiya yana tare da ita, kuma
duk wani mai neman amana yana girmamata.
Malamai suka kira ta:
“Sayyidat
Quraish” – Mace mafi daraja a cikin Quraysh.
A lokacin da Manzon Allah Muhammad ɗan
Abdullah yana shekaru 25, kafin ya zama Annabi ya shahara da:
• Gaskiya da Aminci da Kyawawan halaye ga Tausayi
ga Adalci ga Natsuwa, dukkan mutune suna kira shi da "As-Sādiq al-Amīn".
Farkon Kasuwancinsa Da Khadija
Khadija ta ji labarin mutuncinsa, da gaskiya
da Amanarsa sa ta gayyace shi ya yi mata tafiyar kasuwanci zuwa Sham, tare da
bawanta Maysarah.
A wannan tafiya, Maysarah ya lura da abubuwa
waɗanda suka bambanta shi da sauran mutane: domin ya
sameshi Alaihissalam bashi da yaudara, baya yawan Magana, bai san ha’inci ko
cuta ba.
Maisarah ya ga abubuwar mamaki tare da shi,
kamar rana da tana masa inuwa, da sauran abubuwan mamaki tare da shu.
Lokacin da suka dawo daga Sham, sun dawo da ribar
mai yawa, da ta wuce kowane lokaci da aka taɓa samu.
Maysarah ya faɗa
mata kywawan halayensa da suka saka ta ta nutsu da shi.
Khadija Ta Nuna Sha’awar Aurensa
Bayan ta tantance gaskiyar halayensa, ta ga
cewa wannan matshi ba kamar kowa ba ne.
Ta ambata wa aminiyarta Nafisa bint Munabbih
cewa tana sha’awar auren shi, amma cikin kunya da ladabi.
Nafisa ta je ta ambatawa Annabi Muhammad (SAW)
ta ce:
“Idan
aka kawo maka mace mai daraja, mai arziki, mai tsafta fa zaka aureta?”
Ya tambaya: “Wacece?”
Ta ce: “Khadija bint Khuwaylid.”
Sai ya ce da mamaki:
“Ita
take so na?”
Nafisa ta tabbatar masa — zuciyar sa ta
amince.
Abu Talib ne ya jagoranci nemna auren, kuma
aka yi auren bisa ka’idar Larabawa, manyan Quraysh ne suka halarta. An yi taro
mai annashuwa da mutunci. A ranar da aka yi auren, Abu Talib ya yi jawabi a
inda ya ce:
"Idan akwai wanda ya cancanci Khadija, to
shi ne Muhammad. Haka kuma idan akwai wanda ya cancanci Muhammadu, to ita ce
Khadija."
Khadija ta kasance mace: Mai kwantar masa da
hankali, mai tallafa masa, mai bayar da dukiyarta don alheri.
Sun haifi 'ya'ya shida kamar haka:
1. Qasim
2. Zainab
3. Ruqayyah
4. Ummu
Kulthum
5. Fāṭimah
6. Abdullah
(Tayyib/Tahir)
Duk ’ya’yan Annabi, in banda Ibrahim, daga
Khadija ne.
AIKO SHI DA SAƘO ﷺ
A shekara ta 40 ne, a cikin watan Ramaḍan, a wata dakiƙa
mafi daraja a tarihin duniya, Mala’ika Jibrilu ya zo wa ma’aiki Alaisalam a kogon Hira,
ya ce:
“Iqra’
—Yi karatu.”
Daga nan Annabci ya fara.
Zuciyarsa ta yi nauyi, jikinsa ya xauki rawar
sanyi yana kar-karwa, ya dawo gare ta Sayyida Khadijah yana cewa:
"Zammilūnī, zammilūnī"
“Ku
lullube ni! Ku lullube ni!”
A take Khadija ta kwantar masa da hankali tana
mai cewa:
“Kada
ka ji tsoro. Wallahi babu wani abu mara kyau da zai taɓa
samun ka. Domin kai mutum ne mai yawan zumunci, mai taimakon marasa ƙarfi, mai ciyar da talakawa, mai girmama baƙi.
Khadija ta kasance mace ta farko da ta yi
shahada. Allah Ya zaɓe ta, Ya ɗaukaka
ta, Ya girmama, ta har Mala'ika Jibrilu ya gaisheta tare da yi mata bushara da
gida Aljanna.
Kamar yadda Hadisi ya tabbata cewa:
، قَالَ عنه الله رضي هُرَيْرَةَ أَبِي عَنْ:
جَاءَ
جِبْرِيلُ إِلَى النَّبِيِّ ﷺ فَقَالَ: "يَا رَسُولَ اللَّهِ، هَذِهِ
خَدِيجَةُ قَدْ أَتَتْ، مَعَهَا إِنَاءٌ فِيهِ إِدَامٌ أَوْ طَعَامٌ أَوْ شَرَابٌ،
فَإِذَا هِيَ أَتَتْكَ فَاقْرَأْ عَلَيْهَا السَّلَامَ مِنْ رَبِّهَا وَمِنِّي،
وَبَشِّرْهَا بِبَيْتٍ فِي الْجَنَّةِ مِنْ قَصَبٍ لَا صَخَبَ فِيهِ وَلَا نَصَبَ".
Ma’ana:
Jibrilu ya zo wurin Annabi ﷺ ya
ce:
"Ya Manzon Allah! Ga Khadija ta zo, tana ɗauke
da abin ci ko abin sha. Idan ta iso gare ka, ka gaishe ta da sallamar Ubangiji,
kuma ka gaishe ta da sallamarka. Ka kuma yi mata bushara da cewa Allah Ya
tanadar mata gida a Aljanna na lu’u-lu’u, ba hayaniya a cikinsa kuma babu
gajiya."
Sahih al-Bukhari – Hadisi
mai lamba (3820)
Sahih Muslim – Hadisi mai
lamba (2432)
Ta rasu a shekarar ‘Āmul Ḥuzn — Shekarar Baƙin Ciki, saboda irin matsayinta a rayuwar
Annabi ﷺ.
BABI NA 5
Koyarwar
Annabi ﷺ
Kan Imani (Aqida)
1. Tauhidi
Manzon Allah ﷺ
ya zo da sakon tabbatar da Tauhidi, wato kadaita Allah a cikin:
·
Rububiyya: Yarda da cewa Allah shi ne kaxai mahalicci, mai rayawa kuma da
kashewa.
·
Uluhiyya: Bauta ga Allah shi kaɗai
ba tare da haxa komai da Shi ba.
·
Sifofi:
Yarda da dukkan sifofin kamalar Allah kamar yadda suka zo a cikin Alƙur’ani
da Hadisai.
Allah ya yi hani ga shirka, (wato haxa wani da shi) domin shirka
ita ce babbar kafa da ta jawo halakar al’umman baya, haka nan itace babbar
kofar da ke fitar da bawa daga musulunci a take.
2. Yarda Da Annabci Da Bin Koyarwar Manzon Allah ﷺ
Ma’anar Yarda da Annabci (Imanun bi an-Nubuwwah)
Yarda da annabci na nufin:
·
Gaskata cewa Annabi Muhammad ﷺ bawan Allah ne kuma ManzonSa.
·
Allah ne ya aiko shi da sakon shiriya ga dukkan al’umma.
·
Ya zo da gaskiya, ba ya magana da son rai.
Allah Madaukakin Sarki Ya ce:
:﴿ وَمَا آتَاكُمُ ٱلرَّسُولُ فَخُذُوهُۥ ۖ وَمَا نَهَىٰكُمْ
عَنْهُ فَٱنتَهُوا۟
Ma’ana
“Abin da Annabi ya baku ku karɓa, abin da ya hana ku ku guje shi.” (Al-Hashr: 7)
Abubuwan da ke cikin yarda da Annabci:
1. Gaskata shi cikin zuciya.
2. Furta shahada da harshe.
3. Bin koyarwarsa a zahiri da ɓoye.
4. Kaunar sa sama da kaunar duk
abin da mutum yake so.
5. Karrama shi ba tare da wuce
gona da iri ba.
6. Yarda da hukuncinsa a dukkan
lamura.
Inda Yarda da Annabci take kai mutum
Yin imani da Annabi ﷺ
yana inganta zuciya, yana kawar da shakku.
Shi ne abin gwajin imanin kowanne bawa.
Allah Ya ce:
“Ba su yi imani ba har su yarda da hukuncinka.” (An-Nisa'i: 65)
Duk wanda ya bi Annabi ﷺ
ba zai ɓata ba, domin Annaba ne
jagoran kaiwa ga gafara da dukkan alheran duniya.
Wanda ya gaskata Annabi kuma ya bi shi, to wannan Aljanna ce makomarsa.
Bin Koyarwar Annabi ﷺ (Ittiba’u Sunnah)
Bin koyarwar Annabi ﷺ
na nufin:
·
Yin ibada kamar yadda ya koyar.
·
Guje wa abin da ya hana.
·
Yin mu'amala da halaye kamar yadda ya koayar kuma ya yi.
·
Karɓar rayuwarsa da koyarwarsa a
matsayin jagora.
Siffofin bin koyarwar Annabi
1. Bin koyarwarsa da niyya ta
samun yardar Allah, ba don duniya ba.
2. Bin koyarwarsa a zahiri da ɓoye.
3. Bin koyarwarsa cikin sauƙi ba tare da tsanantawa ba.
4. Bin koyarwarsa cikin ilimi, ba
cikin son rai ba.
Wuraren Da Ya Kamata Musulmi Ya Fara Biyayya da Bin Sunnah
A cikin ibada
·
Yin sallah kamar yadda Annabi ﷺ ya yi.
·
Yin azumi da hajj ko umrah bisa
koyarwarsa.
·
Koyon alwala da tsarki yadda ya yi.
A cikin mu’amala
·
Aikata Gaskiya a dukkan mu’amala.
·
Yin Adalci a dukkan ayyuka.
·
Rashin cin amana.
·
Kyautata mu'amala ga abokan hulɗa.
