Takaitaccen Tarihin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wa Sallam)
Nasabarsa: Shine Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul-Muɗɗalibi ɗan Hashimi ɗan Abdul-Munafi ɗan Kusayyi ɗan Kilabi, Sallallahu alaihi wa aalihi wa
sallam, nasabarsa maɗaukakiya tana tukewa zuwa ga Annabi Ibrahim, alaihis salatu wassalam. Manzon Allah ne cikamakin Annabawa shuganan Manzanni.
Mahaifiyarsa: Ita ce Aminatu (Āminah) 'yar Wahbi ɗan Abdul Munaf ɗan Zuhrata ɗan Kilabi (Radhiyallahu anha).
Alkunyarsa: Ana masa alkunya da Abul'Qasim, ko Abu Ibrahim.
Sunayensa: Al-Musɗafa yana da sunaye da yawa da suka zo a cikin Ƙur'ani Mai Girma, kamar: Khataman-Nabiyyin, da Al-Ummiy da Al-Muzzammil da Al-Muddassir da An-Nazir da Al-Mubin da Al-Karim da An-Noor da An-Ni'ima da Ar-Rahma da Al-Abdu da Ar-Ra'uf da Ar-Rahim da Ash-Shahid da Al-Mubasshir da An-Nazir da Ad-da'i da sauransu.
Tarihin haihuwarsa: Anhaife shi Salallahu Alaihi wasallam Ranar Litinin 12 ga watan Rabi'ul Auwal Shekarar Giwa, bisa mash'hurin zance.
Wurin haihuwarsa: An haifeshi Salallahu Alaihi wasallam a Garin Makkah.
Aikoshi: An aiko shi a Makkah yana da shekaru arba'in.
Koyarwarsa: Ya zo da daidaito tsakanin dukkan halitta da 'yan-uwantaka da rangwame na gaba ɗaya ga wanda ya shiga musulunci, sa'annan ya kafa shari'a maɗaukakiya da dokoki na adalci da ya karɓo daga wajan Allah, su kuma musulmi suka karɓa daga gare shi (SAW).
Mu'ujizozinsa: Mu'ujizarsa madauwamiya ita ce Alkur'ani amma waɗanda suka faru a farkon Musulunci suna da yawa ba su kirguwa ba.
Kiransa: Ya kira mutane zuwa ga Tauhidi a Makkah a ɓoye shekara uku ya kuma kira su a bayyane shekara goma.
Hijirarsa: ya yi hijira daga Makkah zuwa Madinah a farkon watan Rabi'ul Auwal bayan shekaru 13 daga aikensa, wannan ya faru ne sakamakon cutarwa daga kafirai gare shi da sahabbansa.
Yakokinsa: Allah ya yi wa Manzo izinin yakar mushirikai da kafirai da munafukai, ya yi ɗauki ba daɗi da su a wurare da yawa, mafi girmansu sune: Badar, Uhud, Al-Khandak (Ahzab), Khaibar, Hunaini da sauransu.
Matansa: Matansa 12 ne, cikin su akwai, Khadijah 'yar Khuwailid ita ce matarsa ta farko, sauran su ne: Saudatu 'yar Zam'a da A'isha 'yar Abubakar da Hafsa yar Umar da Ramla 'yar Abu Sufyan (Ummu Habiba) da Ummu Salama 'yar Abu Umayya da Zainab 'yar Jahash da Zainab 'yar Huzaima da Maimunah 'yar Al-Haris da Juwairiyya 'yar Al-Haris da Safiyya 'yar Huyayyi ɗan Akhdabl (R.A).
'Ya'yansa: Yayansa 7 ne, Akwai Abdullah, sai Al-Kasim da Ibrahim da Faɗima da Zainab da Rukayya da kuma Ummu Kulthum.
Ammominsa: Ammonin sa su Tara ne, su 'ya'yan Abdul-Muɗɗalib ne: Al-Haris da Zubair da Abu Ɗalib da Hamza da Al-
Ghaidaq da Dirar Al-Muqawwam da Abu Lahab da Abbas.
Ammominsa mata: Su shida ne daga iyaye mata daban-daban su ne: Aminah da Ummu Hakima da Barra da Atika da Safiyya da Arwa.
Mai tsaron ƙofarsa: Anas ɗan Malik.
Mawakansa: Hassanu ɗan Sabit, da Abdullahi ɗan Rawahata, da Ka'abu ɗan Malik.
Masu kiran sallarsa: Bilal Al-Habashi da Abdullahi ɗan Ummu Maktum da Sa'ad Al-Kirdi.
Tambarin Zobensa: Muhammadur Rasulullah!
Tsawon rayuwarsa: shekaru 63.
Tsawon lokacin Annabtarsa: shekaru 23.
Tarihin wafatinsa: Yayi wafati Ranar Litinin 12 ga watan Rabiyyul Awwal a Madinah, an binne shi a Masallaci Maɗaukaki Mai Alfarma.
Allah kakara tsira da Aminci ga Shugabanmu Sallallahu Alaihi wasallam
12 ga Rabi'ul Auwal 1444
8th October 2022
No comments:
Post a Comment