Wednesday, 1 October 2014

Bayani kan Amosanin Ka

BAYANI AKAN AMOSANIN KA

Da farko dai ya kamata da kai da sauran masu karatu su fahimta cewa amosanin kai ba ciwo ba ne, wato ba cuta ba ce wadda wata kwayar cuta ke iya sa wa. Kamar matsalar saba ta sauran fatar jiki da wasu suke ganin kamar ciwo ne, amosani shi ma saba ce da kan faru a fatar kai wadda take karkashin suma. To idan tana barbashewa za a ga fari-fari na zuba kamar gari, musamman idan an zo taje kai ko kitso ko an zo yi wa mutum aski.

Bari mu fara dora bayanin a kan ita kanta fatar jiki tukuna, sa’annan ka gane cewa ba matsalar da za ka damu da ita ba ce sosai. Dama fatarmu canzawa take daga lokaci zuwa lokaci, kusan a ce wata-wata, dangane da irin abinci da muke ci da yanayin gari wato, zafi ko hunturu ko rani ko damin, da irin abin da muke shafa mata da kuma
yawan shekaru, wato tsufa ko kuruciya. Duka fatar kowa tana son abinci mai lafiya isasshe, mai dauke da sinadarin abinci mai gina jiki wato protein, wanda daga shi ne fatar kan sarrafa sinadaran keratin da collagen da elastin, wadanda su ne ginshikan ita kanta fatar. Sai kayan marmari masu dauke da bitaman masu sa fata sheki da
walwala. Akan iya samun wasu sinadaran a man da muke shafawa, wanda shi ma fata kan tsotse su idan an shafa. Don haka za ka ga fatar wadanda suka faye samun wadannan irin abinci da mai daban da ta wadanda ba su cika samun hakan ba kuma a iya cewa fatarsu ta fi lafiya kuma ta fi rashin nuna matsaloli.

Dangane da yanayi kuma wasu fatarsu ta fi son zafi, wasu kuma ta fi son yanayin danshi, a wasu kuma ta fi son yanayin sanyi. Babu fatar da ke son busasshen yanayi irin na hunturu. Misali, shi ya sa kusan kowa yakan samu matsalar fata a wannan lokaci, tun daga kaushi zuwa faso zuwa saba zuwa tsagewar lebe, zuwa waskane, har zuwa
amosanin ka.

To amma duk da cewa amosani ba ciwo ba ne, yana daya daga cikin abin da kan sa mutane da yawa damuwa musamman ma mata, don haka dole a saurari mai korafin wannan matsala.

Matsalar kan shafi kusan rabin mutanen duniya, ba bambanci a tsakanin jinsinan duniya. Wasu lokuta yakan sa kaikayi, mutum ya yi ta sosa kai, wanda wannan ma idan a cikin mutane ne sai
kunya ta fara kama shi. Idan ana sosawa kuma barbashin kan biyo kai a gan shi a saman suma ko a kafada.

A gaskiya babu abin da zai warkar da amosanin ka, tun da ba ciwo ba ne, sai dai abin da zai rage shi. Kamar yadda muka fada a baya, yanayin abinci da na wuri suna taimakawa, haka ma man wanke kai wadanda ga su nan birjik a kasuwanni da manyan shaguna ba sai a kyamis ba. Da mutum ya je ya ce a ba shi maganin shamfo na amosani za a ba shi mai kyau. Mutane da dama sun fi ganin amfanin wani wai shi head and shoulders fiye da sauran. A mafi yawan lokuta da an fara amfani da shi za a fara ganin saukin barbashewar suma da kuma kaikayi. Ba wai hana fatar marmashewa yake ba, a’a yakan ba fata laushin da ba za a san lokacin da ta canza ba, tunda dole ne duk bayan ’yan makonni sai ta sama ta marmashe ta karkashi ta tofo. Ka ga ke nan babu tabbas din idan ka daina amfani da shi
ba zai dawo ba.

Babu kanshin gaskiya game da cewa idan kurar kai ta mai amosani ta sauko ta shiga ido tana illa ga lafiyar idon.

BAYANI GAME DA CUTAR HAWAN JINI

Bayani akan CUTAR HAWAN JINI

Cutar Hawan jini ta yawaita matuka a cikin mutane harda al’umarmu ta jinsin bakaken fata, kuma tana jawo mana illoli masu yawa. Babban abin damuwa da bakin ciki shine, da yawa daga cikin al’umarmu basu da cikakken bayani game da wannan cuta; wasu kuma sun sani amma basa bada himma wajen neman magani.

MENENE CUTAR HAWAN JINI?
Ana cewa mutum ya kamu da wannan cuta ne idan an auna shi da na’urar awon karfin bugun jini (wato spygmomanometer) wadda ta nuna awon jininsa ya kai, ko ya wuce, dari da arba’in bisa casa’in (wato > 140/90mmHg) kuma awon ya dauwama a haka. Sai dai wannan adadi da aka ambata yana sabawa saboda bambancin shekaru, jinsi (wato namiji ko mace), halin da mutum yake ciki, da sauransu. A takaice dai, sai
an je asibiti za’a iya tabbatarma mutum ko yana da cutar ko baya da ita.

MENENE YAKE KAWO CUTAR?
Ta la’akari da yadda wanna cuta ke faruwa ga mutane, an raba wannan cuta zuwa gida biyu.

Kashi na farko - Sama da kashi casa’in (>90%) na mutane dake fama da wannan cuta, har yanzu ba’a san takamaiman dalilin da za’ace shi ya kawo masu wannan cuta ba sai dai akwai wasu abubuwa ko al’amura da aka alakanta ga faruwar wannan cuta ga wadannan mutane na kashin farko.
Wadannan abubuwan sun hada da:
· Yanayin kwayoyin halittar dan-adam, ma’ana ana iya gadon wannan cuta.
· Jinsin dan-adam (anfi samu a bakaken fata)
· Yawaita shan gishiri fiye da kima.
· Yawaita shan barasa (giya).
· Kibar jiki mai tsananin yawa.
· Rashin motsa jiki, da dai sauransu.

Kashi na biyu - A wannan bangare, an gano wasu cututtuka na musamman da suke kawo wannan cuta. Cututtukan sun hada da:
· Cututtukan dake shafar kodar mutum.
· Cututtukan dake shafar kwakwalwa.
· Wasu daga cikin magunguna na bature.
· Wasu cututtuka dake shafar jijiyoyin jini, da dai sauransu.

TA YAYA AKE GANE ALAMOMIN WANNAN CUTA?
Wasu daga cikin mutanen da suka kamu da wannan cuta basu da wasu alamomi da suke ji, wasu kuma sukan ji kamar yawan ciwon kai, fargabar zuciya, raguwar gani ko gani dishi-dishi. Wasu kuma suna zuwa asibiti ne da alamomi na illolin da cutar ta haifar musu (za’a yi bayani nan gaba). Wasu kuwa sai sunje asibiti dalilin wata cutar, wurin bincike sai a gano cewa suna da cutar hawan jini.
Karin bayani a nan shine, ba wai ance da mutum yaji yana fama da daya ko wasu daga cikin alamomin can na sama kawai sai yace ya kamu da cutar ba. Wannan kuskure ne. Mutum ya bari sai yaje an auna shi domin a tabbatar masa ko yana da cutar ko bashi da ita, domin tabbatacciyar hanyar sanin mutum ya kamu da cutar hawan jini ita ce ta auna jinin da na’urar asibiti.

ILLOLIN CUTAR HAWAN JINI.
Wannan matsaloli zasu iya faruwa ga wanda bai dade da kamuwa da cutar hawan jini ba ko kuma ga wanda ya dade da ita. Sun kunshi:
· Ciwon koda wanda zai iya jawowa ta daina aiki.
· Raguwar gani ko makancewar ido.
· Ciwon shanyewar wani bangare na jiki kamar rabin jiki (wato Paralysis).
· Ciwon zuciya, da dai sauransu.

Sai dai abinda ya kamata a fahimta game da wadannan matsaloli shine, ba cutar hawan jini kawai ke kawo suba. Za’a iya samun su ta wasu cututtuka kamar ciwon suga (wato Diabetes Mellitus) da sauransu. Wadannan illoli sun fi faruwa ga mutanen da suke da wannan cutar kuma basa shan magani ko kuma basa sha kamar yadda likita ya umarta.

MAGANIN CUTAR HAWAN JINI.
Akwai magunguna kala-kala da ake bayarwa ga masu wannan cuta. Suna yin amfani ne wajen tabbatar da daidaitar awon jini na mutum ta yadda ba zai yi yawa har ya kai ga samar da wadancan illoli da muka ambata ba. Wadannan magunguna za’a same su idan anje asibiti wajen likita.
Haka kuma kula da wadannan abubuwa da zamu zana wadanda ke da alaka da wannan cuta suna taimakawa matuka wajen kiyaye kai daga samun wannan cuta ko rage matsalolinta ga wadanda suke da cutar. Abubuwan sune:
· Barin shan barasa.
· Rage yawaita shan gishiri a abinci.
· Motsa jiki akai-akai.
· Rage kiba mai tsanani, ta hanyar rage yawaita cin abinci fiye da kima, rage cin man kitse, motsa jiki da sauransu.
· Yawaita cin kayan lambu da ababen marmari kamar su lemo, yalo, karas, alaiyahu, zogale, rama, da danginsu.

KAMMALAWA DA SHAWARWARI.
Tunda mun fahimci wani abu daga wannan cuta, kamar abubuwan da aka alakanta ta da su, matsalolin da take jawowa da sauransu, to ya kamata mu tashi haikan, mu nemi kariya daga gareta kamar yadda Allah (SWT) da ManzonSa suka umurta, ta kiyaye abubuwan da ke iya jawota.
Ba karamin kuskure neba ga mai wannan cuta ya ki shan magani, wato yace ya warke, domin ba shi jin alamomin ta. A yanzu babu wani magani da ke warkar da ita gaba daya har abada, sai dai a sami saukin da zai bada dammar rayuwa kamar yadda mai Lafiya yake yi. Tabbas, mun yi imani da bayanin Annabi Muhammadu (SAW) inda yake cewa “kowace cuta tana da magani”, amma muna fata Allah cikin rahamarSa zai fahimtar da likitoci maganin da zai warkar da ita nan gaba. Saboda haka sai a dauki wannan cuta a matsayin kaddara daga Allah, a kuma nemi lada daga wajenSa, a cigaba da shan magani domin a samu
rayuwa cikin kwanciyar hankali kamar kowa.
Kada mutum ya tsaya a zuwa kemis kawai ya ki zuwa asibiti. Illar wannan shine, za’a iya bada maganin da bai dace da mutum ba, ko kuma wanda zai iya kawo masa babbar matsala ga jiki.
A kuma lura, kada a tsaya a yi ta shan magunguna na gargajiya, a ki zuwa asibiti domin wadannan magunguna basu da tabbas, kuma za su iya taimakawa wajen kawo matsaloli da zasu shafi koda, hanta da sauran sassa na jiki.
A karshe ina tunatar damu game da fadin Allah Madaukakin Sarki a cikin surar bakara “…kada ku jefa kawunanku cikin halaka…”, wato mutum kiri- kiri ya zauna ya bari ciwo yayi masa illa ya ki shan magani, karshe a zo ayi ta wahala da jidali akan zuwa asibiti, sabanin inda mutum ya tashi tunda farko ya nemi magani. Muna yin addu’a duk wadanda basu da Lafiya, Allah Ya basu sauki. Masu Lafiya, Allah Ya kara kiyaye su, Amin summa Amin.