A cikin halaye
·
Zamantowa mai tausayi da ladabi, da natsuwa a kowanne yanayi.
·
Rashin kamun harshe wajen aikata zagi, ko cutar da mutane.
·
Kulawa da marasa ƙarfi da tallafamusu.
A
cikin zamantakewa
·
Kyautata wa iyaye.
·
Kyautata wa mata da yara.
·
Kula da makwabci da jama’a.
5. Dalilan da yasa dole a bi Annabi ﷺ
Annabi ﷺ shine mafi kusanci da wahayi,
shi ne mafi sani ga Addini, kuma mafi daraja a dukkan bayin Allah.
Allah ya umurce mu da biyayya gare shi
Biyayya ga Annabi ita ce biyayya ga Allah. Kaurace wa koyarwarsa na kaiwa
ga ɓacewa.
Shi ne mafi kyawawan halaye da kyautatawa
Allah Ya ce:
“Hakika kana da ɗabi’a
mafi girma.” (Al-Qalam:
4)
Rayuwarsa ita ce mafi dacewa ga ɗan Adam
Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam ya yi jagoranci, ya yi aure, ya
yi kasuwanci, ya yi yaƙi, ya yi zaman lafiya.
Dukkan fannonin rayuwasa akwai abin koyi a cikinsu.
Alamar Wanda Ya Yarda Da Annabi Kuma Yake Bin Koyarwarsa
1. Tsoron
Allah a voye da bayyane.
2. Yin
sallar dare ko lokutan da ake barci.
3. Gaskiya
da amana a kowane hali.
4. Tausayi
da mutunci ga kowa.
5. Rashin
aibata mutane ko yawan faɗa.
6. Neman
halal da guje wa abin da ya haramta.
7. Yawaita
yin salati a gareshi.
Yarda da annabci da bin koyarwar Annabi ﷺ shine ginshiƙin Musulunci. Duk wanda ya zamo mai yarda da bi koyarwarsa zai zamo:
·
Zuciyarsa za ta tsarkaka.
·
Halayensa za su gyaru.
·
Al’amuransa za su zamo masu albarka.
·
Makomarsa ita ce Aljanna.
3. Imani da Mala’iku, Littattafai da Kaddara
Manzon Allah ﷺ ya
karfafa imani da wanzuwar Mala’iku da yin Imani da su, da Imani da Littattafan
Allah kuma su zamo su ne jagora ga dukkan rayuwa mu. Sannan mu yarda da qaddara
mai kyau da mara kyau duk mu amince daga Allah suke.
Koyarwar Annabi ﷺ
Kan Sallah
1. Muhimmancinta
Sallah ita ce ginshiƙin Musulunci. Manzon Allah ﷺ ya nuna cewa sallah ita ce farkon abin da za a tambayi bawan a ranar
alqiyama, in tayi kyau za a karvi sauran ayyukan sa, in kuma batayi kyau ba, to
baza a duba dukkan sauran ayyukan da ya aikata ba.
2. Tsarin Sallar Annabi ﷺ
Annabi ya koya mana:
·
Tsarki da yin alwala cikin ladabi.
·
Tsayuwa da nutsuwa a cikin sallah.
·
Karatun Fatiha da surori.
Musamman ya umurci mutane da cewa:
"Ku yi sallah kamar yadda kuka ga ni ina yi."
3. Tarbiyyar Sallah
– Sallah tana hana alfasha da mummunan aiki.
– Tana qara tsoron Allah da natsuwa.
– Tana magance damuwa da munanan halaye.
Koyarwa Kan Azumi
– Azumi yana tsarkake ruhu da zuciya.
– Yana koyar da haƙuri, juriya da jinkan raunana wato
talakawa.
Kyawawan Halaye a Lokacin Azumi
Annabi ﷺ ya ce:
·
Wanda yake azumi ya kiyaye harshensa da gabobinsa.
·
Ya guji zagi, tsinuwa, da yawan jayayya.
·
Ya zama mai ƙoƙarin samun lada wajen yawaita addu'a da sadaqa.
Bukatar Ciyarwa da Tausayi
– Annabi ﷺ ya kasance mafi karamci a
Ramadan.
– Ya koyar da buda baki cikin sauƙi da rashin wahala.
Zakka, Sadaka da Kyautatawa
1. Ma’anar Zakka
Zakka tana tsarkake dukiya, tana kuma kawo albarka.
Annabi ﷺ ya yi hani ga qin bada zakka
a dukiya, in har ta kai yawan da za a fitar da zakkar.
Kyautatawa ga Talakawa
Annabi ﷺ Ya nuna cewa akwai lada mai yawa
wajen taimakon marayu, da marasa lafiya, da miskinai da mabuqata.
– Ya ce: “Ku ceci kanku daga wuta ko da da kashi daya na dabino.”
Sadakatu Jariya
– Gina masallatai
– Koyar da ilimi
– Samar da ruwan sha
Wadannan duk suna ci gaba da zama lada bayan mutuwa.
Halayen Annabi ﷺ
(Akhlaq)
1. Haƙuri
– Annabi ya jure wahalhalu da cin zarafi.
– Idan aka zubar masa jini a Ta’if, bai yi addu'ar halaka ba.
2. Gaskiya da Amana
– Kafin aiko shi, an san shi da “Al-Amin”.
– Bai taɓa karya ba ko cuwa-cuɗi.
3. Tausayi
– Ya tausaya wa matasa, tsofaffi, marayu, talakawa da mata.
– Ya nuna kyakyawan fuska da dariya mai annashuwa.
Iyali, Zumunci da Auren Annabi ﷺ
1. Darajar Iyaye
Ya ce:
“Aljanna na ƙarƙashin ƙafafun uwa.”
– Ya jaddada kula da uba, uwa, kakanni da ‘yan uwa.
2. Auren Annabi ﷺ
Dukkanin Auren da Ma’aiki Alaihissalam ya yi, yana nuna zumunci, da kunya,
da tausayi yana yawan kyautatawa ga matansa. Ya kasance yana taimakawa matan sa
a aikace-aikacen gida.
3. Tarbiyyar Yara
Ma’aiki Alaihissalam yana wasa da yara, yana musu addu’a, ya koya musu
gaskiya, da tsoron Allah da nutsuwa.
Shugabanci da Tsarin Siyasar Annabi ﷺ
1. Shura
Ma’aiki Alaihissalam ya gina gwamnatin Madina bisa tattaunawa da
sahabbansa tare da neman shawara daga garesu. A tsarin shugabancin sa bai yarda
da zalunci ba, balle cin zarafin juna.
2. Adalci
Ma’aiki Alaihissalam ya haramta cin hanci da rashawa, yana hukunci ga kowa
bisa gaskiya da adalci.
3. Kula da Talakawa
Annabi ﷺ ya ce:
“Duk wanda ba shi da tausayi, Allah ba zai tausaya masa ba.”
Koyarwa Kan Kasuwanci da Hulɗar Zamani
Bincike da Gaskiya a Ciniki
Ma’aiki Alaihissalam ya haramta cin riba a dukkan kasuwanci, ya haramta zamba,
da boye aibu a cikin cinikayya, yana bayyana cewa yin gaskiya a kasuwanci ytana
kawo albarka.
Mu’amala da Mutane
Ma’aiki Alaihissalam ya kasance yana kare harshen mutum, yana kula da haƙƙin makwabta, sannan bai yarda
da a cutar da kowa ba.
3. Sana’a da Neman Halal
Annabi ﷺ ya koyar da cewa neman halal
ibada ne, domin shi ma ya taba yin kiwon dabbobi da cinikayya.
Darajar Ilimi da Malamai
Wajibcin Neman Ilimi
Annabi ﷺ ya wajabta ga kowane Musulmi da
ya nemi ilimin da zai gyara addininsa, domin shi Ilimi haske ne da ke yaye duhun
jahilci.
Girman Mai Ilimi
Annabi ﷺ ya bayyana cewa su Malamai magada
Annabawa ne, kuma Allah yana ɗaukaka
darajar masu ilimi.
Aiki da Ilimi
Annabi ﷺ ya ce:
“Ilimi ba ya amfani sai idan an yi aiki da shi.”
Koyarwa Kan Tsarkake Zuciya da Ibadu
Tawakkali
Annabi ﷺ ya kouar da dogaro ga Allah
tare da miqa dukkan lamara gareshi.
2. Zikri da Istigfari
Annabi ﷺ ya sanar da mu cewa zikiri yana
magance damuwa, sannan yana kawo nutsuwa. Sannan ya kasance yana yawan neman
gafara fiye da sau 70 a rana, domin zikiri yana qankare zunubai, yana qara
arziki.
Tuba da Tsoron Allah
Annabi ﷺ ya karfafemu da yawan tuba
saboda yawan tuba yana qarawa ɗan
Adam daraja, tareda da koyar da cewa, tsoron Allah shi ne ginshiƙin dukkan alheran duniya da
lahira.
Koyarwar Annabi ﷺ
ta shafi kowane fanni: imani, ibada, mu’amala, halaye, siyasa, zamantakewa, da
tarbiyya. Wanda ya bi koyarwarsa zai rayu cikin nutsuwa da haske a duniya da
lahira.
BABI NA 6
MU'UJIZOJIN
MANZON ALLAH (SAW)
1. Ma’anar Mu’ujiza
Mu’ujiza ita ce wani abin al’ajabi wanda ya sava wa tsarin dabi’a, Allah
Yana bayar da ita ga Annabawa domin tabbatar da gaskiyar saƙon da suka zo da shi.
Allah Madaukakin Sarki ya ce:
“Manzanni ba su da wani abin da ya rataye a kansu face isar da saƙo bayyananne.” (Surah
An-Nahl: 35)
2. MU’UJIZAR DA TA FI GIRMA: ALƘUR’ANI
2.1. Dalilin da yasa Alƙur’ani
Mu’ujiza ce
Alƙur’ani shi ne mafi girman mu’ujiza ce saboda:
·
KalamanSa sun gagari malaman Larabawa a lokacin Jahiliyya.
·
Ya taho da ilimin da ya zarce duk tunanin ɗan Adam.