Friday, 29 August 2014

Cutar Sankarar Mama

Memene sankaran mama?

Sankaran mama na afkuwa ne a yayin da kwayoyin halittar jikin mama suka fara girma a kan kansu ba tare da jiki ya umarce su ko ya bukace su da su yi haka ba.

Me yake jawo sankaran mama?
Mutane da dama sukan so su san abinda yake jawo wannan cuta ta sankaran mama.  Har ma sukan tambayi kansu, me yasa na gamu da wannan cuta?  Ko me ya sa matata ko kanwata ko ya ta ko kawata ta gamu da wannan cuta?  Ko akwai wani abu da na yi ko suka yi, da ya kamata su yi, ko na yi, da banyi ba, ko basu yi ba domin kare kai na ko kansu daga wannan cuta?.

Babu wani sanannen dalili da za a iya kawowa kai tsaye wanda za a ce shi yake kawo wannan cuta.  Sai dai akwai wasu dalilai da sukan sanya wannan cuta ta fi saurin kama wasu matan a maimakon wasu.  Waɗannan dalilai su ne:

Shekaru – karfin zaton kamuwar mace da sankaran mama, yana karuwa ne da yawan shekarun mace.

Sinadarin iyistirogin – Yawan Sinadarin iyistirogin da yake jikin mace. Shi wannan sinadari na iyistirogin yana ɗaya daga cikin sinadaran da jikin mace ya kunsa kuma yana da kyau a ce jikin mace yana  da wannan sinadari isashshe. Sai dai kuma bai kamata a ce jiki yana fitar da shi ba tare da hutu ba.

Wannan hutun yana zuwa ne a lokacin da mace take da ciki ko take shayarwa. Don haka  dalilan da suke haifar da kasancewar sinadarin iyistirojin a jiki suna jefa jiki cikin haɗarin kamuwa da cutar sankaran mama.  

Daga ciki akwai fara jinin al’ada da wuri (kafin a kai shekara goma sha biyu), yin al’ada har a wuce shekara hamsin da biyar, rashin haihuwa, da kuma jinkirin haihuwa da wuri har a wuce shekara talatin.  Waɗannan abubuwa ba yin kanmu ba ne, kuma za a iya saisaita yawan wannan sinadari a jiki ta hanyar shan magungunan hana ɗaukar ciki da na sa haihuwa da sauransu.

Girman Jiki da sura- Mace mai tsaho da mace mai kiba ta fi faɗawa hadarin kamuwa da wannan cuta.  Matan da sukayi kiba kuma basu rame ba har bayan sun daina jinin al’ada haɗarin kamuwarsu da sankaran mama yafi yawa. Haka kuma komai shekarun mace, wanda suke da tarin kitse a tumbin su ko kuma a kugun su suma hadarin kamuwarsu da sankaran mama yafi yawa

Tarihin cuta a cikin ‘yan uwa – Macen da a cikin yan uwanta an taɓa samun wata kamar mahaifiyarta, ko yarta, ko ‘yarta ta tana da wannan cuta, ta fi fadawa haɗarin kamuwa da wannan cuta.

Tarihin Kamuwa da cutar Sankaran mama: Macen da cutar  sankara ta taɓa kama ta a mamanta guda ɗaya, cutar za ta iya kama ɗaya maman ma

Wasu cututtukan mama da ba sankara ba: Wasu matan da aka taɓa cire musu tsiro a mamansu wanda likita ya ce musu ba sankara bane.  Dole sai suna zuwa a na duba wannan mama akai-akai domin irin wannan tsiro  zai iya juyawa ya koma cutar sankara daga baya

Akwai tabbacin cewa kamuwa da cutar sankaran mama ba laifin mutum ba ne. Bata da alaka wacce take kai tsaye da abincin da muke ci, kuma ba cuta bace mai kwayoyi da za’a iya kamuwa dasu ba.  Haka kuma ba a daukar ta ta hanyar jima’i, ko ta hanyar hulda da wanda yake da wannan cuta.

Ta ya ya ake gane sankaran mama?

Abu na farko da za a fara lura a tabbatar da cewa jiki ya kamu da cutar sankaran mama shine samuwar wani dan tsiro a cikin nonon maras ciwo.
Shi wannan tsiro za a ji shi kamar kurjin maruru sai dai ba ya  ciwo.  Duk macen da ta ji irin wannan a jikin mamanta sai ta garzaya wajen likitanta nan take. Dole ne a cire duk ilahirin irin wannan tsiron sannan a gwada a asibiti.
Maman da cutar sankara ta fara kamashi in an kalle shi a ido ba za a ga wani canji ba, haka kuma a jiki ma ba za a ji komai ba.  Ba ya kawo ciwo, baya sa zazzabi, amai, gudawa ko rashin cin abinci kuma ba ya hana ayyukan yau da kullum.  Ba lallai ba ne a ce kin taɓa ganin ko jin labarin cutar ba, domin mai yiwuwa ne a ce bata taɓa kama wata yar uwarki ba ko wadda kika sani.  A wannan mataki na farkon shigar wannan cutar akwai fatan cewa in dai aka yi maganin wannan cutar za a iya warkar da ita.

Sankaran mama kuma tana iya farawa  ta hanyar fitowar ciwo a kan mama ko fatar da ta zagaye kan maman.

A wasu matan kuma, kan nonon ne zai fara shigewa ciki. Za’a ga mazaunin sa ba daya yake dana ɗaya ɓangaran ba.

Idan aka kyale tsiron, ci gaba zai yi tayi da girma. Zai iya girma daga cikin maman har ya ratso fatar maman ya zamo gyambo (ciwo) wanda yake fitar da ruwa  da jinni mai wari, kuma ba zai warke ba sai anyi maganin wannan cuta.

A sa’ar da wannan cuta ta cigaba da bunkasa, ta kan bazu zuwa wasu sassa na jiki kamar kwakwalwa, hunhu, kasussuwa da hanta ta wata hanya da ake kira (Metastasis) da turanci.  Ita wannan bazuwar zuwa ga wadannan gabobin ne ke cutarwa, kuma da zarar hakan ta faru, duk da cewa bayar da magani ya zama dole, samun waraka abu ne mai wahala. 

Za  a iya gane irin wannan buzuwar cutar ta hanyar samuwar tari, haki, kumburin ciki, ciwo a kasussuwa musamman ma baya, rashin karfin kafafu da rashin iya motsa su.

Shin za a iya gane cutar sankaran mama da wuri?

Za’a iya gane wannan cuta da wuri ta hanyar lura da halin da maman ke ciki.  Wannan wadansu matakai ne da mace zata rika bi sau daya a wata domin ta duba mamanta ko akwai wani tsiro, kumburi, ko wata cuta a jikin maman.  Ya kamata ki bukaci likitarki ta koya miki yadda zaki rika duba mamanki ita ma kuma ta duba miki mamanki a kalla sau daya a shekara.  Daukan hoton mamman a asibiti don binciken cutar, na iya taimakwa wajen gano ta da wuri.

Matakan Sankaran Mama

Ana iya fahimtar tsanin bazuwar da wannan cuta tayi a jikin marar lafiya ta hanyar matakin da cutar take a wannan lokacin. Waɗannan matakai su ne:

Mataki na I: Tsiron cikin maman da bai  kai sentimita biyu ba, ko kuma yana daidai da sentimita biyu.  Kuma idan aka gwada kaluluwar hammata za’a ga babu wannan cuta.

Mataki na II: Faɗin tsiron cikin maman yana tsakanin sentimeta biyu zuwa biyar tare da kaluluwar hammata wacce ta nuna akawai cuta ko kuma wacce ta nuna babu cutar. Zai kuma iya kasancewa faɗin tsiron cikin maman ya wuce sentimeta biyar tare da kaluluwar hammata wacce ta nuna cewa akwai cutar.

Mataki na III: Wannan matakin an kasa shi zuwa gida biyu A da B.

A: A nan faɗin tsiron cikin maman ya fi sentimita biyar, kuma akwai kaluluwar hammata masu motsi waɗanda suke dauke da wannan cuta.  Ko kuma girman kumburin zai iya zama ko ma ya ya da kuma kaluluwar wacce kaluluwar hammata waɗanda suka maƙalewa juna kokuma suna maƙale da wata tsoka dake wannan gurbin.

B: A nan faɗin tsiron cikin maman zai zama ko yaya amma ya bazu zuwa fata, bangon kirji, ko kaluluwa da suke can kasan nono kuma a can cikin kirji.

Mataki IV: A nan faɗin tsiron cikin maman ko ma ya girmansa yake anan ya bazu zuwa wurare masu nisa kamar ƙasussuwa, hunhu, ko kaluluwar jiki da suke nesa da mama.

Mataki na I da na II su ne farkon kamuwa da wannan cuta amma mataki na III da IV cutar ta riga ta bunkasa.

Yaya ake maganin cutar sankaran mama?

Ana maganin sankaran mama sabuwar kamu ta wadannan hanyoyi:

Surgery (Fiɗa): Wannan shine a cire maman gaba daya ko wani ɓangarensa ta hanyar fida.  Amma yin wannan fiɗa ya danganta da abubuwa da dama wanda zaki tattauna da likitanki.

Chemotherapy - Shine yin amfani da magani domin a kashe kwayoyin da suka gina wannan cuta, wadda ta riga ta bazu zuwa wasu ɓangarori na jiki ko a kankantar da wannan kumburi na mama.  Duk da dai waɗannan magunguna su na da illoli, amma akwai hanyoyin da likitoci sukan bi domin taimakawa mai wannan cuta wajen samun saukin waɗannan illoli.

Hormone Treatment - yin amfani da wannan sinadari na homon domin su hana kwayoyin wannan cuta girma.  Za a iya yin wannan ta hanyar fiɗa, radiotherapy, ko shan da magunguna.

Radiotherapy - yin amfani da kwayoyi na wuta wajen kashe kwayoyin wannan cuta.

Akwai hanyoyi da dama da ake bi a warkar da wannan cuta, sai dai ya danganta da bazuwarta a jiki,  zabin mai ɗauke da wannan cuta, kuɗin da za’a iya kashewa, da yadda za a iya daurewa bin ka’idojion shan magani, da kuma kayan aiki da ake da su.

Yin maganin wannan cuta ya kan ɗau lokaci mai tsaho kuma ana bukatar yawan zuwa asibiti.  Yana da tsada kuma yakan dau lokaci.  Duk wadannan abubuwa ne da suka zama dole a tattauna su da likita.

Haka kuma yana da kyau mai ɗauke da cutar sankaran mama ta tattauna da ‘yan uwanta domin su gane yadda cutar take domin su ba ta goyon baya da kwarin gwiwa, kuma su taimaka wajen faɗakarwa game da lura da mama.

Sakamakon magani

Karbar magani ga jiki ya bambanta daga mutum zuwa mutum kuma ya danganta da:-

·  Matakin cutar a lokacin da aka gano ta: Cutar da aka gano ta tunda wuri tafi saukin warkarwa.

· Yanayin cutar sankara: Saukin  warkewar ya danganta da irin cutar sankarar da ta kama mutum.  Ana gane irin cutar ne bayan an yi gwaje-gwaje akan tsiron da aka ciro daga jikin mai ɗauke da cutar.

· Bin ka’idojin magani ba tare da kuskerawa ba.