·
Ya kasance hujja mai xorewa har ƙarshen duniya.
Allah Ya ce:
“Idan mutane da aljannu sun haɗu don su kawo makamancin wannan Alƙur’ani,
ba za su iya ba…”
(Surah Al-Isra: 88)
2.2. Hadisin da ya tabbatar da mu’ujizar Alƙur’ani
Annabi (SAW) ya ce:
“Babu wani Annabi da Allah ya ba shi mu’ujizojin da mutane suka gaskata
shi da su. Amma abin da aka ba ni shi ne Wahayi (Alƙur’ani).
Ina fatan in kasance mafi yawan mabiya a ranar ƙiyama.”
(Bukhari da Muslim)
3. MU’UJIZOJIN DA SUKA FARU TUN YANA QARAMI
3.1. Tsaga Kirjin Annabi (SAW)
Lokacin yana ƙarami a gidan Halima Sa’adiyya, Mala’ika Jibrilu ya zo, ya tsaga
kirjinsa, ya cire wani ɓangare
“hazzun-shaidan” wato wani abu da ka iya zama rabo na Shaixan Allah ya cireshi
da ga zuciyarsa, ya tsarkaketa.
Hadisin Anas (RA) ya ce:
“Jibrilu ya zo ya tsaga kirjinsa, ya fitar da wani baƙin abu ya ce: wannan ne ɓangaren shaidan da yake nak.”
(Muslim)
4. MU’UJIZOJIN A LOKACIN AIKIN ANNABCI
4.1. Ƙaruwar Abinci
A lokuta da dama abinci ya nininku fiye da yadda ake tsammani.
Misali – Abincin Jabir
Jabir (RA) ya ce:
“Annabi ya sanya hannunsa cikin gurasar, sai ta yi yawa har ta wadaci
mutane dubu.”
(Bukhari)
4.2. Fitar Ruwa daga Hannunsa
An tabbatar da cewa ruwa ya fito daga yatsun Annabi (SAW) har Sahabbai
suka sha.
Jabir (RA) ya ruwaito:
“Na ga ruwa yana zuba daga yatsun Annabi kamar zubar ruwa daga rijiya.”
(Bukhari 3572)
4.3. Kukan Rakumi
Annabi (SAW) ya share hawayen wani rakumi da aka zalunta, raqumin ya
gane Annabi kuma ya kai kuka tare da neman taimakoSa Salallahu Alihi wasallam.
“Rakuninsa ya zo wurin Annabi ya yi kuka, sai Annabi ya ce: ku ji tsoron
Allah a kan waɗannan dabban.”
(Abu Dawud)
4.4. Bishiya tayi tafiya ta je zuwa ga Annabi
An ga bishiya ta taso daga inda take zuwa wajen Annabi, sannan ta koma.
“Bishiya ta zo gabansa ta tsaya, sannan ya mayar da ita inda take.”
(Tirmidhi)
5. MU’UJIZOJIN TAIMAKON ALLAH
5.1. Saukar Mala’iku a Yaƙin Badar
Allah ya saukar da mala’iku domin tallafa wa musulmai a lokacin da ake
tsaka da yaqin Badar.
“(Allah) Ya saukar da mala’iku domin su taimaka muku.”
(Surah Al-Anfal: 9–12)
5.2. Tsira a lokacin Hijira
A likacin da Ma’aiki Alaihissalam zai yi hijra, makiyansa sun kewaye
gidansa, domin du cutar da shi kuma su hanashi yin hijira, amma sai Allah Ya
lullube idanunsu da barci. Kamar yadda ya faqa cikin littafinsa maitsarki:
“Mun sanya wani shinge a gabansu da bayan su, sai suka zama makafi.”
(Surah Yasin: 9)
Hadisi:
“Suka zuba masa ido amma ba su gan shi ba.”
(Ibn Hibban)
6. ANNABCI: BAYANIN ABUBUWAN DAZA SU FARU
Annabi (SAW) ya annabcin abubuwa da dama kuma suka faru kamar yadda ya
faɗesu:
6.1. Faxuwar Farisa da Rum
Manzon Allah (SAW) ya bayyana cewa lallai kisra da rum zasu faxi, kuma
abin ya faru kamar yadda ya faxa:
Ya ce: “Za a warware kujerar Kisra (sarkin Farisa).” Kuma haka ya
faru.
(Bukhari)
6.2. Warwatsuwar Musulunci
Manzon Allah (SAW) ya bayyana cewa Addinin Musulunci zai watsu a ko ina
gabas da yamma kudu da aewa, kamar yadda ya faxa a Hadisi:
“Addinina zai kai har inda rana ta faɗa da inda take fitowa.”
(Ahmad)
7. ISRA’I DA MI’IRAJI
Tafiyar da akyi da Annabi Alaihissalam daga Masallacin Harami zuwa
Masallacin Al-Aqsa, sannan aka tafi da shi zuwa sama wato Mi’iraaji, inda ya
gana da Allah ya karvo Sallah, kamar yadda Allah ya faxa cewa:.
“Tsarki ga Wanda Ya tafiyar bawansa daga Masallacin Harami zuwa Masallacin
Al-Aqsa…”
(Surah Al-Isra: 1)
Hadisi:
Ya sadu da Annabawa, sannan aka wajabta masa sallolin farilla.
(Bukhari da Muslim)
8. MU’UJIZOJIN WARKARWA
8.1. Warkar da Sahabbai
Lokaci da Sayyadi Aliyu (RA) yana ciwon Ido, ya shafi idon nasa da
hannayensa, a take sai idon ya warke nan take.
Kamar yadda Hadisi ya fada:
“Sai Annabi ya shafe idanunsa da hannunsa, ya warke kamar bai taba ciwo
ba.”
(Muslim)
9. MU’UJIZAR DA TA DAWWAMA: SUNNARSA
Duk sauran mu’ujizojin Annabawa suna wuce wa ne bayan
Annabwan sun faku, Amma shi Manzon Allah (SAW) abubuwan da ya bari suna nan har
zuwa ranar Alqiyama zasu tabbata, wato Alƙur’ani
da Sunnarsa (Hadisai) da sauran kq’idodin rayuwa da zamantakewa da ya bar mana.
Hadisi:
“Na bar muku abu biyu, ba za ku bata ba matuqar kun riƙe su: Littafin Allah da
Sunnata.”
(Malik a Muwatta')
Mu’ujizojin Manzon Allah (SAW) hujja ce ta gaskiyar saƙon sa da matsayin da Allah Ya girmama shi da shi.
Rayuwarsa ta tabbata a matsayin jagora, alƙibla, da misali na nagarta.
BABI NA 7
KIRAN
ANNABI (SAW) ZUWA TAUHIDI A MAKKAH
Shekaru Uku a ɓoye, da Shekara Goma a bayyane
Da Allah Madaukakin Sarki Ya aiko Annabi Muhammadu (SAW) da saƙon Musulunci, farkon abin da
ya fara kira shi ne Tauhidi, wato a bauta wa Allah shi kaɗai ba tare da haɗa wani da Shi ba. Wannan kira
shi ne tushen dukkan hukunce-hukuncen Musulunci.
A lokacin da aka fara saukar da wahayi, daular Qur’aysh da mazaunanta
cike suke da shirka, bautar gumaka, zalunci da ɗabi’u marasa kyau. Saboda haka, Manzon Allah
(SAW) ya fara kira a hankali, a tsanake, domin a kare saƙon daga barazanar Quraysh tun
farko.
2. Farkon Kira: Shekaru Uku a ɓoye
2.1. Dalilin da ya sa yin kira a ɓoye
Annabi (SAW) ya yi kira a ɓoye shekaru uku saboda: Matsin
lambar Qur’aysh da azabtar da duk wanda ya ƙi bautar gumaka. Kuma domin shugaba
ya kafa ƙananan tushe na muminai masu aminci daga makusantansa. Kuma duk wani
yunkuri na bayyana kiran a wannan lokaci zai iya kawo hare-hare tun da wuri.
Allah Ya ce:
“Ka
yi haƙuri da abin da suke faɗi.”
(Surah Ta-Ha: 130)
2.2. Suwaye na farko da suka amsa kira?
A wannan lokacin ne makusanta ga shugaba suka fara karɓar Musulunci, daga cikin na
farko farkon amas kira sun hadar da:
·
Sayyida Khadija (RA)
·
Abu Bakr Siddiq (RA)
·
Aliyu bn Abi Dalib (RA)
·
Zaid bn Haritha (RA)
·
A wasu riwayoyi kamar Bilal, Ammar, Sumayya da Yasir.
2.3. Gidan Al-Arqam
Ina ne Gidan Arqam: shine gidan da Annabi (SAW) yake tara sahabbansa a ɓoye, yana koyar da su Tauhidi,
karatun Alƙur’ani da ladubban Musulunci.
Hadisi:
“Muminai na farko sun kasance ƙasimi-ƙasimi, ba su da yawa.”
(Ibn Sa’d, a Ṭabaqāt)
3. Kiran Bayyane: Na tsawon Shekara Goma
Bayan an gina Imani a zukatan ƙananan muminai a ɓoye, sai Allah ta;ala Ya yi
umarni da ya fito yayi kira a bayyane, kamar yadda ya bayyana a cikin littafin
sa maitsarki:
أَنْذِرْ عَشِيرَتَكَ الْأَقْرَبِينَ
“Ka
yi wa danginka mafi kusa gargaɗi.”
(Surah Ash-Shu’arā: 214)
Wannan shi ne matakin da ya canza yanayin kira daga ɓoye zuwa fili.
3.1. Kiran farko a kan Dutsen Ṣafa
Annabi (SAW) ya hau dutsen Ṣafa ya ce:
“Da zan faɗa
muku cewa akwai mayaƙa suna zuwa daga bayan wannan dutse, shin za ku
gaskata ni?”
Suka ce:
“Mun san ba ka taɓa
yin ƙarya ba.”
Sannan ya ce:
“Ni Manzon Allah ne gare ku, ina gargadin ku daga azabar da ta gabato.”
(Bukhari)
3.2. Turjiya daga Qur’aysh
Tun daga wannan rana Qur’aysh suka fara yaƙi da saƙon Tauhidi, suna fara sukar sa
da yunƙurin kashe shi, da tozarci ga muminai tare da fatattakar dukkannin waxanda
suka karɓi Addinin Musulunci
3.3. Ayyukan Annabi (SAW) a Shekaru Goma
A cikin wannan lokaci wato shekaru Goma, Ma’aiki Alaihissalam ya yi
abubuwa masu muhimmanci kamar:
1. Kiran jama’a daga kowane matsayi
Ya yi kira ga talakawa da matasa da bayi da attajirai har da shugabanni.
2. Jarabawar Musulmai
Muminai da suka amshi wannan kira daga shugaban halitta sun sha tsananin
azaba, waxanda suka sha azabar sun haxar da:
·
Sayyadina Bilal (RA) da azabarsa a rana, domin ana kwantar da shi ne a
tsakiyar rana mai zafi cikin sahara a xora dutse a cikin sa akan lallai sai ya
bar addinin Musulunci
·
Yasir da Sumayya (RA) sune na farko da sukayi shahada, don sun ki barin Addinin Musulunci
aka kasha su
·
Hijira ta farko zuwa Habasha: sabo da tsanani azabar da muminai ke ciki
yasaka wasu daga cikin su yin kaura zuwa kasar Habasa.
3. Da’awah cikin hikima
Allah Ya ce:
“Ka kira zuwa hanyar Ubangijinka da hikima da nasiha mai kyau.”
(Surah An-Naḥl: 125)
Annabi Salallahu Alaiji wasallam ya yi amfani da hikima wajen isar da saƙon Tauhidi, yana kauce wa
tashin hankali.
4. Shiga Tsakanin Qabilu
Annabi (SAW) yana ziyartar ƙabilu a lokacin hajji yana
cewa:
“Ku ce: ba wani abin bautawa sai Allah, za ku ci nasara.”
(Ahmad)
4. Muhimman Abubuwan da kira a Makkah ya kunsa
1. Tauhidi
Kira zuwa ga bautawa Allah shi kaɗai ba tare da haɗa
wani da Shi ba.
2. Kiyaye da zalunci
Annabi Alaihissalam ya faɗakar da quraysh da su daina azabtar da talakawa da mata da bayi.
3. Girmama hakkin ’yan uwa
Annabi Alaihissalam ya kira su zuwa adalci da kaucewa cin amanar jama’a.
4. Kiyaye alfarmar iyaye
Annabi Alaihissalam yayi kira da a kare alfarmar iyaye a girmamasu, a
kula da dangantaka waro yan’uwantaka, ya qarfafa sada zumunci da girmama maqota.
5. Sakamakon Kiran Shekaru Goma
1. An sami ƙaramin al’umma ta muminai masu aminci.
2. An shimfiɗa tushe da ba za a gusar da
shi ba.
3. An samu mummunan turjiya daga
Qur’aysh wadda ta haifar da hijira zuwa Madina.
4. Saƙon Tauhidi ya watsu a hankali
har zuwa lokacin da Allah Ya buɗe
Madina ga Musulunci.
Kiran Annabi (SAW) zuwa Tauhidi a Makkah na ɓoye da na bayyane ya kafa
ginshikin Musulunci.
Shekaru uku na farko sun gina ƙananan muminai, shekaru goma na bayyane kuwa sun tabbatar da haƙurinsa, jajurcewa da tsantsar
da’awah.
Daga wannan, Musulunci ya samu direba, tushe, da al’umma da suka zama
madogara bayan hijira.
BABI NA 8
HIJIRAR MANZON ALLAH ﷺ
MA’ANAR HIJIRA
Hijira na nufin barin ƙasa ko wuri zuwa wani wuri
domin kare addini da imani, da kuma samun damar bauta wa Allah cikin
’yanci.
Hijirar Manzon Allah ﷺ ita
ce barinsa Makkah zuwa Madinah a shekarar 622 Miladiyya, wacce ta zama tushen
tarihin Musulunci (Hijira Calendar).
DALILAN HIJIRAR MANZON ALLAH ﷺ
1. Tsananin takura daga kafiran Makkah
Kafirai sun tsananta wa
Musulmin da suka bar bautar Gumaka da tsananin azba ga irin su Bilal bn Rabah,
sannan suka kashe Sumayyah (wacce ta zamo farkon shahidai), haka zalika sun lillace
Banu Hashim daga dukkan wata mu’amala.
2. Makirci na kashe Annabi ﷺ
Kafirai sun yanke shawarar kashe Annabi ﷺ
gaba ɗaya, a cikin wata tattaunawa da sukayi suka amince
da su tura matasa daga mabanbantan qabilu din su kasha shi.
Dalili daga Al-Qur’ani:
Fassara:
“Ka tuna lokacin da kafirai suka shirya makirci a kanka, ko su tsare ka, ko su
kashe ka, ko su fitar da kai. Suna shirya makirci, Allah kuma yana shirya, kuma
Allah Shi ne mafi kyawun masu shirya makirci.”
SHIRIN HIJIRA
1. Izinin Allah
Annabi ﷺ bai
bar Makkah ba sai da Allah Ya ba shi izini.
2. Zabar Abu Bakr (RA) a matsayin abokin tafiya
Abu Bakr (RA) ya kasance shine Annabi (SAW) ya
zava domin suyi tafiyar tare.
3. Shigarsu Kogon Thawr
Ma’aiki Alaihissalam da Abubakar (AS) Sun ɓuya
a Kogon Thawr na tsawon kwanaki uku a hanyarsu ta tafiya Madina.
ABIN DA YA FARU A KOGON THAWR
Kafirai sun zo har bakin kogon. Abu Bakr (RA)
ya ji tsoro.
Hadisi (Bukhari da Muslim):
مَعَنَا اللَّهَ إِنَّ تَحْزَنْ لَا
Fassara:
“Kada ka damu, lallai Allah Yana tare da mu.”
Hujjar Qur’ani:
“Idan ba ku taimake shi ba, to lallai Allah Ya taimake shi, lokacin da kafirai
suka fitar da shi, su biyu ne kawai, suna cikin kogo...”
(Suratut Taubah: 40)
TAFIYA DAGA MAKKAH ZUWA MADINAH
Wanda ya Jagoranci tafiyar shi ne: Abdullahi bn
Uraiqit (duk da bai Musulunta ba)
Sun bi hanyar da ba hanyar da ake bi kai tsaye ba,
don bavadda sawu da nuna hikima a cikin tafiyar
Abubuwa masu ban mamaki sun faru, ciki har da:
Labarin Suraqa bn Malik wanda ya so kama
Annabi ﷺ amma Allah Ya kare shi
A lokacin Hijirar Annabi Muhammad ﷺ daga Makkah zuwa Madina,
mushrikan Quraysh suka sanya lada mai yawa ga duk wanda ya kama Annabi ﷺ ko
Sahabinsa Abubakr (RA).
Saboda wannan lada da aka sanya, Suraqa bn Mālik bn Ju‘shum ya
fito da niyyar sai ya nemo su a duk inda suke.
Da ya hango su ya kusanta zuwa wajen su a cikin
hamada, sai dokin Suraqa ya fara nutsewa a cikin ƙasa,
in ya jiya sai dikin yaci gaba da tafi, in ya sake bin su sai ya cigaba da
nutsewa, haka yayi tayi sau da dama, har sai ya gane cewa wannan kariya ce
daga Allah ga Annabinsa ﷺ. Sai tsoro ya kama shi, ya
roƙi Annabi ﷺ da
ya yi masa addu’a, ya kuma yi alƙawarin
ba zai cutar da su ba.
Sai Annabi ﷺ ya
yi masa addu’a, dokinsa ya kuɓuta, sannan Annabi ﷺ ya
ba shi bishara mai girma, yana cewa:
“Yaya za ka ji, ya Suraqa, idan ka sa munduƙan Kisra (Sarkin Farisa) a
hannunka?”
Daga baya, bayan Musulunci ya yi ƙarfi a zamanin Sayyidina Umar bn Khattab (RA), bayan
ancinye Kisra da yaqi da aka kawo dukiyar Kisra, sai aka bawa Suraqa ya
sa munduƙan
Kisra, kamar yadda Annabi ﷺ ya faɗa
tun farko.
Wannan labari yana nuna:
·
Kariyar Allah ga Manzonsa ﷺ
·
Cikar annabcin Annabi ﷺ
·
Ikon Allah kan dukkan al’amura
·
Kuma yadda Allah ke juya maƙiyi ya zama mai imani
Daga baya Suraqa ya karɓi Musulunci, ya
kuma zama Sahabi mai daraja.
SHIGOWAR MANZON ALLAH ﷺ MADINAH
1. Tarba mai girma
Bayan kammala Hijira daga Makkah,
Annabi Muhammad ﷺ ya iso yankin Yathrib (Madina) a cikin
watan Rabi‘ul Awwal, shekara ta 13 bayan fara wahayi. Shigowarsa Madina
ya zama babban sauyi a tarihin Musulunci.
1. Tsayuwarsa a Qubā’
Da Annabi ﷺ ya
iso kusa da Madina, ya fara sauka a Qubā’, inda ya kwana na wasu kwanaki (kimanin huɗu).
A can ne ya gina Masallacin Qubā’, masallaci na farko a Musulunci, inda ya hadu da
Sahabbai, yana jagoranci sallah tare da su.
Allah ya faxa a Qur’ani:
(Suratut Taubah: 108)
2. Shigowarsa cikin Madina
A ranar Juma’a, Annabi ﷺ ya
nufi Madina daga Qubā’. A hanya ya yi sallar
Juma’a ta farko a wuri da ake kira Banu Salim bn ‘Awf. Daga nan ya
ci gaba da tafiya har ya shiga cikin birnin Madina.