Idan babu kumburi a hammata kuma girman sankaran bai wuce girman sentimita uku ba ko kasa da haka, kashi casa’in da tara cikin dari na waɗannan majinyatan sukan rayu har tsahon shekara biyar.  Haka kuma kashi sittin  cikin dari na  majinyatan da suke da kaluluwar hammata guda biyu zuwa hudu za su iya rabuwa da cutar a cikin shekara biyar in aka haɗa da kashi arba’in cikin dari na masu ɗauke da kaluluwa shida zuwa goma.

Idan kuma cutar ta riga ta bunkasa fa? A na nufin kenan ba za ta warke ba? To in da rai da robo.  Domin kididdigar da aka bayar a sama, ta samu ne ta hanyar hada sakamakon mutane da yawa da aka yi.  Babu likitan da zai ce lallai yadda aka samu din nan, haka ne zai faru a kanki, koda a ce an yi ta maganin amma cutar ta ki warkewa, likita zai iya bakin kokarinsa wajen bada magunguna waɗanda za su rage zafin cutar.

To magungunan gargajiya fa? Abun sani anan shine, duk wanda yake jinyar mai ɗauke da cutar sankara, fatansa ne a samu sauki da wuri saboda mai cutar ta daina shan wahala. Abin takaici shine, cigaban da aka samu akan  shawo kan cutar a kimiyyance bai taka kara ya karya ba. Amma duk da haka, yafi amfani nesa ba kusa ba, yafi rashin cutarwa, kuma yafi tabbaci fiye da kowane irin hanyar magani da wani ko wata zai zo miki dashi a yanzu. A karshe, mutum zai iya taimakawaa ckin  binciken samo maginin da yafu na yanzu aiki ta hanyar ba da gudunmawa da haɗin kai ga masu bincike a asibiti.

Yana da mutukar amfani mutum ya je asibiti da wuri da zarar ya lura da waɗansu canje-canje don neman magani.

TARIHIN SHAIK AHMADU TIJJANI (RTA)

An haifi Shaihu Ahmad Tijjani, wanda ya kafa darikar Tijjaniyya, a garin Ainu Mali a shekara ta 1150 BH. Mahaifinsa ya rasu a lokacin yana da shekaru goma sha shida a duniya.Shaihu Tijjani ya haddace Alkur’ani yana dan shekara bakwai a hannun wani malami da ake kira Abu Abdullahi Muhamamd binu Hamu.

Sa’an nan ya ci gaba da neman ilmi inda ya karanta fannoni dabam-daban a hannun malamai masu yawa. Daga nan kuma sai ya karkata zuwa ga tafarkin Sufanci,ya shagala da yakar kai da hore dare da gudun duniya da sauran abubuwan dake hawa wuyan wanda ya bi tafarkin Sufanci.

A lokacin da Shaihu Tijjani ya yi nufin shiga sha’annin Sufanci tsundum, sai ya rabu da matarsa ta aure don ya zama ya samu damar tattara hankalinsa a kan abinda ya sa a gaba. Kuma a bayan da ya gamsu da cewa ya samu abinda ya samu a cikin wannan sha’ani, watau ya kai wani mukami babba a Sufanci, sai ya sayi kuyangi guda biyu, ya ‘yanta su, kana ya daura aure da su. Ya sanya wa dayarsu suna Mabruka dayar kuma Mubaraka.

Allah ya arzuta Shaihu Tijjani da ‘ya’ya maza guda biyu da kuma mata masu yawa. Babban dansa shi ne Muhammad Kabir, dan wajen matarsa Mabruka, na biyun kuwa shi ne Muhammad Sagir wanda aka yi wa lakabi da Habib. Shi wannan matarsa Mubaraka ce ta haifa masa shi, kuma shi ne ya zama halifar Shaihin na farko a bayan rasuwarsa.

Shaihu Ahmad Tijjani ya yi tafiye-tafiyeda dama wajen neman ilmin Sufanci, kuma ya shiga dariku masu yawa kafin daga bisani ya zauna a wuri guda ya kafa tasa darikar ta kansa. A lokacin dayake zaune a Moroko, Shaihin ya shigadarikun Qadiriyya da Nasiriyya da kuma darikar Shaihu Abul Abbas Ahmad Habib wanda aka fi sani da lakabin Algimari. Bayan ya bar wadan nan dariku duka, ya tashi daga Moroko ya nufi cikin hamadar Sahara inda ya ya da zango a zawiyar Shaihu Abdulkadir binu Muhammad Al’abayal.

Daga nan Shaihu Tijjani ya fita zuwa Hajji. A kan hanyarsa ta zuwa Makka, ya wuce ta kasashen Tilmisan da Tunis da Masar. Ya isa Makka a shekara ta 1187 BH, inda ya sauke farali kuma ya sadu da malamai masu yawa. Bayan kammala aikin hajji, ya komo ta kan hanyarsa ta Masar da Tunis, sa’an nan Tilmisan wurin da ya ya da zango kadan kafin ya wuce zuwa birnin Fas, inda ya ziyarci kabarin Maula Idris kakan Sharifan Moroko a shekara ta 1191 BH. A wannan tafiya ne har ila yau, a wani kauye da ake kira Wajda, Shaihu Tijjani ya gamu da babban alamajirinsa, Shaihu Ali Harazimi.

A shekara ta 1196 BH, Shaihu Tijjani yakafa darikar Tijjaniyya a wani gari da ake kira Abu Samgun wanda a yanzu yake cikin kasar Aljeriya. Sa’an nan ya yi kaura daga wannan garin ya koma birnin Fas, a cikin kasar Moroko, inda Sarkin Moroko na wannan lokaci, Sarki Sulaiman, ya ba shi gida wanda ya zauna a cikinsa har zuwa karshen rayuwarsa. A nan ne kuma ya kafa zawiyarsa, ya tattaro alamajiransa, kuma ya ci gaba da aikin yada darikarsa. Shaihu Tijjani ya rasu a shekara ta 1213 BH. Ya bar matan aurebiyu, ‘ya’ya maza biyu da mata masu yawa.Sabanin Sidi Abdulkadir, Shaihu Tijjani ya mutu bai bar wani littafi da ya tattare lamuran darikarsa ba.

Amma mutane uku daga cikin manyan almajiransa sun rubuta littafai wadanda suka kunshi tarihin Shaihin da ka’idojin darikarsa da kuma ra’ayoyinsa dangane da tafarkin Sufanci. Wadan nan alamajirai su ne, Shaihu Ali Harazimi wanda ya rubuta littafin Jawahirul Ma’ani, Shaihu Muhammad binu Mushri wanda ya wallafa Aljami’u fil Ulumil Fa’ila da Shaihu Muhammad Dayyib Assufyani, wanda ya rubuta Al’ifadatul Ahmadiya. Daga wadan nan littafai ne mai bincike zai iya samun kusan duk abinda yake bukata dangane da darikar Tijjaniyya da tarihin Shaihinta.

Darikar Tijjaniyya tana da sharadai guda bakwai wadanda su ne harsashen da aka gina ta a kansa. Sharadan su ne kamar haka:

1. Wanda ya shiga darikar Tijjaniyya, yakarbi wurdinta, to ba ya fita har abada.

2. Kar ya gama ta da wata darikar dabam, watau kada ya zama yana Tijjaniyya kuma yana yin wata darikar alokaci guda.

3. Kada ya ziyarci wasu waliyyai, na raye ko mamata, sai dai Sahabban Annabi (SAW) kawai, da Shaihu Tijjani da sauran Shaihinnan Tijjaniyya.

4. Ya lazimci tsoron Allah a ko wane hali.

5. Ya lazimci kaunar Shaihu Tijjani da zuri’arsa da almajiransa.

6. Ya debe kauna daga abinda yake hannun mutane na samu, sai dai abinda suka kawo suka ba shi ba tare da ya roka ba.

7. Har abada ya rika sada zumunci da sasanta tsakanin ‘yan uwa.

Wurdin Tijjaniyya kuwa ya kasu gida uku:•

Na Farko: Wurdi Lazimi, watau wurdin farilla.
Wannan ya kunshi istigfari kafa dari, salatin Annabi dari, da hailala dari.
Ana yin wannan wurdi safe da yammaci.
Lokacin wurdin safe shi ne tun daga bullowar alfijir har ya zuwa lokacin walaha.
Lokacin wurdin yammakuma, daga bayan La’asar zuwa sallar Isha. Wanda lokacin safe ya wuce shi bai yi wurdin a cikinsa ba, to wannan zai iya ramawa a sauran wuni duka.
Wanda lokacin yamma ya wuce shi kuwa, yana iya ramawa a sauran dare duka. Haka nan, wanda wurdin rana guda (watau safe da yamma gaba daya) ya wuce shi, to dole ya biya wannan wurdi har abada.
Watau ana bin sa bashin wannan wurdi har tsawon rayuwarsa. Wannan shi ne wurdin farilla, ko kuma Lazimi.•

Na Biyu: Wurdin Wazifa.
Wannan ya hada da istigfari kafa dari, Salatul Fatihidari ko hamsin, Hailala dari ko dari biyu, da kuma wata addu’a da ake kira Jauharatul Kamal kafa goma sha daya.
Ba’a karanta Jauhara sai da cikakkiyar alwala, kuma taimama ba ta isarwa wajen karatun ta.
Wazifa ba farilla ba ce, saboda haka ana iya yin ta a safe da yamma ko kuma a lokaci daya kawai.•

Na Uku: Zikirin Jumma’a.
Wannan anayin sa ne ranar Jumma’a kawai, kuma ba ya inganta sai a cikin jama’a.
Lokacinsa shi ne daga bayan sallar La’asar har zuwa faduwar rana. Baya inganta mutum daya ya yi zikirin jumma’a sai fa in ya zama a garin babu‘yan Tijjaniya. Zikirin Jumma’a ya kunshi Hailala ne kawai, kuma bai da wani adadi kayyadajje.

Darikar Tijjaniyya ta watsu a sassa da dama na duniyar Musulmi. Daga cikin kasashen da ake samun mabiyan darikar akwai Masar, Turkiya, Muritaniya, Sudan, Senegal, Nijeriya, Gini, Gambiya da sauransu.

Thursday, 28 August 2014

Ciwon Sarke Hakora (Tetanus)

Ciwon sarke hakora ko tatanas kamar yadda wasu suka fi sanin sa da shi, shi ma nau’in ciwo ne da kan iya kama kowa, manya da yara, kuma kwayoyin cuta na bacteria da ake kira Clostridium tetani ke haddasa shi, kuma suna nan a kowane yanki na duniya.

Su wadannan kwayoyin cuta a cikin kasa suka fi rayuwa, amma iska kan kwashe su su bazu, wasu su hau fatar jiki. Idan suka samu suka shiga jiki sai su rika samar da wata guba da kan kama jijiyoyin jiki, su hana wurin motsi.

An yi kiyasin cewa duk shekara wannan ciwo na halaka mutane kusan dubu dari uku, yawancinsu jarirai, musamman a kasashe irin namu.

Yadda ake kamuwa da ciwon sarke hakora:
kwayoyin za su iya shiga jiki ne yayin da mutum ya ji rauni komi kan kantarsa (ko yanka ko kujewa ko gyambo ko kuna ko cizon wata dabba), idan  ba a dauki matakin kariya ba.