3. Yadda aka tarbe shi
Mutanen Madina – Ansar
(Aus da Khazraj) maza da mata, yara da manya – sun fito suna murna, suna
tarbarsa da girmamawa. Sun riƙa Raira
waƙar maraba:
“Ṭala‘al-badru ‘alaynā…”
Sun nuna farin ciki da albarka saboda shigowar
Manzon Allah ﷺ. Kowanne gida yana fatan Annabi ﷺ ya
sauka a wajensa.
4. Zabin inda zai sauka
Annabi ﷺ ya
ce:
“Ku bar rakumina, domin an umarce ta.”
Rakumar tasa Al-Qaswā’ ta tsaya a wani fili na marayu biyu daga Banu
Najjar. A nan ne: Annabi ﷺ ya sauka a gidan Abu
Ayyub al-Ansari (RA). Daga
baya aka gina Masallacin Annabi ﷺ a wannan fili.
5. Ma’anar wannan tarba
Tarbar Annabi ﷺ a
Madina ta nuna:
·
Soyayya da biyayya ga Manzon Allah ﷺ.
·
Haɗin kan Musulmi
(Muhajirai da Ansar).
·
Farkon kafuwar ƙasar Musulunci mai
cikakken tsari.
Shigowar Annabi ﷺ
Madina ya zama tushen nasarar Musulunci, kuma daga nan ne aka fara sabon
babi na tarihi mai cike da shiriya da adalci.
MUHIMMAN ABUBUWAN DA SUKA BIYO BAYAN HIJIRA
1.
Gina Masallacin Annabi ﷺ
2.
Ƙulla
‘yan uwantaka tsakanin Muhajirai da Ansar
3.
Kafa tsarin mulki (Sahifatul Madinah)
4.
Musulunci ya samu ƙarfi da ’yanci
5.
Hijira ta zama rabo tsakanin gaskiya da ƙarya
MUHIMMANCIN HIJIRA A MUSULUNCI
1. Hijira ibada ce
Annabi ﷺ ya
ce:
Fassara:
“Ayyuka suna tare da niyya… Duk wanda hijirarsa ta kasance zuwa ga Allah da
Manzonsa, to hijirarsa ta tabbata zuwa ga Allah da Manzonsa.”
BABI NA TARA
Yakokin
Annabi Muhammad ﷺ
Rayuwar Annabi Muhammad ﷺ
ba ta taƙaita ga kira zuwa ga tauhidi da koyarwa kawai ba, har ta haɗa da jagoranci a fagen tsaro
da kare Musulunci. Yake-yaken da Annabi ﷺ ya shiga ba don zalunci ko mamaya ba ne, sai dai don kare addini,
rayuka da ’yancin bauta wa Allah. Dukkan yaƙe-yaƙen sun gudana ne bisa ƙa’idojin
adalci da rahama.
Adadin Yake-yaken Annabi ﷺ
Malamai na tarihi sun yi bayani cewa:
·
Yake-yaken da Annabi ﷺ ya fita da kansa (Ghazawāt): 27
·
Yaƙe-yaƙen da bai fita da kansa ba, ya
aika sahabbai (Sarāyā): sama da 50
Wannan babi zai mayar da hankali ne kan Ghazawāt – wato yaƙe-yaƙen da Annabi ﷺ ya halarta da kansa.
Ma’anar Ghazwah da Sariyya
·
Ghazwah: Yaƙin da Annabi Muhammad ﷺ
ya jagoranta da kansa.
·
Sariyya: Rundunar yaƙi da Annabi ﷺ
ya aike ta ƙarƙashin jagorancin sahabi, shi kuma bai fita ba.
Jerin Yake-yaken (Ghazawāt) na Annabi ﷺ
1. Ghazwatul Abwā’ (Waddān) – Shekara ta 2 bayan Hijira
·
Yaƙi na farko da Annabi ﷺ
ya fita
·
Ba a yi artabu ba
2. Ghazwatul Buwāṭ
3. Ghazwatul ‘Ushayrah
4. Ghazwatul Badr al-Kubrā – 17 Ramadan, 2H
·
Babban nasara ga Musulmi
“Hakika Allah Ya taimake ku a Badar alhali kuna kaɗan.”
(Suratul Al-Imran: 123)
5. Ghazwatul Banī Qaynuqā‘
6. Ghazwatul Uhud – Shekara ta 3H
·
Jarrabawa ga Musulmi
7. Ghazwatul Hamrā’ul Asad
8. Ghazwatul Banī Naḍīr
9. Ghazwatul Khandaq (Ahzāb) – Shekara ta 5H
·
An haƙa rami domin kare Madina
“Kuma Allah Ya wadatar da muminai daga yaƙi.”
(Suratul Ahzab: 25)
10. Ghazwatul Banī Qurayẓah
11. Ghazwatul Banī Liḥyān
12. Ghazwatul Dhātur-Riqā‘
13. Ghazwatul Banī Muṣṭaliq (Muraysī‘)
14. Ghazwatul Khaybar – Shekara ta 7H
·
Nasara babba ga Musulmi
15. Ghazwatul ‘Umratul Qaḍā’
16. Ghazwatul Fatḥu Makkah – Shekara ta 8H
·
Nasara ba tare da jini ba
“Idan taimakon Allah da nasara suka zo.”
(Suratun Naṣr: 1)
17. Ghazwatul Ḥunayn
18. Ghazwatul Ṭā’if
19. Ghazwatut Tabūk – Shekara ta 9H
·
Yaƙi mafi nisa
Hikimar Yake-yaken Annabi ﷺ
·
Kare Musulmi daga zalunci
·
Kare ’yancin addini
·
Kafuwar adalci da tsaro
·
Nuna cewa Musulunci addinin zaman lafiya ne, amma ba na rauni ba
Ƙa’idojin Yaƙi a Musulunci Daga Annabi ﷺ
·
Haramcin kashe fararen hula
·
Haramcin kashe mata, yara da tsofaffi
·
Haramcin lalata amfanin gona
·
Umurnin kyautata wa fursunoni
Yake-yaken Annabi Muhammad ﷺ darussa ne na jagoranci, haƙuri da adalci. Duk da yaƙe-yaƙe sun faru, rahama da
tausayi su ne ginshiƙan tafiyarsa.
Allah Ya sanya mu cikin masu fahimtar hikimar rayuwar Annabinsa ﷺ, Ya kuma ba mu ikon koyi da
kyawawan dabi’unsa. Ameen.
Babi Na 10
MATAYEN ANNABI ALAIHISSALAM
Matan Annabi Muhammad ﷺ
suna da matsayi na musamman a Musulunci. Allah Ya kira su "Ummuhātul Mu’minīn" (Uwayen Muminai), domin girmama su da nuna
matsayin da suke da shi a rayuwar Musulmi. Tarihinsu cike yake da darussa na
tarbiyya, haƙuri, ilimi, sadaukarwa da biyayya ga Allah.
Matayen Annabi ﷺ
da Matsayinsu
Matan Annabi ﷺ
su ne matan da Annabi ya aura bisa halaccin aure. Allah Ya haramta wa muminai
su aura su bayan rasuwarsa, yana cewa:
“Annabi ya fi kusa da muminai fiye da kansu, kuma matansa uwayensu ne.”
(Suratul Ahzab: 6)
Haka kuma Allah Ya ce:
“Ba ya halatta a gare ku ku cutar da Manzon Allah, kuma ba ya halatta ku
auri matansa bayan sa har abada.”
(Suratul Ahzab: 53)
Yawan Matan Annabi ﷺ
Annabi Muhammad ﷺ
ya aura mata 11, ya rasu yana tare da 9 daga cikinsu.
1. Sayyidatina Khadija bint Khuwaylid (RA)
Nasaba da Tarihi
·
‘Yar Khuwaylid bn Asad
·
Mace mai daraja da kasuwanci a Makka
Auren ta da Annabi ﷺ
·
Annabi ﷺ ya aure ta yana da shekara
25, ita kuma tana kusan 40
·
Ita ce mace ta farko da Annabi ya aura
Falalarta
·
Ita ce ta farko da ta yi imani da Annabi ﷺ
·
Ta tallafa masa da dukiyarta da zuciyarta
Annabi ﷺ ya ce:
“Ta yi imani da ni lokacin da mutane suka kafirta, ta gaskata ni lokacin
da mutane suka ƙaryata ni.”
2. Sayyidatina Sawda bint Zam‘ah (RA)
·
Mace mai haƙuri da sauƙin kai
·
Annabi ﷺ ya aure ta bayan rasuwar
Khadija (RA)
·
Ta sadaukar da kwanakinta ga A’isha (RA) domin faranta wa Annabi ﷺ rai
3. Sayyidatina A’isha bint Abi Bakr (RA)
Matsayinta
·
‘Yar Khalifa Abu Bakr As-Siddiq (RA)
·
Mafi ilimi daga cikin mata
Falalarta
·
Ta rawaito fiye da hadisai 2,000
·
Annabi ﷺ ya ce:
“Falalar A’isha akan sauran mata kamar falalar Tharid akan sauran
abinci.”
4. Sayyidatina Hafsa bint Umar (RA)
·
‘Yar Umar bn Khattab (RA)
·
Ita ce ta ajiye mushafin Alƙur’ani
a zamanin Abu Bakr (RA)
·
Mace mai yawan azumi da sallah
5. Sayyidatina Zaynab bint Khuzayma (RA)
·
Ana kiranta Ummul Masakinai
·
Ta rasu bayan ‘yan watanni da aurenta
6. Sayyidatina Ummu Salama (RA)
·
Mace mai hikima da basira
·
Ta ba Annabi ﷺ
shawara a yarjejeniyar Hudaybiyya
·
Daya daga cikin manyan malaman mata
7. Sayyidatina Zaynab bint Jahsh (RA)
·
‘Yar ammin Annabi ﷺ
·
Allah Ya aura ta da Annabi ﷺ daga sama
“Sa’annan muka aurar da kai da ita.”