Jariri kan iya dauka a jikin abin da aka yanke cibi da shi, in ba mai tsabtaba ne. Bayan kamar kwanaki hudu zuwa mako biyu da yankan cibi ko yin rauni, gubar da kwayoyin cutar ke saki ta fara barna, za a ga jariri yana ta amai da zazzabi da yawan kuka da kin karbar mama. Wadannan su ne alamu na farko, in ba a dau matakin kai wa asibiti ba, za a ga wani bangare na jikin jariri ko kuma duk jikin gaba daya yana jijjiga, ko yana sandarewa.

A manya kuwa za a fara jin mukamukai sun cije, hakora sun sarke, sai wuya ya sandare, a kasa hadiyar ruwa ko abinci, sanadiyar wannan guba ta kwayoyin cutar. In ba a dauki mataki ba, haka za a ga duk jiki ya sandare daga sama zuwa kasa, wato daga kai har zuwa kafa, mara lafiya na bankarewa.

Kashi 40 zuwa 80 cikin dari na masu wannan karkarwa da sandarewa ba sa kai labari ko an je asibiti.

Hanyoyin kariya daga wannan ciwo: Allurar riga-kafin kamuwa da ciwon sarke hakora ita ce hanyar da aka tabbatar za ta kare kamuwa daga wannan ciwo.
Saboda haka:

1. Kowa da kowa ya samu a yi masa allurar riga-kafin sarke hakora akalla sau daya a cikin shekaru goma.

2. Mata masu ciki su rika zuwa awo domin a wurin ne ake ba da allurar riga-kafin wannan ciwo. Jaririn da ke ciki kan samu nasa rabon ta mahaifa.

3. A kai yara daga wata biyu ga cibiyoyin riga-kafi, a basu wannan allura, a sake komawa in sun kai wata hudu da wata shida, sannan duk yara daga shekaru 3-7 domin su suka fi yin rauni a yau da kullum ba tare da iyaye sun sani ba.

4. Idan yaro ko wani babba ya yi rauni, bayan zuwa asibiti an wanke ciwon, an ba da magunguna, to a tabbata an karbi allurar tatanas don yin riga-kafi.

5. A tabbatar ungozoma mai karbar haihuwa a gida tana amfani da sabuwar reza ko aska wajen yanke cibi, ba tsohuwar reza ko aska ba, domin ko tafasa reza da askar baya kashe kwayar cutar tatanas.

6. Manoma su yawaita zuwa karbar wannan allura, su kuma rika amfani da takalmin ruwa irin na roba domin wani zubin sukan yi rauni da lauje ko fartanya ba tare da ma sun sani ba.

7. A yi hanzarin kai jariri mai yin jijjiga ko mai nuna alamomin da aka zayyana a sama asibiti mafi kusa, ko da mai gida ba ya kusa, musamman in a gida aka haifi jaririn.

8. A yi hanzarin kai duk wani babba da hakoransa ko mukamukansa suka cije, ya kasa magana ko cin abinci asibiti mafi kusa.

Allah ya kara mana lafiya.

Friday, 20 June 2014

HUKUMCIN AZUMIN YA MACE A SHARIA

BAYANI AKAN HUKUMCIN AZUMIN MACE A SHARI’A

Daga www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah mai yawan Rahama,  Mai yawan jin kai, tsira da Aminci su kara tabbata ga fiyayyan halitta Annabin rahama, tare da saabbansa da iyalan gidansa, da duk masu binsa da kyautatawa har zuwa ranar Alkiyama.

Bayan haka Azumin watan Ramadan wajibi ne akan kowanne musulmi Namiji da musulma mace, kuma yana daya daga cikin manya manyan ginshikan musulunci, kuma daya ne daga cikin rukunansa, kamar fadin Allah (SWT) cikin littafinSa Mai tsarki cewa: "Yaku wadanda kuka yi imani, an wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi ga wadanda suka gabace ku, don kuji tsoron Allah" (Bakara aya ta 283).

Kamar yadda shari'a ta dora yin azumi akan namiji, haka ta dorawa ya mace yinsa, na Ramadanne ko na nafila, amma kuma shari'a ta rwangwantawa mace game da yin azumin a wasu wurare ko kuma ace awasu lokuta, wannan saboda kasancewar mace mai rauni ta fanin shari'a da hankali,

Idan watan ramadan ya tsaya to ya wajaba akan ko wanne musulmi da musulma, baligai, kuma masu lafiya, mazauna gida su yi azumi, ma'ana su kame bakinsu daga ci ko sha ko saduwar aure daga fudowar alfijir har zuwa faduwar rana, wanda kuma ya kasance mara lafiya ko yazamo matafiyi acikin kwanakin azumin ramadan, to ya halata agare shi da ya sha azumin sa'annnan ya rama adadin kwanakin da ya sha acikin kwanakin da bana ramadanba.

Allah (SWT) yace: "Wanda ya riski wata dag a cikin ku, to sai ya azumce shi, wanda kuma ya zamo maras lafiya ko matafiyi, to sai ya rama a kwanaki na gaba..." (bakara aya ta 185).

Don haka duk wanda watan Ramadan ya riske shi amma ya tsufa tukuf, ko kuma mara lafiya dake a kwance, da ba'a sa ran zai warke daga rashin lafiyar, mace ko namiji, to ko wanne daga cikin wadannan zai sha azumin, amma sai ya ciyar da miskini daya rabin sa'i, ma'ana mudu biyu na galibin abincin kasar, amaimakon ko wace rana, wacce ya sha azumi acikin ta. kamar yadda Allah maigirma da daukaka ya bayyana cikin suratul bakara aya ta 184.

To anan mace ma shari'a ta bata damar shan azumi saboda wadansu uzururuka wadanda ke faruwa agareta wadanda basa faruwa ga da namiji, wadannan uzururruka sune kamar haka:-

1. JININ HAILA DA JINI BIKI:- 
Ya haramta ga mace mai jinin biki ko na haila tayi azumi, amma kuma wajibi ne ta rama azumin awasu kwanaki da ba na ramadana ba, sabanin salloli su baza ta rama su ba.
Saboda Nana A'isha (RA) tace:- "Mun kasan ce ana umurtar mu da rama azumi amma ba'a umurtar mu da mu rama salla. Awata ruwayar ta imam muslim yace, "Mu'azatu tace na tambayi Nana A'isha nace saboda me mai haila zata rama azumi amma bazata rama sallah ba, sai tace:- ke 'yar (khawarijawa ce) sai nace ni ba ita ba ce nadai tambaya ne kawai, sai tace dani hakan na samun mu, sai aka umurce mu da mu rama azumi, amma ba'a umurce mu da mu rama salla ba, kuma ta kara da cewar wadannan al'amura ne da mutum yake tsayawa inda aka tsai da shi, ba ra'ayi ake bi ba a’a nassi ake bi. idan kuma mace taga farar kassa, wato wani ruwa da mahaifa take fitarwa bayan karewar jinin haila, wacce mace ke gane samun tsarkinta idan ta gan ta, to sai ta daura  niyya don daukan azumi. idan kuwa bata da wata takamaimiyar hanyar samun tsarki sai tayi kunzugu da Auduga ta gargajiya ko 'yar kanti, ko dai wani abu makamancinta kamar tolet paper, idan ta cirota da ganta tsaf babu jini ta tsarkaka kenan, to sai ta dauki azumi, amma kuma idan bayan ta dauki azumi sai jinin ya dawo mata a wannan ranar, to sai ta sha azumin, amma idan bata sha ba sai jinin ya dauke kafin magariba, to azuminta ya ingan ta. sa'annan matar da taji alamar fitowar jinin haila amma sai bai fito ba, sai bayan magariba to ita ma azumin ta yayi.
Matar da take haila sai jinin ta ya dauke tun dare sai tayi niyar yin azumi, kuma ta kasance bata yi wanka ba har alfijir ya keto to azumin ta ya ingan ta, bisa mazhabar daukacin malamai.
matar da tasan cewar gobe ne jini zai zo mata, amma sai ta tashi da azumi to ba zata ci abinci ba har sai idan jinin ya zo mata, sannan sai ta sha azumin, idan kuma bai zo mataba sai taci gaba da azuminta.
Mai biki idan ta samu tsarki kafin kwanaki Arba'in da haihuwar ta, to sai tayi wanka tayi niyyar azumi, amma idan jinin ya haura kwana Arba'in bai dauke ba to sai ta dauki jinin a matsyin jinin istihada (wato jinin cuta) sai dai kuma idan jinin ya yi dai dai da lokacin al'adarta wadda take yi duk wata, to wannan kam sai ta dauke shi amatsayin jinin haila.

2. Mace mai ciki da mai shayarwa:- Itama mace mai ciki ko mai shayarwa idan har yin azumi gareta zai cuce ta, ko ya cuce jaririn ta, ko kuma duka su biyun zasu cutu, to ita ma anyi mata rangwame akan ta sha azumi a cikin halin cikin ko shayarwar.
Amma kuma idan yin azumin zai cutar da jaririn ta ne kawai ban da ita, to zata rama azumin kuma ta ciyar da miskini daya maimakon azumin da duk ta sha aduk lokacin da tazo ramawa, amma idan yin azumin zai cutar da ita ne ita kadai to zata rama azumin kawai banda ciyarwa.Top of Form Domin Ayar da ke yin bayani akan wanda ke iya yin azumi amma da kyar to lallai akwai mace mai ciki da mai shayarwa idan suka jiwa kansu ko jaririn su tsoron cutuwa.
Don haka zance mafi rinjaye anan shine anyiwa mace mai ciki da mai shayarwa kiyasin marar lafiya don haka ya halatta da su sha azumin kuma ba su da kaffara sai dai ramuwa, ya Alla suna jiwa kan su tsoro ko suna jiwa 'ya'yan su tsoro, hujjar wannan itace ruwayar Imamu Tirmizi yace: Annabi (SAW) yace: Allah madaukakin sarki ya daukewa matafiyi wani yanki na azumi (wanda ya sha alokacin tafiyar sa) da wani yanki na sallah (yana nufin yin kasaru) kuma ya daukawa mace mai ciki, da mai shayarwa yin azumi.

3. Jini rashin lafiya:- ko kuma jinin ISTIHADHA macen da jini yake zuwar mata bana haila ba, azumi wajibi ne akan ta, bai halatta ta sha azumi saboda wannan jinin domin shi jinin rashin lafiya ne kamar zuwan kumallo ne ko fitar jini saboda rauni, ko fitar ruwan kurji, duk wadannan abubuwa ne wadanda basu da lokaci kayadadde na zuwan su, balantana ace mace tabar azumi domin su, ma'ana zuwan su ba zai hana mata yin azumi ba. 4. Matar aure:- Bai Halata ga Macar aure tayi Azumin Nafila ba, alhali mijin ta na gida sai da izinin sa ko idan baya gari ya yi tafiya, amma kuma ban da na ramadan, macen da azumi ya wajaba akan ta idan ta dauki azumin ramadan sai mijinta ya tara da ita da rana alhali tana dauke da azumin ramadan, kuma bisa yardarta, to dukkan su zasu yi ramuwa da kaffara, amma idan tilasta mata ya yi, to tayi iyakar kokarin ta na hana shi, amma bata yi nasarar hana shi ba, to ita babu kaffara a kanta sai dai ta rama azumi. Amma idan mace tana barci acikin watan ramadan sai mijinta ya tara da ita, to malamai sunce ita ma babu kafara akan ta sai dai ta rama azumi.