(Suratul Ahzab: 37)
8. Sayyidatina Juwayriya bint Al-Harith (RA)
·
Aurenta ya zama sanadiyyar ‘yantar da bayin kabilarta
9. Sayyidatina Ummu Habiba Ramlah bint Abi Sufyan (RA)
·
Ta yi hijira zuwa Habasha
·
Najashi ne ya aurar da ita da Annabi ﷺ
10. Sayyidatina Safiyya bint Huyayy (RA)
·
Daga zuriyar Annabi Haruna (AS)
·
Annabi ﷺ ya ‘yantar da ita sannan ya
aure ta
11. Sayyidatina Maymuna bint Al-Harith (RA)
·
Ita ce ta ƙarshe da Annabi ﷺ
ya aura
·
Aurenta ya ƙarfafa zumunci tsakanin Musulmi
Hikimar Yawan Auren Annabi ﷺ
·
Koyar da mata hukunce-hukuncen addini
·
Ƙarfafa zumunci tsakanin kabilu
·
Kula da zawarawa da marayu
·
Watsa Sunnah ta hanyar yakokinsa
BABI NA SHA XAYA
‘YA’YAYEN MANZON ALLAH ﷺ
’Ya’yan Manzon Allah Muhammad ﷺ suna da matsayi mai girma a Musulunci. Rayuwarsu ta ƙunshi manyan darussa na haƙuri, jarabawa, tausayi da
yarda da ƙaddarar Allah. Duk da cewa Annabi ﷺ shi ne mafi daraja a cikin halitta, Allah Ya jarabce shi da rasuwar
yawancin ’ya’yansa tun suna ƙanana, domin ya zama abin koyi ga al’umma wajen haƙuri da tawakkali.
Annabi ﷺ ya haifi ’ya’ya guda
bakwai (7): maza uku (3) da mata huɗu (4). Dukkansu daga Sayyidatina
Khadija bint Khuwaylid (RA) ne, sai Ibrahim wanda aka haife shi daga
Māriyah Al‑Qibtiyya (RA).
’Ya’ya Maza na Manzon Allah ﷺ
1. Al‑Qāsim bn Muhammad ﷺ
Shi ne babban ɗan
Annabi ﷺ. Da sunansa ne aka yi wa
Annabi ﷺ kunya da Abul‑Qāsim. Mahaifiyarsa ita ce
Sayyidatina Khadija (RA). Ya rasu yana ƙarami a Makka.
Darasi:
Rasuwar Al‑Qāsim ta nuna haƙurin Annabi ﷺ
da cikakkiyar yarda da hukuncin Allah tun farkon rayuwarsa.
2. Abdullahi bn Muhammad ﷺ
Ana kiransa da Ṭayyib da Ṭāhir. Mahaifiyarsa ita ce
Sayyidatina Khadija (RA). Ya rasu yana jariri. A lokacin rasuwarsa, mushrikai
suka ce Annabi ﷺ ya zama abtar (wanda
zuriyarsa ta yanke), sai Allah Ya saukar da Suratul Kawthar a matsayin
ta’aziyya da girmamawa.
“Lalle Mun ba ka Al‑Kawthar.”
(Suratul Kawthar: 1)
3. Ibrahim bn Muhammad ﷺ
Mahaifiyarsa ita ce Māriyah Al‑Qibtiyya (RA). An haife shi a Madina, ya
rasu yana da kusan watanni goma sha shida zuwa goma sha takwas. Annabi ﷺ ya yi kuka a rasuwarsa, amma
ya nuna cikakkiyar yarda da ƙaddarar Allah.
Annabi ﷺ ya ce:
“Ido na zubar da hawaye, zuciya na baƙin ciki, amma ba za mu faɗi sai abin da Ubangijinmu Ya
yarda ba.”
Darasi:
Halaccin kuka da nuna tausayi, tare da haƙuri da tawakkali.
’Ya’ya Mata na Manzon Allah ﷺ
4. Zaynab bint Muhammad ﷺ
Ita ce babbar ’yar Annabi ﷺ. Ta auri Abul‑‘Āṣ bn Rabī‘.
Ta rasu a Madina a shekara ta 8 bayan Hijira.
Darasi:
Darajar aure da kiyaye amana ko da a lokacin sabani.
5. Ruqayya bint Muhammad ﷺ
Ta auri Uthman bn Affan (RA). Ta yi hijira zuwa Habasha tare da
mijinta. Ta rasu a Madina a lokacin da Musulmi suke Yaƙin Badar.
6. Ummu Kulthum bint Muhammad ﷺ
Bayan rasuwar Ruqayya (RA), Annabi ﷺ ya aurar da ita ga Uthman bn Affan (RA). Saboda auren ’ya’yan
Annabi biyu da yayi, aka kira Uthman da Dhun‑Nurayn (Mai haske biyu). Ta
rasu a shekara ta 9H.
7. Fāṭima Az‑Zahrā’
bint Muhammad ﷺ
Ita ce ƙaramar ’yar Annabi ﷺ kuma mafi soyuwa a gare shi.
Ta auri Ali bn Abi Talib (RA). Daga gare ta ne zuriyar Annabi ﷺ ta ci gaba ta hanyar Hasan
da Husain (RA).
Annabi ﷺ ya ce:
“Fāṭima yanki ce daga jikina; duk wanda ya cutar da ita ya
cutar da ni.”
Ta rasu watanni kaɗan
bayan rasuwar Manzon Allah ﷺ.
’Ya’yan Manzon Allah ﷺ
sun kasance ginshiƙai na darasi ga al’umma wajen haƙuri, tarbiyya, tausayi da
yarda da ƙaddarar Allah. Rayuwarsu ta nuna cewa daraja a wurin Allah ba ta hana
jarabawa ba, amma tana ƙara lada da ɗaukaka
ga masu haƙuri.
Auren Nana Fāṭima
Auren Nana Fāṭima (RA) ‘yar Manzon Allah ﷺ da Sayyidina Aliyu bn Abi Ṭālib (RA) na ɗaya daga cikin auren da suka fi albarka a tarihin
Musulunci. Wannan aure ya haɗa gidan Annabci da
gidan Jarumta da Ilimi, kuma daga cikinsu Allah Ya azurta Musulunci da jikokin
Annabi (SAW)
Nana Fāṭima (RA) Ta kasance: mai tsananin kunya da tsarki, Mai
ibada da haquri, Mai
ƙaunar mahaifinta ﷺ
matuƙa
Sayyidina Aliyu bn Abi Ṭālib (RA)
Sayyidina Aliyu shi ne:
·
Ɗan ammin
Annabi ﷺ
·
Ɗaya daga
cikin farkon masu karɓar Musulunci
·
Jarumi, masani, kuma mai tsananin ƙauna ga Manzon Allah ﷺ
Annabi ﷺ ya ce game
da shi:
“Aliyu yana tare da gaskiya, gaskiya kuma tana tare da
Aliyu.”
Yadda
Aka Yi Auren Fatima da Ali (RA)
Neman
Auren
Sayyidina
Aliyu (RA) ya nemi auren Nana Fāṭima
(RA), amma saboda kunya da talaucinsa bai da kayan duniya. Da ya zo wajen
Annabi ﷺ, sai
Annabi ﷺ ya
tambaye shi:
“Me
kake da shi na sadaki?”
Aliyu
ya ce ba shi da komai sai garkuwarsa. Annabi ﷺ ya
ce ya ba da ita a matsayin sadaki, ya aurar masa da Fāṭima.
Sauƙin Aure
Babu almubazzaranci
Babu girman kai
Aure
ne bisa tsoron Allah da albarka
Annabi
ﷺ ya
yi musu addu’a, ya ce:
“Ya Allah, ka albarkaci aurensu, ka albarkaci
zuriyarsu.”
4.
Rayuwar Aurensu
Rayuwar Fāṭima
da Ali (RA):
·
Ta kasance mai sauƙi da haquri
·
Sun yi rayuwa bisa ibada, aiki da juna
·
Sun sha wahala amma ba su koka ba
Nana Fāṭima
tana niƙa hatsi da hannu har hannuwanta suka
kumbura, Aliyu kuma yana aiki tukuru. Duk da haka, Annabi ﷺ ya koya musu tasbihi maimakon bawa.
5. ‘Ya’yan Fatima da Ali (RA) – Jikokin Annabi ﷺ
(a) Hasan bn Ali (RA) Shi ne Jikan Annabi ﷺ na farko ga Annabi, har Annabi ﷺ ya ce: “Hasan da Husain
shugabannin matasan Aljanna ne.”
(Tirmidhi)
Sayyadina Hassan ya kasance mai haquri da son zaman
lafiya. Ya kasance mai sadaukar da mulki domin zubar da jini ya tsaya
(b)
Husain bn Ali (RA): shi ne jikan Annabi (SAW) na
biyu, shi ma ya zamo Jarumi, mai gaskiya, ya yi shahada a Karbala
Annabi
ﷺ ya
ce: “Husain daga gare ni ne, ni kuma daga gare shi nake.”
(Tirmidhi)
(c)
Zaynab (RA): Zainab ita ma ‘ya ce ga Fāṭima da Ali, ta kasance
itama Jaruma mai yawan haquri.
(d) Ummu Kulthum (RA): Ita ma ‘ya ce ga Fāṭima da Ali, ta
shahara da tsoron Allah da ladabi
Darussa daga Auren
Fatima da Ali (RA)
1.
Sauƙaƙa aure shi ne albarka
2.
Darajar tsoron Allah fiye da dukiya
3.
Gina gida bisa imani da haquri
4.
Darajar zuriyar Annabi ﷺ da girmamawarsu
Auren
Nana Fāṭima da Sayyidina Ali (رضي الله عنهما)
misali ne na aure na Musulunci mai tsarki da albarka. ‘Ya’yansu – Hasan,
Husain, Zaynab da Ummu Kulthum – sun zama haske a tarihin Musulunci,
kuma su ne jikokin Manzon Allah ﷺ da Musulmi ke
girmamawa da ƙauna.
Allah
Ya yarda da su baki ɗaya, Ya haɗa mu
da Annabi ﷺ da iyalansa a Aljanna.