Anaso ga mace budurwa ko wacce mijinta ya yi mata izinin yin Azumin da ta rika yawan yin azumin nafila, ko yin Azumin mustahabbi (wato abin da aka so) da kuma yin azumin a ranakun litinin da Alhamis, da kwanaki shida na watan shawal, (wato Sittu Shawwal) da kwanaki goman farko na zulhijja, (Wato Ashara Zulhijja) da azumtar ranar Arafat da ranar Tasu'a da Ashura, sai dai kuma bai kamata ba gareta da tayi azumin nafila ba, alhali ana binta ramuwar wani azumin, har sai ta rama azumin da ake bin ta. kuma ya kamata ga duk matar da ta san cewa mijin ta baya iya danne sha'war sa a duk lokacin da dama ta samu, to ta nisanci mijin ta acikin azumi, kuma ta daina yin ado ko kwalliya a cikin watan azumi.

Akarshe malamai sun ce wajibe ne akan mace ta ramuwa azumin da ake binta kafin kamawar wani azumin, sai dai idan da wani uzuri mai girma, amma idan bata rama ba har wani azumin ya kama, ba tare da wani uzuri ba, to duk yayin da tazo rama wa, bayan ta rama sai ta ciyar da miskini daya. Kamamalawa Abin da akeso agare ki ya ke 'yar'uwa Musulma, idan kina Jinin haila to ki zauna bisa al'adarki tayin jini a duk wata, ki yarda da abinda Allah (SWT) ya hukunta agareki, kada kiyi kokarin shan wani abu da zai hana jinin fitowa, ki karbi abin da Allah ya yarje miki, na shan azumin akwanakin haila da yin ramuwar su bayan salla, domin kuwa haka matan Annabi (SAW) iyayen muminnai, da matan salihan bayin Allah, suka hakura.Amma idan kika ki, kika sha wani magani domin hana fitar jinin haila a watan azumi, jinin kuwa ya dauke kika samu tsarki kika cika azumin ki cif cif, batare da kin sha ko daya ba, to babu kommai amma baki yi koyi da iyayen muminai ba, kuma baki samu ladan yin koyi da salihan bayi ba.

Wannan shine dan abi da ya sawwaka game da hukumcin da shari'a ta dorawa mace game da azumi, da fatan zamu amfana, abin da akji na daidai daga Allah ne na kuskure kuma daga gareni ne, ina sauraron gyara,

Akulu kauli hadha wa astagfilullaha li wa lakum Wassalamu alaikum warahamatullah.

ADDUA TAKOBIN MUMINI

Addu’a takobin mumini
Daga www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jinkai.  Dukkan yabo da godiya su tabbata ga  Allah, Ubagijin halittu baki daya.  Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga mafificin halittu, Annabi Muhammadu sallallaahu alaihi wasallam, tare da alayensa da sahabbansa  baki daya, da duk wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar karshe.   Bayan haka, a yau inaso in dan yi tsokaci ne a kan addu’a a matsayinta na takobin mumini.  Za mu ga ma’anarta da falalarta da lokuta da guraben da ake karbarta, sannan da ladubbanta.  Haka nan akwai nau’in wadanda ake karba musu addu’a da kuma wadanda ba a karba musu ko kuma ake jinkirta musu. Sannan da bayanan a kan dalilan dasuke sawa ba a karbar addu’a  duk daga abin da aka cirato daga zantuka da bayanan magabata na kwarai, Allah Ya jikansu da rahama.  Sai kuma wani waige a kan Istikharah. Bismillah! MA’ANARTA A Larabce addu’a na nufin kiran wani, ko neman miko wani abu.  Suna cewa: da’aa bil kitabi, ma’ana ya nemi a miko masa littafi.  A isdilahi  kuma addu’a tana nufin tarin kalmomin yabon Ubangiji, masu nuni ga neman wani abu daga gare Shi, ko neman tsarin wani abu (sharri) daga gare Shi. FALALARTA “An karbo daga dan Abbas, Allah Ya yarda da shi cewa Yahudawan Madina sun tambayi Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) suka ce: ‘Ta yaya Ubangijinmu Zai ji addu’armu, bayan kai kana zaton cewa tsakaninmu da sama kimanin tafiyar shekara dari biyar ne.  Kuma tsakanin kowace sama da ’yar uwarta ma haka ne ?’  Sai Allah Ya saukar da:  “Duk lokacin da bayiNa  suka tambaye ka game da Ni, to Ni Makusanci ne. ina amsa addu’ar mai roko in ya roke Ni.”  Bakara aya ta 186 ( daga Algunya ta Sidi Abdulkadir Shafi Na 373). Ma’aiki, sallallahu alaihi wasallam,  ya ce “Addu’a ita ce ibada.”  Kamar yadda aka fitar a littafin Riyadhussalihin na Imam Nawawi a Kitabul – da’awati . A wata riwayar kuma ya ce: “Hakika Ubangiji na mu’amala irin ta jin kunya.  Idan bawa ya buda hannu ya roke Shi, Ya ki amsa masa,  ko dai ya gaggauta masa a amsawar tun a duniya, ko ya jinkirta masa sai a ran kiyama.” LOKUTA DA GURABEN AMSA ADDU’A Ana karba (amsa) addu’a a wurare da lokuta da kuma guraben yanayi kamar haka: 1- Yayin sujjada. 2- Lokacin alwala. 3-Lailatul kadri. 4- Yayin saukar ruwan sama. 5- Tsakar dare. 6- Tsakanin kiran sallah da ikama. 7- Ranar Juma’a 8- Ranar  Arfa. 9- Yayin kiran sallah.        10- Bayan kiran sallah. 11- Bayan jifan shaidan.      12- A Safa da Marwa. 13- Sallolin farilla.        14- Watan Rajab. LADUBBAN ADDU’A Yana daga cikin ladubban addu’a mutum ya kasance yana da: 1- Ikhlas – wato ya kasance yana da tsarkin zuciya, ya fuskanci Allah kadai a cikin abin da yake bukata. 2- Kyakyawan zaton amsa ta. 3- kankan da kai da sassauta sauti. 4- Shiga (suturarsa) da ci da shansa su kasance na halal. 4- Fuskantar alkibla.   5- Naci a addu’ar. 6- Cudanyata da yabon Ubangiji da kirari gare Shi. 7- Salatin Annabi farko da tsakiya da karshe. 8- Fadada abin nema ga sauran musulmai. 9- Yin ta a tsanani da walwala. 10- Halarto zunubi da bayyana tuba. 11- Bijiro ni’imomi da bayyana godiya ga Allah. 12- daga hannu sama da shafar fuska da shi bayan addu’ar. WADANDA BA A KIN AMSA ADDU’ARSU 1- Mai azumi yayin buda baki.   2- Wanda aka zalinta. 3- Shugaba nagari.   4- Matafiyi kan yardar Allah. DALILIN kIN AMSA ADDU’A Wofintar addu’a ga ladaban amsa ta na jawo kin amsa ta.  An tambayi Shehi Ibrahim  dan Adhama, Allah Ya yi masa rahama, cewa ‘ko me ya sa muke rokon Allah ba Ya amsa mana?’ Sai ya ce saboda :- 1- Kun san sunnar Ma’aiki, sallallahu alaihi wasallam, ba ku bi. 2- Kun san Alkur’ani ba ku aiki da shi. 3- Kuna cin ni’imomin Ubangiji ba ku godiya. 4- Kun san Aljanna ba ku nemanta. 5- Kun san wuta ba ku tsoranta. 6- Kun san shaidan kuna binsa. 7- Kun san mutuwa ba ku yi mata tanadi ba. 8- Kun san mamata ba ku tunawa da su. 9- Kun bar abinku kun shagalta da na mutane. Haka nan Allah Yakan jinkirta wa bawa addu’rsa don soyayya, kamar yadda hadisi ya bayyana cewa, “Bawa kan roki Allah Ya biya masa da wuri, saboda ba Ya son jin muryarsa; wani (bawan kuma) ya roka a jinkirta masa, saboda son jin muryarsa da Allah Yake .” TSAWAITA  ADDU’A KO TAKAITA TA Nana A’ishah, Allah Ya yarda da ita, ta ce Manzon Allah,  sallallahu alaihi wasallam, yana son  dunkulalliyar addu’a, yana barin watanta (ma’ana ba ya tsawaita mai wuce haddi), kamar yadda aka fitar a littafin Riyadhussalihina a Kitabul da’awati shafi na 264). ISTIKHARAH Wannan na nufin neman zabin Allah kan wani al’amari da bawa yake so ko zai aikata. Sayyadina Jabir, Allah Ya kara masa yarda, ya ce “Ma’aikin Allah, sallallahu alaihi wasallam, ya kasance yana koya mana istikhara a duk al’amari , tamkar sura daga Alkur’ani.  Yana cewa, ‘idan dayanku ya nufi wani al’amari, sai ya yi sallar nafila raka’a biyu, sai ya ce: Allahumma inni astakhiruka bi ilmika wa astakdiruka bi kudratika wa as’aluka min fadlikal azim fa innaka  takdiru wala akdiru wa ta’alamu wala a’alamu wa anta allamul guyub; allahumma in kunta ta’alamu anna hazal amra khairun li fi dini wa ma’ashi  wa akibati amri fakdirhu li wa yassirhu li summa barik li fihi; wa in kunta ta’alamu anna hazal amra sharrun li fi dini wa ma’ashi wa akibati amri fasrifhu anni wasrifni anhu wakdir liyal khaira haisu kana summa ardhini bihi  (sai mutum ya ambaci bukatarsa) – Imamul Bhukari. Tabbas Allah na fushi da bawanSa in ba ya rokonSa.  Allah Ka daukaka Musulunci da musulmai, Ka rusa kafirci da kafirai.  Ka yalwata mu da soyayyar Ma’aikinmu, sallallahu alaihi wasallam, Ka sa al’amarinmu ya kasance a ranar mutuwarmu muna masu cikawa da kalmar la’ilaha illallah muhammadur rasulullah

Tuesday, 17 June 2014

Bayani akan Aikin Hajji a takaice

Takaitaccen bayani kan aikin Hajji
Daga: www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah mai yawan Rahama mai yawan jinkai, tsira da aminci sukara tabbata ga Shuhaban Halitta da dukkanin sabansa baki daya.

Bayan haka Shi dai aikin Hajji ya kasu kashi uku ne:
1. Hajjin Tamattu’i.
2. Hajjin Kirani.
3. Hajjin Ifradi.

1. Hajjin tamattu'i: Shi ne wajibin wanda yake zaune a nesa da garin Makkah, nisan da ya kai mil 48, yayin da Hajjin Kirani da Ifradi sune wajibin wanda yake zaune a garin Makkah da kewayenta, wato nesansu da garin Makkah bai kai mil 48 ba. To amma a aikin Hajjin bakance, ko na mustahabbi, ya halatta ga mazaunin Makkah da wanda ke nesa da Makka ya zabi duk aikin Hajjin da ya ga dama tsakanin raben-raben da aka ambata a sama.
To bisa la’akari da cewa aikin Hajjin Tamattu’i shi ne wajibin mafiya yawa mutane, musamman mutanenmu, don haka za mu yi bayani ne kan wannan nau’i na aikin Hajji.

Ga yadda ake yin Umurar Tamattu’i: Da farko mutumin da ya yi niyyar yin aikin Hajjin Tamattu’i zai fara ne da daura harami a daya daga cikin wararen da ake daura haramin guda biyar, ko kuma abin da ake ce wa ‘mikati,’ wato: 

(1) Zul Hulaifa 

(2) Akik 

(3) Juhfa 

(4) Yalamlam 

(5) Karnil Manazil.


1. Harami: Shi ne sanya kyallen tufafin nan guda biyu da Alhaji zai sa yayin aikin Hajjin. 

Yadda ake daura harami shi ne: Mutum zai yi niyyar yin harami da Umurar Tamattu’i na Hajjin wajibi, sannan ya sanya tufafin haraminsa guda biyu, zai daura guda, ya kuma yafa guda, wato ya yi mayafi da shi. Daga nan sai ya fara ‘talbiyya’ wato fadin: Labbaikallahumma labbaik, labbaika la sharika laka labbaik, innal hamda, wan ni’amata laka wal mulk, la sharika laka. To idan mutum ya yi haka ya zamanto muhrimi (wanda ya daura harami) kenan da aikata wasu abubuwa suka haramta masa kamar su kusantar mace, shafa turare, sanya kewayayyen tufafi ga namiji, farauta da makamantansu. Akwai kuma wasu ayyuka na mustahabi da ake so mutum ya aikata, misalin yin wanka kafin daura harami da makamantan hakan. 

2. Dawafi: Abu na biyu cikin aikin Umrar Tamattu’i shi ne Dawafi, wato kewaya Dakin Ka’aba. Yadda kuma ake yin sa shi ne: Mutum zai fara da yom niyyar Dawafin Umurar Tamattu’i ne,sai ya fara zagaya Dakin Ka’aba har sau bakwai, zai fara ne daga inda Hajrul Aswad yake, wato Dakin Ka’aba na hannunsa na hagun. Idan ya fara daga wajen Hajrul Aswad ya zagayo ya zo wajen da ya fara, to ya yi guda kenan, haka-haka har sau bakwai.

3. Sallar Dawafi: Idan mutum ya gama dawafi wato ya kewaye Dakin sau bakwai, sai ya yi sallar Dawafin raka’a biyu a Makama Ibrahim. Wannan shi ne wajibin Umura ta Tamattu’i.

4. Sa’ayi: Wajibi na hudu shi ne Sa'ayi, wato tafiya tsakanin Safa da Marwa, yadda ake yin ta kuwa shi ne: Mutum ya yi niyyar yin Sa'ayi na Umrar Tamattu’i na Hajjin wajibi, sai ya fara tafiya daga Safa ya zo Marwa, daya kenan, sannan daga Marwa ya zo Safa, biyu kenan har sau bakwai. Wato tafiya daga Safa zuwa Marwa sau hudu, daga Marwa kuma zuwa Safa sau uku, wanda karshen tafiyar za ta kare ne a Marwa.

5. Aski: Wajibi na biyar kuma na karshe a Umurar Tamattu’i shi ne: Aski, ko kuma saisaye, mutum ya aske wani abu daga cikin gashin kansa ko gemunsa, ko gashin bakinsa, ko kuma ya yanke farcensa. Da hakan ne ake kare aikin Umurar Hajjin Tamattu’i, wanda hakan na nufin kenan dukkan abubuwan da aka haramta masa saboda harami a halin yanzu ya halatta a gare shi, misali kusantar mace, sanya turare da sauransu. Daga nan sai mutum ya jira lokacin daura haramin Hajjin Tamattu’i.

HAJJIN TAMATTU'I: 

Ayyukan Hajjin Tamattu'i Su ne: 

1. Saka harami a Makka.

2. Tsayuwa a Arafa.

3. Tsayuwa a Mash'arul Haram.

4. Jifan Jamratul-Akaba (jifan shaidan).

5. Yin hadaya.

6. Aske gashin kai ko rage shi.

7. Kwana a Mina a dare na sha daya.

8. Jifan jamrori(shedanu) uku a rana ta sha daya.

9. Kwana a Mina a dare na sha biyu.

10. Jifan jamrori (shedanu) uku a rana ta sha biyu.

11. Dawafin hajji.

12. Sallar dawafi.

13. Sa'ayi (Safa da Marwa).

14. Dawafin mata.

15. Sallar dawafi.

HUKUNCE - HUKUNCEN HAJJIN TAMATTU'I

An shardanta wa hajjin tamattu'i abubuwa kamar haka:

Na daya: Niya, ita ce nufin aikata irin wannan nau'in hajjin yayin daura ihramin umarar. Idan ba haka ba, bai inganta ba.

Na biyu: Ya zama umrar da hajjin ya yi su a watannin aikin hajji.

Na uku: Tilas ya yi hajji da umrar a cikin shekara guda.

Na hudu: Ya zama mai yin hajjin da umrar mutum guda ne.

Da zai dauki hayar mutum biyu su yi wa mamaci hajjin tamattu'i, watau daya ya yi umra dayan kuma ya yi masa hajjin, bai isar masa ba.

Riba Da Illolinta A Musulunci

Riba Da Illolinta A Musulunci

Littafin Da yake Tsoratarwa Game da Masu mu’amala da Riba, da Hatsarin dake cikinta

 

 

 

 

 

 

Wallafar

 

Comrade Auwal Zakari Ayagi

(Barden Ayagi)

2025

Haqqin Mallaka (M): Auwal Zakari Ayagi (Barden Ayagi)

Lambar Waya:      07038775781

Bugu Na Xaya      2025/1446

 

 

 

 

 

 

 

 

TSARAWA DA BUGAWA

Al-Azmiyya Islamic Foundation: No. 313 Al’Mustapha House Kadawa Western Bypass AL’EEMAAN Medicine Store Building, Adjacent to Gwarzo Road Kano.

E-mail: auwalzakari@gmail.com

www.sautulazimiyya.blogspot.co.uk/

GSM:  07038775781, 08023615685


Sadaukarwa

Na sadaukar da wannan Littafi ga Mahaifana Marigayi Alhaji Zakari Muhammad Usman Ayagi (Allah ya gafarta masa) da Mahaifiyata Hajiya Rakiya Usaini Lawan (Inna) Allah ya qara mata Lafiya, Amin.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Godiya

Da sunan Allah mai yawan Rahama Mai Jin qai, Tsira da Aminci su qara tabbata ga shugaban halitta Annabi Muhammad Tsira da Aminci su qara tabbata a gareshi.

Bayan haka ina godiya ga Allah Subhanahu wata’ala da ya bani ikon rubuta wannan qaramin littafi mai Suna: RUBA DA ILLOLINTA A MUSULUNCI.

Godiya mai tarin yawa ga Malamaina, da Abokaina Almajirai bisa ga yanda suka bani kwarin gwiwa wajen ganin na wallafala wannan littafi.

Daga qarshe nake mai qara Addu’a ga dukkan ‘Yan’uwa da suka bada gudunmawa wajen kammaluwar wannan littafi, Allah ya sakawa kowa da Alhairi Ameen.

Auwal Zakari Muhammad Ayagi

 (Barden Ayagi)

5 ga Zulhijja 1445= 1/6/2025


 

Ta’aliqi

Da sunan Allah mai rahama da jinqai. Salati da taslimi ga fiyayyen halitta salallahu alaihi wasallam.

Batan haka, na ke tofa ‘yan kalmomi game da wannan littafi, wanda na nazarce shi tun daga gabatarwa izuwa kammalawa, inda ya qunshi babuka guda uku, da nuquxoxi ashirin da biyu cikin ayoyi da Hadisai da maganganun malamai masana duk cikin bayanin ita riba da kuma illolinta, wanda xan uwa Com. Malam Auwal Zakariyya Ayagi/Kabuga ya wallafa, Allah ya saka masa da alkhairi. Kalmomi na suna ne:

·        Babu shakka mawallafin ya fito mana da illolin riba fai-da-fai tarwai abun da ya rage mana shi ne mu karanta wannan littafi kuma mu yi aiki da abin da ke ciki gwargwadon iko.

·        Wannan littafi ne da zai yi mutuqar amfani kuma littafi ne da ya zo a lokacin sa, wato wannan zamanin da mu ke ciki na yaki halal yaki haram, lokaci na a yi kuxi dare xaya, inda da yawan mu ke mance faxin Allah (يا أيها الذين آمنوا عليهكم أنفسكم).

·        Littafi ne da ya kamaci a ce kowane xan kasuwa ya mallake shi don ya samu madubin da zai dinga dubawa yana kaucewa abin da ake kira Riba.

·        Duk mai neman albarka cikin kasuwanci ko wata sana’a kuma yake fatan samun dacewar Allah duniya da lahira to ga mafita nan a fanni gujewa riba.

Allah ya saka da alkhairi ya yawaita mana ire-iren wannan mawallafi, albarka Shugaba (S.A.W).

 

Wassalamu Alaikum

Mallam Muhammad Shafi’u Almaliky

Qofar Kabuga

25/06/2025

 

 

 


 

ABUBUWAN DA KE CIKI

Sadaukarwa…………………..…………………. 3

Godoiya…………………………………………. 4

Ta’aliqi………………………………………….. 5

Abubuwan da ke ciki……………………………..7

Gabatarwa …………………………………........ 8

Babi Na Farko:

Cin Riba tanadin yaki ne da Allah da Manzosa….9

Menene Riba? ………………………………..... 10

Rabe Rabeb Riba ……………………………… 11

Hukumcin Riba ……………………………….. 12

Uqubar Masu cin Riba ………………………… 14

Hikimar Haramta Riba ………………………… 21

Babi Na Biyu:

Hukuncin Imam Mālik Game da Riba …………25

Babi Na Uku:

Fatawowin Malaman Musulunci Game da Riba..31

Fatawowin wasu daga Malaman Nigeria ……... 33

Riba A Bankuna……………………………….. 40

Babi Na Huxu:

Wasu daga Nau’o’in kasuwanci Halatttatu……….42

Kammalawa……………………………………. 47

Taqaitawa……………………………………….48

Shawarwari……………………….................................................... …………… 49

Gabatarwa

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin-qai, tsira da Aminci su qara tabbata ga shugaban halitta Annabin Rahama Salallahu Alihi Wasallam.

Bayan haka duba ga yanayin da muke a ciki a halin yanzu na kasancewa tsindum cikin Riba, a kasuwanci, a mu’amalar yau da kullum kamar a wajen bada Bashi, da Bankuna da makamantansu.

Don haka naga dacewar in rubuta wannan littafi dana tattaro daga litattafan Malamai, da Fatawoyin su, da karatuttukansu don daxa fadakarwa, da wayar da kan Al’umma game da Riba, domin wasu da dama suna ma’amala da ita bisa rashin sani ne.

Dafatan Allah yasa wannan littafi ya zamo sila na sanin Menene Riba, da qoqarin ganin an kauce mata, abin da aka gani kuma na kurakurai a ciki dafatan Allah ya yafe mana, wanda kuma akayi daidai Allah ya karva mana yasa a mizani.

Wassalamu Alaikum

Auwal Zakari Muhammad Ayagi

 (Barden Ayagi)

5 ga Zulhijja 1445= 1/6/2025

Kashi Na Farko

(1)

Cin Ruba Tanadin Yaqi Ne Da Allah Da Manzosa

Ubangiji mai girma da daukaka yana fada cikin Alkur’ani mai girma:

يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ ٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَذَرُوا۟ مَا بَقِىَ مِنَ ٱلرِّبَوٰٓا۟ إِن كُنتُم مُّؤْمِنِين (278)َ

فَإِن لَّمْ تَفْعَلُوا۟ فَأْذَنُوا۟ بِحَرْبٍ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَإِن تُبْتُمْ فَلَكُمْ رُءُوسُ أَمْوَٰلِكُمْ لَا تَظْلِمُونَ وَلَا تُظْلَمُون (279)

Ma’ana

 “Yaku Waxanda Kukayi Imani Kuji Tsoron Allah ku bar Abin da yayi saura daga Riba In kun kasance Mumunai[1].