BABI NA SHA BIYU
AMMOMIN MANZON ALLAH ﷺ
Ammomi Maza:
Malamai sun ruwaito cewa Abdul-Muṭṭalib yana da ’ya’ya maza da dama,
daga cikinsu shahararru su ne:
1. Al-Ḥārith – Shi ne babba daga cikinsu
2. Abu Ṭālib – Shi ne wanda ya raini
Annabi ﷺ
3. Abdullahi – Shi ne mahaifin Annabi ﷺ
4. Ḥamza bn Abdul-Muṭṭalib – Sayyidus-Shuhadā’,
shahidi a Uhud
5. Al-‘Abbās – Daga zuriyarsa ne aka samu Banu
Abbas
6. Abu Lahab – Ya zamo makiyi Annabi ﷺ (ya mutu a kan kafirci)
Ammomi Mata:
Daga cikin ’yan Abdul-Muṭṭalib mata, shahararru sun haɗa da:
1. Ṣafiyya bint Abdul-Muṭṭalib (RA) – Ta zamo Musulma, kuma itace
mahaifiya ga Zubair bn Awwam (RA)
2. Ātikah bint Abdul-Muṭṭalib
3. Arwā bint Abdul-Muṭṭalib
4. Ummayma bint Abdul-Muṭṭalib
5. Barrah bint Abdul-Muṭṭalib
Wasu daga cikinsu sun musulunta, wasu kuma sun rasu kafin Musulunci ya
bayyana sosai.
Ammominsa
sun taka rawa daban-daban a rayuwarsa, wasu suka kare shi (kamar Abu Talib
da Hamza), wasu kuma sun yi gaba da shi (kamar Abu Lahab)
Wannan ya nuna cewa gaskiya ba ta la’akari da zumunci, sai bin
umarnin Allah.
BABI NA SHA UKU
MASU HIDIMA GA MANZON ALLAH ﷺ
Manzon Allah Muhammad ﷺ
ya kasance yana da manyan Sahabbai masu hidima a fannoni daban‑daban:
masu tsaro, masu kiran salla, mawaƙa, da masu hidimar gida. Waxannan
Sahabbai sun taka muhimmiyar rawa wajen kare shi, isar da saƙonsa, da tallafa masa a rayuwa
da jihadi.
Ga wasu daga cikin su:
1. Anas ɗan Mālik (RA) – Ya kasance mai hidimar ga
Annabi (SAW)
Asalinsa da zamansa mai hidima
Anas bn Mālik Al‑Ansari daga Banu Najjar ne. Mahaifiyarsa Ummu Sulaym (RA) ce ta kai shi wajen Annabi ﷺ yana ƙarami, tana cewa:
“Ya Rasulallah, ga ɗana
Anas, ka ɗauke shi ya yi maka hidima.”
Annabi ﷺ ya karɓe shi, Anas ya yi hidima
tsawon shekaru goma a Madina.
Halayensa a hidima
·
Ya kasance mai biyayya, ladabi da gaskiya.
·
Annabi ﷺ bai taba tsawata masa ba, bai
ce masa “me ya sa ka yi haka?” ko “me ya sa ba ka yi ba?”.
·
Ya shaida cikakken halin Annabi ﷺ a gida da wajen gida.
Darajarsa
·
Ya ruwaito dubban hadisai.
·
Ya rayu tsawon lokaci, ya yada ilimi a Basra.
·
Annabi ﷺ ya yi masa addu’ar yawaitar
arziki da zuriya.
Mawaƙan Manzon Allah ﷺ (Masu kare Musulunci da
harshe)
1- Hassan ɗan Thābit (RA) Hassan shi ne babban mawaƙin Annabi ﷺ. Ya yi amfani da waƙa wajen kare Annabi ﷺ da Musulunci daga zagin mushrikai.
Annabi
ﷺ ya ce masa:
“Ka yi musu martani, Ruhu’l‑Qudus (Jibril) yana tare da kai.”
2-Abdullahi ɗan
Rawāḥa (RA) Shi ma Sahabi ne, kuma mawaƙi gashi kuma jarumi a fagen
jihadi. Waƙoƙinsa suna ƙarfafa Musulmi a filin yaƙi, ya yi shahada a Yaƙin Mu’uta.
3-Ka‘abu ɗan
Mālik (RA) shi ma ya zamo mawaƙi mai yawan hikima, ya shahara da labarin tuba bayan Yaƙin Tabuk. Waƙoqinsa suna tattare da
gaskiya, nasiha da tsoron Allah.
4-Ka‘ab bn Zuhayr (RA) – shi ma mawaqi ne shi ne marubucin
“Banat Su‘ad”, shi ne wanda Annabi ﷺ ya lullube shi da bargonsa.
3. Masu kiran Sallar Annabi ﷺ (Mu’azzinai)
(a) Bilāl Al‑Habashi (RA): Bilal ya zamo shi ne mai kiran Sallah (mu’azzini)
na farko a Musulunci. Annabi ﷺ ya zaɓe shi saboda kyakkyawar
murya da tsarkin imani. Bilal ya sha wahala a wajen mushurikan Makkah
saboda Musulunci. Har Annabi ﷺ
ya ce ya ji takunsa a Aljanna.
(b) Abdullahi ɗan
Ummu Maktūm (RA): shi ma Sahabi ne kuma makaho, ya
kasance mai kiran Sallah (mu’azzini) tare da Bilal. Annabi ﷺ yana barinsa a matsayin wakili
a Madina idan ya fita jihadi.
An
saukar da aya game da shi a Suratul ‘Abasa.
(c) Abu Mahdhura (RA): shi ma ya zamo maikiran
Sallah a garin Makkah bayan fatahu Makkata. Annabi ﷺ ya koyar da shi lafazin kiran
salla kai tsaye.
4. Sauran Muhimman Masu Hidima ga Annabi ﷺ
(a) Abu Ayyub Al‑Ansari (RA): Shi ne wanda Annabi ﷺ ya sauka a gidansa bayan hijira.
(b) Zayd ɗan
Hāritha (RA): Shi ya zamo Bawan Annabi ﷺ da ya ‘yanta shi. Ya kasance kamar
ɗa a gare shi (SAW).
(c) Usāma ɗan Zayd (RA): Shi Ɗa ne ga Zayd bn Haritha. Annabi
ﷺ ya naɗa shi shugaban runduna tin
yana saurayi.
(d) Asmā’u bint Abi Bakr (RAا): Ita ma ta yi hidima ga Annabi (SAW) a lokacin hijira,
ana kiranta “Dhatun‑Nitaqayn”.
Masu hidimar Manzon Allah ﷺ sun kasance ginshiƙai wajen nasarar da’awar
Musulunci. Kowa ya bayar da gudummawa bisa baiwar da Allah Ya ba shi: hidima,
waƙa,
kira zuwa salla, tsaro, ko ilimi. Tarihinsu darasi ne na biyayya, sadaukarwa
da ƙauna ga Annabi ﷺ.
BABI NA SHA HUXU
SIFFOFI DA HALAYEN MANZON ALLAH ﷺ
Siffofin Annabi Muhammad ﷺ suna daga cikin manyan hujjojin annabtcinsa. Allah Ya haɗa masa kyawawan siffofi na
halayya (akhlaƙ) da kamala ta ɗabi’a, har ya zama abin koyi ga
dukkan halittu.
Kyawawan dabi’u na Manzon Allah Muhammad ﷺ su ne tushen shiriya da tarbiyya ga al’umma. Allah Ya haɗa masa kamala ta ɗabi’a, tausayi, adalci da
hikima, har ya zama abin koyi mafi kyau ga duk wanda yake neman kusanci
da Allah.
Wannan babi zai tattauna siffofinsa tare da Kyawawan dabi’unsa tare da hujjoji
daga Al-Kur’ani da Hadisai sahihai.
1)
Gaskiya (Aṣ-Ṣidq)
Annabi ﷺ ya shahara da gaskiya tun
kafin a ba shi wahayi, har mushrikai suke kiransa Al-Amīn (Amintacce).
Allah ta’ala yana cewa:
“Wanda ya zo da gaskiya, kuma
aka gaskata shi, su ne masu taƙawa.”
(Suratu
Az-Zumar: 33)
Malamai suka ce: wanda ya zo da gaskiyar nan shi ne Annabi Muhammad ﷺ.
Yazo a Hadisi Abu Sufyan ya shaida wa Heraclius cewa:
“Ba mu taɓa gwada shi da ƙarya ba.”
(Sahih
Bukhari)
2)
Amana (Al-Amāna)
Annabi
ﷺ ya kasance abin dogaro wajen
ajiya da al’amuran jama’a, har ma abokan gābansa suna ajiye masa dukiyarsu.
Allah Ta’ala yana cewa:
“Lallai Allah yana umartar ku
da ku mayar da amana ga ma’abotanta.”
(Suratu
An-Nisa’i: 58)
Annabi ﷺ ya fi kowa cika wannan
umarni.
3)
Cikar Kyawawan Dabi’u
(Husnul-Khuluq):
Dukkan halayensa Alaihissalam cikin maganganunsa, aikisa, mu’amalarsa
duk sun kasance bisa daidaito da adalci.
Allah ta’ala yana cewa:
“Kuma lallai kai kana kan
kyakkyawan ɗabi’a mai girma.”
(Suratu Al-Qalam:
4)
Yazo a Hadisi: Annabi ﷺ ya ce:
“An aiko ni ne domin cika
kyawawan ɗabi’u.”
(Muwatta’
Malik)
4) Tausayi da Rahama:
Manzon
Allah (SAW) ya zamo mai tausaya wa yara, da mata, da talakawa, har ma da
dabbobi.
Allah ta’ala yana cewa:
“Ba Mu aiko ka ba face rahama
ga talikai.”
(Suratu
Al-Anbiya’: 107)
Yazo a Hadisi: Annabi ﷺ ya ce:
“Masu rahama, Mai Rahama zai
yi musu rahama.”
(Tirmidhi)
5) Haƙuri da Juriya:
Annabi ﷺ ya fuskanci tsangwama, duka
da ƙauracewa,
amma bai rama da zalunci ba.