In har baku Aikata ba (Barin cin Ribar) Ina muku Izini da Yaki da Allah da ManzonSa, In kuka Tuba asalin Dukiyarku na gareka baku yi Zalunci ba ba’a Zalince kuba”[2].  

Wannan aya tana tsoratar damu game da Mu’amala da Riba, inda Allah da kansa yake cewa; duk wanda bai bar cin Riba ba, ya na masa izinin yin yaqi dashi da AnnabinSa , kamar yadda yazo a labari cewa: Ranar Alqiyama Ubangiji zai bawa mai cin Riba makami, ya umarce shi da ya yi yaqi da shi, Allah ya kiyaye mu, Allah yace; amma in kuka tuba to sai ku xebi asalin Dukiyarku (Jarinku) ragowar kuxin sai ku rabar, in kukai haka bakuyi zalunci ba kuma ba’a zalunce ku ba.

Menene Riba a Musulunci?

Riba: a larabci na nufin "ƙari" ko "yawaita abu fiye da yadda ya dace", amma a cikin shari’ar Musulunci, Riba tana nufin: "Kowane irin ƙari da aka samu a cikin wata mu'amala, wanda ba a halatta ba, musamman a cikin bashin kudi ko cinikin kayayyaki masu nauin Riba."

Rabe-Raben Riba

Riba ta rabu gida biyu a Musulunci

1.     Riba al-Nasīah

2.     Riba al-Fal

1.     Ribal-Nasīah: Tana nufin: "Ƙarin da ake karɓa a kan bashi saboda jinkirin biya." Wato, mutum ya ba wani bashi (misali: kuɗi ko kaya), amma ya sa ƙarin adadi a cikin bashin idan har lokacin biyan ya wuce.

 Ma’anar Riba al-Nasīah daga Larabci:

•        "Nasīah" na nufin "jinkiri" ko "xage lokaci".

•        Don haka, Riba al-Nasīah ita ce ribar da ke aukuwa, sakamakon xage lokacin biyan bashi tare da ƙarin adadi na abin da aka bayar.

Misali: Ka ba wani bashin (N10,000) zai biya cikin wata ɗaya, amma sai ka ce: "Idan ka jinkirta wato in lokaci yayi baka biya ba, to za ka ƙara (N1,000)." Wannan shi ne mafi shahara kuma mafi tsanani daga cikin Riba. Shi ne Allah da Manzonsa suka ayyana yaƙi da duk wanda ya ke aikata shi a cikin Suratul Baqarah 2: Aya ta 279.

Rabe-Raben Ribal-Nasīah

Ribal-Nasīah: Ribar jinkiri ta rabu kashi biyu Kamar haka:

i)      Riba Mai Ninkawa

ii)   Riba Mai daxuwa don dogon lokaci.

i.                Riba mai ninkawa: Ita ce ake cewa Rubar Jahiliyyah, wannan ita ce ubangiji ya haramtata da nassin Alkur’ani mai girma, inda yake cewa:

يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ لَا تَأْكُلُوا۟ ٱلرِّبَوٰٓا۟ أَضْعَٰفًا مُّضَٰعَفَةً وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمْ تُفْلِحُون  (130)

Ma’ana:

Yaku Wadanda Kukayi Imani Kada Kuci Riba Ninkin-Baninkin, Kuji Tsoron Allah ko kwa Rabauta[3].

Yanda wannan Riba take, Shi ne a baiwa mutum bashi zuwa wani lokaci abin ayyanawa, idan lokacin ya yi bai samu damar biya ba, sai ace dashi ko dai ya biya ko kuma a qara masa kuxin, sannan kuma a qara masa lokacin biyan, haka za’a riqa qara masa kuxin, ana kuma qara masa lokacin biyan, har kuxin su ninninka kansu.

Misali kan wannan shine, kamar bashin da qasashe suke ciyowa bisa yarje-jeniyar zasu biya zuwa Shekarun da aka ayyana, idan lokacin yayi basu biya ba, sai kuxin suyi ta karuwa gwargwadon tsawon lokacin da qasar tayi bata biya ba, sai aga kuxin sun ninka kansu ninkin-ba-ninkin, to wannan itace Ribar da wannan aya take Magana akai.

ii.             Ruba Mai Daxuwa Don Dogon Lokaci; Wannan ita ce Rubar da ake bada bashi da qari don bashin zai xauki dogon lokaci, misali: abada bashin Naira Dubu Goma (N10,000) amma za’a biya Naira dubu Goma sha xaya (N11,000) a tsawon kwanaki ishirin ko makamancin haka.

Ko sayen wani abu da qari kan asalin kuxin sa don xaukan dogon lokaci, misali sayen Sha’ir ko Dabino ko wake, ko masara, ko gero da makamantansu, amma da qarin kuxi in zai kai wani lokaci, misali: ana sayar da Masara Naira Dubu xaya da xari biyar (N1,500) a ko wacce kasuwa, sai abada ita bashi akan Naira dubu xaya da xari shida (N1,600) a watanni biyu, ko biya biyu ga ma’aikata, da makamantansu, to wannan qarin Riba ne.

2.     Ribal-Fal: Wannan shi ne cinikin abubuwa masu kama (irin su Zinariya da Zinariya, Alkama da Alkama, Naira da Naira), amma ɗaya yafi ɗaya nauyi ko ƙima ko yawa.

Misali: A musanya mudu xaya na Alkama da mudu biyu na Alkama, wannan Riba ce a cewar hadisin Manzon Allah .

Zinariya da zinariya, Azurfa da Azurfa, Alkama da Alkama, sha'ir da sha'ir, Tamar da Tamar, Gishiri da Gishiri, sai dai dai-dai da dai-dai, kuma hannu-da-hannu. Duk wanda ya ƙara ko aka ƙara masa, to ya ci riba. [4]

Wato ita Ribal-Fadl tana nufin cinikin Jinsi xaya kamar (Gero da Gero, Dawa da Dawa, Naira da Naira da dai sauransu) amma tare da daxi akan cinikin, kamar asayi Gero kwano xaya, amma sai ace sai an daxa rabin kwano akan kwano dayan, ko sayan sababbin kuxi misali na Naira Dubu biyar amma ace sai ka daxa Naira Dubu xaya akai, da sauransu.

Har ila yau Ribal-Fal na nufin: Ƙarin da ake samu yayin musayar kaya guda biyu iri ɗaya, amma ba daidai suke ba, ko a nauyi ko a ƙima."

Fassarar Ma’anarta:

•       “Fal” a larabci na nufin Qari ko Fifiko.

•       Don haka, Ribal-Fal tana nufin ƙari ko fifiko a cikin musayar kayayyaki waxanda suke iri xaya da juna.

 Misali cikin Sauƙi shine:

§  Idan mutum ya musanya mudu xaya na Alkama da mudu biyu na Alkama, wannan Ribal-Fal ce. (Kamar yanda muka kawao a baya)

§  Ko ya musanya Zinariya mai nauyin Gram 10 da Zinariysa irinta mai nauyin Gram 12, wannan ma Ribal-Fal ce.

Koda kuwa suma kayayyaki iri ɗaya ne, idan ƙimar su ko nauyin su bai daidaita ba, kuma musayar bata yi kai-da-kai ba, to haramun ne.

 Hadisin Manzon Allah :

Zinariya da zinariya, Azurfa da Azurfa, Alkama da Alkama, sha'ir da sha'ir, Tamar da Tamar, Gishiri da Gishiri, sai dai dai-dai da dai-dai, kuma hannu-da-hannu. Duk wanda ya ƙara ko aka ƙara masa, to ya ci riba [5].

Sharuɗɗan Gujewa Riba al-Fal:

1.     Kaya iri ɗaya?

Dole suyi daidai a ƙima (a nauyi ko a yawa).

Dole musayar ta zama kai-da-kai.

 

2.     Kaya iri daban?

Za a iya musanya da ƙari, amma dole ta zama kai-da-kai.

Muhimmancin Saninta:

Riba al-Fal tana faruwa a cikin cinikayya, ba bashin kuɗi kawai ba. Don haka ya ke da matuƙar muhimmanci ga dukkan yan kasuwa da masu canjin kuxaxe ko dillalai da su kula su hankalta da wannan Riba, don su guje mata.

Dalilin Haramcinta:

      Kare mutane daga cuta da zalunci.

      Hana makircin ciniki da ya ke haifar da rashin daidaito.

      Koyar da adalci da gaskiya a mu'amala.

Hukuncin Riba

Ita dai Riba haramun ce, sabo da fadin Ubangiji maxaukakin sarki cikin suratul Bakara Ayata 275 cewa:

وَأَحَلَّ ٱللَّهُ ٱلْبَيْعَ وَحَرَّمَ ٱلرِّبَو

Ma’ana:

Allah Ya Halatta Ciniki Ya Haramta Ruba” [6]

Da fadinsa maxaukakin Sarki cikin Suratu Ali Imram Ayata ta 130:

يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ لَا تَأْكُلُوا۟ ٱلرِّبَوٰٓا۟ أَضْعَٰفًا مُّضَٰعَفَةً  (130)

 “Yaku Wadanda Kukayi Imani Kada Kuci Ruba Ninkin-Baninkin. [7]

Ga kuma fadin Annabi Alaihissalam cewa:

Allah ya tsinewa mai cin Riba, da wakili akan Riba, da masu shaida akan Riba, da marubucin Riba” [8] (As-habu Sinan)

Har ila yau da faxin sa Alaihissalam , cewa:

“Sisi na Riba da Mutum yake cin sa yana sani, shi yafi tsananin Azaba da Zina Talatin da mutum zaiyi. [9]

Da fadin Annabi Alaihissalam cewa:

“Riba kofa Saba’in da Uku ce mafi saukinsu shine mutum ya auri mahaifiyarsa. [10]

Da fadin Annabi Alaihissalam cewa:

Ku nisanci abubuwa bakwai mafiya Ukuba, sai aka ce; Ya Rasulullahi Menene? Sai ya ce: Yin Tarayya da Allah, da Sihiri, da Kashe Ran da Allah ya Haramta, da cin Riba, da cin dukiyar Marayu, da juya baya (Guduwa) Ranar yaki, da yin kazafi ga Mumina Katangaggiya” [11]

Ukubar Masu Cin Riba

Ubangiji madaukakin sarki yafaxa a cikin Suratul Bakara Ayata 275:

ٱلَّذِينَ يَأْكُلُونَ ٱلرِّبَوٰا۟ لَا يَقُومُونَ إِلَّا كَمَا يَقُومُ ٱلَّذِى يَتَخَبَّطُهُ ٱلشَّيْطَٰنُ مِنَ ٱلْمَسِّ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّمَا ٱلْبَيْعُ مِثْلُ ٱلرِّبَوٰا۟ ....