Allah ta’ala yana cewa:
“Ka yi haƙuri, haƙurinka kuwa ba zai kasance ba
sai da taimakon Allah.”
(Suratu
An-Nahl: 127)
“Ka yi haƙuri, lallai Allah yana tare da
masu haƙuri.”
(Suratu
Al-Baqara: 153)
Yazo a Hadisi: Yayin da aka jikkata shi Alaihissalam a yaqin Uhudu,
sai manzon Alah (SAW) ya ce:
“Ya Allah! Ka gafarta wa
mutanena, domin ba su sani ba.”
(Bukhari)
6) Tawali’u (Ƙanƙantar kai):
Duk da matsayinsa na Annabi da shugaban al’umma, Annabi ﷺ ya kasance mai sauƙi da tawali’u,
yana zama da talakawa, yana gyara kayansa da hannunsa.
Yazo a Hadisi: Annabi ﷺ ya ce:
“Ni bawa ne, ina ci kamar
yadda bawa yake ci, ina zama kamar yadda bawa yake zama.”
(Ahmad)
7) Adalci da Gaskiya a Hukunci:
Ma’aiki Alaihissalam ya zamo mai adalci da gaskiya a dukkan hukunce
hukuncen sa.
Allah Ta’ala yana cewa:
“Lallai Allah yana umartar da
adalci.”
(Suratu
An-Nahl: 90)
Yazo a Hadisi: Annabi ﷺ ya ce:
“Da Fatima ‘yata ta yi sata,
da zan yanke hannunta.”
(Bukhari da
Muslim)
8) Afuwa da Yafe Laifi:
Ma’aiki Alaihissalam ya zamo mai yawan afuwa da yafiya a dukkan laifukan
da aka yi masa, har a ranar Fatahun Makkah, duk da abin da kafirai suka
yiwa Musulunci da Musulmai, amma da aka cisu da yaqi saya ce: “Ku tafi, ku ‘yantu.”
Allah Ta’ala yana cewa:
“Ka yi afuwa, ka umarci
alheri.”
(Suratu
Al-A’raf: 199)
9)
Kunya da Tsarkin Zuciya:
Manzon Allah (SAW) ya kasance mai yawan kunya da tsarkin zuciya.
Yazo a Hadisi: An ce: “Annabi
ﷺ ya fi budurwa kunya a cikin ɗakinta.”
(Bukhari da
Muslim)
10)
Ƙauna ga Al’umma
Allah Ta’ala yana cewa:
“Lallai Manzo ya zo muku daga
cikinku; yana jin nauyin abin da ya same ku, yana matuƙar son alherinku.”
(Suratu
At-Tawba: 128)
11)
Tausayi da Rahama
Rahamar Annabi ﷺ
ta shafi Musulmi da waɗanda
ba Musulmi ba.
Allah Ta’ala ya faxa a cikin Al-Kur’ani
“Ba Mu aiko ka ba face rahama
ga talikai.”
(Suratu
Al-Anbiya’: 107)
Yazo a Hadisi Annabi ﷺ ya ce:
“Masu rahama, Mai Rahama zai
yi musu rahama.”
(Tirmidhi)
Kyawawan dabi’u da kyawun halayen Manzon Allah ﷺ su ne haske ga rayuwar
Musulmi. Yin koyi da shi hanya ce ta samun yardar Allah da zaman lafiya a
duniya.
“Lallai haƙiƙa Manzon Allah abin koyi ne
mafi kyau a gare ku.”
(Suratu Al-Ahzab: 21)
WAFATIN MANZON ALLAH ﷺ
Wafatin Manzon Allah Muhammad ﷺ shi ne lamari mafi girman abin da ya taɓa
girgiza zukatan Sahabbai da al’ummar Musulmi gaba ɗaya. Duk da kasancewarsa mafi
soyuwa ga Allah, rayuwar duniya ba
madawwama ba ce, domin Allah Ya ƙaddara mutuwa ga kowane rai.
“Kuma lallai kai ma za ka mutu, kuma lallai su ma za su mutu.”
(Suratu Az-Zumar: 30)
Rashin lafiyar Annabi ﷺ ya fara ne kwanaki kaɗan bayan dawowarsa daga Baqi’a‘. Ya fara jin: - Zazzabi mai tsanani da Ciwon kai da
Rauni a jiki
Yana cewa: “Ina jin zafin gubar da na sha a Khaybar har
yanzu.”
(Sahih Bukhari)
Wannan na nuna cewa wafatinsa
ya kasance cikin jarabawa da ladan
shahada.
2. Kwanaki na Ƙarshe a Rayuwarsa ﷺ
(a)
Jagorantar Sallah: Duk da tsananin
ciwon da yake fama da shi, Annabi ﷺ
yana daurewa ya fita zuwa masallaci don jagorantar Sallah. Sai da ciwon ya
tsananta sosai, sai ya ce: “Ku umurci Abubakr ya jagoranci mutane a
sallah.”
(Bukhari da Muslim)
Wannan alama ce ta darajar Abubakr (RA).
(b) Ziyarar Xakunan Matansa: Annabi ﷺ ya nemi izinin matansa a bar shi ya zauna a ɗakin
Nana A’isha (RA) domin samun sauƙin jinya. A nan ne ya shafe kwanaki
na ƙarshe.
3. Shawarwarin Ƙarshe na Annabi ﷺ
Daga cikin maganganunsa na ƙarshe akwai: - “Ku
kiyaye sallah, ku kiyaye sallah.”
- “Ku ji tsoron Allah game da mata.” - “Ku kula da bayinku.”
Wannan na nuna muhimmancin ibada, adalci da tausayi a Musulunci.
Annabi ﷺ yayi wafati a Ranar Litinin ta cikin
Watan Rabi‘ul Awwal Shekararsa: 63.
Annabi
ﷺ ya jingina kansa a kan kirjin Nana A’isha (RA). A hannunsa akwai aswaki,
ta taimaka masa ya yi amfani da shi.
Ya kan yi addu’a, sai ransa mai tsarki ya fita cikin nutsuwa.
5. Girgizar da Ta Kama Sahabbai
Da labarin wafatinsa ﷺ ya bazu: - Umar bn Khattab
(RA) ya ƙi yarda, yana cewa bai rasu ba. Abubakr (RA) ya
shigo, ya tabbatar da wafatinsa, ya sumbaci goshinsa.
Sai Abubakr (RA) ya yi jawabi
mai ratsa jiki yace: “Duk wanda yake bauta wa Muhammad, to Muhammad ya rasu;
duk wanda yake bauta wa Allah, to Allah Rayayye ne, ba Ya mutuwa.”
Sannan ya karanta fadin Allah
ta’ala: “Muhammad ba wani abu ba ne face Manzo; manzanni sun shude a
gabansa.”
(Suratu Al-Imran: 144)
6. Wankan, Jana’iza da Binnewa
An yiwa Ma’aiki Alaihissalam wanka da tufafinsa a jikinsa, Sahabbai
suka yi sallah a kansa rukuni-rukuni, ba tare da limami ba, aka binne
shi a ɗakin Nana A’isha (RA), inda ya rasu.
Wafatin Shugaba Alaihissalam
na nuna cea mutuwa gaskiya ce ga kowa kuma shu Annabi ﷺ bawa ne na Allah, ba wai abin
bautawa ba ne. Sannan an tabbatar da Addinin Musulunci ya cika kafin wafatinsa,
sai dai yin ruqo da Al-Kur’ani da Hadisai (Sunnah), kamar yadda yake cewa:
“Na bar muku abubuwa biyu; ba
za ku ɓata ba matuƙar kun riƙe su: Littafin Allah da Sunnata.”
Wafatin Manzon Allah ﷺ babban rashi ne, amma saƙonsa ya wanzu har abada. Soyayyarsa ta gaskiya ita ce bin Sunnarsa da kiyaye umarnin
Allah.
Allah Ya ƙara tsira da amincinsa ga
Annabin rahama, da iyalansa, da Sahabbansa baki ɗaya.
KAMMALAWA
Wannan Littafin ya yi cikakken bayani kan rayuwa da koyarwar Manzon Allah Muhammad ﷺ, daga haihuwarsa, zamanin Annabci, hijira, rayuwarsa a Madina, zuwa wafatinsa.
Hakanan ya bayyana siffofi, kyawawan
dabi’u, masu hidimarsa, da abubuwan da suka faru a lokacin rayuwarsa.
Abubuwan da muka tattauna sun haɗa da: ’Ya’yansa da
ammominsa, da yadda ya yi hulɗa da su. Yakokin da yayi
Sahabbai masu hidima, kamar Anas bn Mālik, Bilal Al-Habashi, Hassan
bn Thabit,
da sauran mawaƙa da mu’azzinai.
Kyawawan
dabi’u da siffofi da suka sa ya zama abin koyi ga Musulmi.
Shigarsa
Madina da tarbar Ansar, da kuma kafa ƙa’idojin al’umma da addini.
Wafati
da janarwarsa,
da darussan da Musulmi za su koya daga rayuwarsa.
Wannan
littafi ya nuna cewa Manzon Allah ﷺ ya zo ne domin cika kyawawan ɗabi’u, isar da gaskiya, da
shiryar da al’umma. Duk wanda ya karanta wannan littafi da zuciya ɗaya, zai fahimci cewa bin
koyarwar Annabi ﷺ
shi ne ginshiƙin nasara a duniya da lahira.
A
ƙarshe,
wannan littafi yana ƙarfafa Musulmi da matasa musamman su riƙa koyi da Manzon Allah ﷺ, su kiyaye addini, su girmama
Sahabbai, su yi kyawawan ayyuka, kuma su yi tunani akan mutuwa da rayuwa ta
lahira.
“Lallai haƙiƙa Manzon Allah ﷺ abin koyi ne mafi kyau ga ku.” (Suratul Ahzab: 21)
Comrade Auwal Zakari Ayagi
(Barden Ayagi)
14/12/2025
24/Jumada
Thani 1447
No comments:
Post a Comment