Wadannan da suke cin Riba basa tashi (yayin tashi daga Qaburbura) sai kamar misalin waxanda shaixanu suke bubbugewa (tashin su kamar na masu fyar-fyadiya) da shafa (ta Aljanu) waxannan don cewa su suna cewa shi ciniki kamar Riba ne”[12]

Idan Ubangiji ya tashi mutane a ranar Alqiyama zasu fita suna masu gaggawa, sai masu cin Riba su zasu tashi, suna faduwa kamar masu fyarfyadiya, kasan cewar su ya yin da suke cin Riba, Ubangiji ya na tara Ribar a cukkunansu har ta rinjaye su ranar Alqiyama, duk ya yin da suka tashi sai su faxi, suna son suyi gaggawa kamar sauran mutane amma baza su iya ba.

 

 

 

Hadisan Manzon Allah Da Suke Hani kan Riba

1. Hadisi daga Sahih Muslim

“Annabi ya ce: **Duk wanda ya ci riba, to shi ya yi yaƙi da Allah da Manzonsa.’” [13]

2. Hadisi daga Sahih Bukhari

“Manzon Allah ya ce: ’Riba tana da yawa kamar yadda na gani a cikin abincin.’ [14]

3. Hadisi daga Sahih Muslim

“Duk mai cin riba zai tashi a ranar Qiyama kamar wanda yake mahaukaci.” [15]

4. Hadisi daga Sahih Bukhari

“Annabi ya ce: **Wanda ya ci riba sau ɗaya, to Allah ba zai karɓi sadakarsa ba har sai ya daina riba.’”[16]

5. Hadisi daga Sahih Muslim

“Riba ta fi zina yawa.” [17]

6. Hadisi daga Sunan Abu Dawud

“Annabi ya ce: Riba tana yin laifi iri ɗaya a idanun Allah.’” [18]

7. Hadisi daga Sunan Tirmidhi

“Riba tana hallaka mai yawan ta kamar yadda wuta ke hallaka itace.” [19]

8. Hadisi daga Sahih Muslim

“Annabi ya haramta riba, kuma duk wanda ya ci shi, to shi ya yi yaƙi da Allah da Manzonsa. [20]

9. Hadisi daga Sahih Bukhari

“Wanda ya ci riba a lokacin da aka sani, to ya ci riba, kuma idan ya muta, yana ɗauke da zunubi har abada.[21]

10. Hadisi daga Sunan Abu Dawud

“Allah ya haramta riba, mai cin riba ba zai shiga Aljanna ba har sai ya daina.” [22]

11. "Ku guji riba, koda da ƙanƙantaccen kaso ne."[23]

12. An karvo Hadisi daga Jabir (RA): "Manzon Allah (SAW) ya la’anci mai cin riba, da wanda yake ba da ita, da wanda yake rubuta ta, da kuma shaidunta. Ya ce: dukkansu dai-da-dai suke.” [24]

13. "Riba tana da nau’i saba’in (70) ko fiye, mafi sauƙinta kamar namijin da ya yi zina da mahaifiyarsa." [25]

Waxannan Ayoyi da Hadisai suna nuna girman laifin Riba, da irin Azabar da zata riski masu mu’amala da ita, da kuma mahimmancin barinta.

Hikimar Haramta Riba

Haramcin mu’amala da Riba na xauke da hikima kamar sauran ibadu, an haramta ta ne sabo da jarraba imanin bawa ga biyayya a cikin aikatawar ko hani, sannan yana daga cikin haramcin Riba:

1.     Kiyaye wa a bisa dukiyar Musulmi, don kada yaci dukiya yana mai varna.

2.     Fiskantowar musulmi bisa yaxuwar dukiyar sa cikin hali maxaukaki ba tare da cutar da sauran musulmi ba, a cikin sana’arsa ta Moma ko Kasuwancin ko aikin Gwamnati da sauransu.

3.     Toshe duk wasu hamyoyi masu saka qiyayya ga musulmi, domin qiyayya tsakanin musulmi tana wahalshesu, kuma abar qi ce kuma abar hani ce.

4.     Tseratar da musulmi bisa ga abin da zai kaishi ga halaka, don cin Riba zalunci ne kuma halaka ne.

5.     Bude kofofin biyayya ga musulmi don suyi guzuri sabo da lahira.

Ataqaice: An Haramta Riba ne Domin:

1.  Tana cutar da talaka – Mai bashi ya na cin Riba daga mai buƙata.

2.  Tana haifar da rashin daidaito da zalunci.

3.  Tana hana alheri da albarka.

4.  Tana tayar da husuma tsakanin mutane.

 

 

 

 

 

 

Babi Na Biyu

(2)

Hukuncin Imamu Mālik (RA) Game da Riba

Imam Mālik bn Anas (Allah ya ji ƙansa), wanda shi ne shugaban Mazahabar Malikiyya, ɗaya daga cikin manyan mazahabobin Musulunci guda huɗu, ya rayu daga shekara ta 93 bayan Hijira zuwa 179H, Imamu Mālik yana ɗaya daga cikin manyan malaman hadisi da fikihu da suka yi tasiri a tarihi. An haife shi a Madinah a shekara ta 93 bayan Hijra, cikin gida mai bin addini da ilimi. Mahaifinsa Anas da kakanninsa sun kasance mutane masu tsantseni da kula da ilimi.

Tun yana ƙarami ya zauna cikin Masallacin Manzon Allah (SAW), inda ya koyi hadisi daga manyan malamai fiye da 900, ciki har da Nafi’u (bawan ɗan Umar), da Ibn Shihab az-Zuhri, da Yahyā ibn Saīd al-Ansari, da Rabiatu ar-Rayi.

A cikin ilimin Hadisi shi ne marubucin Al-Muwaṭṭa, ɗaya daga mafi inganci da tsofaffin littattafan hadisi, wanda ya shahara saboda tsantsar zaɓen hadisan da ya tattara.

Imamu Mālik ya yi rayuwa cikin gaskiya da tsoro ga Allah. Ba ya bayar da fatawa sai ya tabbatar da abin da ya fito daga Alƙur’ani, Sunnah, ko abin da Ahlul Madinah suka aikata. Ya shahara da cewa: “Na ce ban sani ba fiye da yadda na ce na sani.”

Ya rasu a shekara ta 179H a Madinah, aka binne shi a Jannatul Baqi’a.

Imam Malik yana daga cikin malamai masu tsauraran ra’ayi akan Riba, musamman Riba a cikin mu'amala da ciniki (Riba al-buyu'u), wanda aka fi samun sa a harkar kasuwanci da musayar kaya.

Hukuncinsa

1.     Riba Haramtacciya ce gaba ɗaya

Imam Mālik ya na ganin duk wani nau'in Riba wato Riba Al-Fadhl da Riba Al-Nasia, haramun ne kuma babban zunubi ne. Ya jingina da nassosin Qur’ani da Hadisi kamar yadda na kawo a baya.

2.     Musayar Kayayyaki Masu nau’in Riba

Imam Mālik ya karɓi cewa musayar abubuwan da suka yi kama (irin su zinari da zinari, ko Alkama da Alkama) dole ne ta kasance:

•   Kai-da-kai wato (Hannu-da-Hannu) wato (yadan –bi-yadan)

•   Adalci cikin nauyi da kuma ƙima

Idan aka savawa hakan, to an shiga Riba, kuma haramun ne.

3.     Duk wata hanya da aka bi don yaudarar tsarin Allah ta hanyar Riba, shi ma haramun ne

Imam Mālik ya yi gargadi daga duk wata hanya da mutane ke amfani da ita don su guje wa hukuncin Riba ta hanyar "makaranta" da "dabara" ya na cewa abin da aka yi da nufin Riba, to haramun ne, koda kuwa ta hanyar dabara ce.

4.     Fatwarsa akan mu’amalar da take ƙunshe da riba a ɓoye (Riba Al-Khafiyyah)

Imam Mālik ya na da tsaurin raayi kan muamaloli da a zahiri kamar ba Riba ba ne, amma a gaskiya Riba ce cikin dabara. Irin waɗannan mu'amaloli ya haramta su bisa ƙaidar:

“Saddan li-dh-dhara’i” – wato toshe hanyar da ke kai wa ga haram.

Misalai daga Al-Muwaxxa ta Imam Mālik:

A cikin "Al-Muwaxxa", Imam Mālik ya kawo ruwayoyi da fatawowi daga Sahabbai da Tabiai da suka haramta riba da tsananin nuni da illarta a cikin al'umma.

Misali:

“Duk wanda ya karɓi Riba ko ya ba da ita ko ya rubuta ta ko ya kasance shaida a kanta, ya shiga cikin haramun." [26]

Hukuncinsa a Taqaice:

•   Riba haramun ce ko da ƙarama ce.

•   Ba a halatta ciniki da ya ƙunshi riba ko ɓoyayyen riba.

•   Hanyoyin dabara don kaucewa riba haramun ne.

•   Zina da mahaifiya ya fi sauƙi fiye da riba, idan aka dubi hadisin da Imam Mālik ya karɓa.

Wasu Bayanai Daga Littafin Al-Muwaxxa ta Imam Mālik Da Suka Shafi Riba:

1. Riba a zamanin Jahiliyya

Imam Mālik ya ruwaito daga Zayd ibn Aslam cewa:

"Riba a zamanin Jahiliyya ita ce: mutum yana ba wani bashi na wani lokaci. Idan lokacin ya cika, sai ya ce masa: 'Za ka biya ko ka ƙara mini?' Idan ya biya, sai ya karɓa; idan kuma bai biya ba, sai ya ƙara masa a cikin bashin kuma ya tsawaita masa lokaci."[27] Al-Muwaṭṭaʼ, Kitāb al-Buyuʻ

Wannan ya na nuna cewa Riba Al-Nasīʼa (ƙarin kuɗi saboda Jinkirin biyan bashi) an haramta ta a Musulunci.

 

2. Musayar Zinariya da Azurfa

Imam Mālik ya ruwaito daga Al-Qāsim Ibn Muammad cewa:

"Umar Ibn Al-Khaṭṭāb ya ce: 'Dīnār da Dīnār, Dirham da Dirham, Sa'a da Sa'a. Abin da za a karɓa daga baya ba za a sayar da shi da abin da ke hannu ba.” [28] Al-Muwaṭṭaʼ, Kitāb al-Buyuʻu

Wannan ya na nuni da cewa musayar abubuwa masu nau'in Riba (kamar Zinariya da Azurfa) dole ne su kasance kai-da-kai kuma daidai gwargwado.

3. Riba a cikin Ciniki

Imam Mālik ya ce: "Abin da ba mu yarda da shi ba, kuma babu sabani a tsakaninmu, shi ne: mutum ya ba wani bashi na wani lokaci, sannan mai bashi ya rage masa adadin bashin, amma ya karɓi kuɗin kafin lokacin. A gare mu, wannan kamar wanda ya jinkirta biyan bashinsa ne, sannan mai ba da bashin ya ƙara masa bashin. Wannan ba komai ba ne face Riba, babu shakka a ciki."[29]

Wannan yana nuna cewa duk wata dabara da ake amfani da ita don samun Riba ta hanyar ciniki ko bashi, haramun ce.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Babi Na Uku

(3)

Fatawowin Malaman Musulunci Game da Riba

Ga wasu daga cikin fitattun malamai da fatawarsu game da riba:

1. Sheikh Ibn Baz (Rahimahullah) – Saudiya

Fatawa: Riba haramun ce, babbar zunubi ce, kuma duk wata fa'ida ko ƙari da ake samu daga bashin kuɗi to riba ce.

Ya ce: "Babu bambanci tsakanin karamin riba da babban riba. Dukkan su haramun ne[30]."

2. Sheikh Muhammad Salih Al-Uthaymeen (Rahimahullah)

Fatawa: Ya bayyana cewa duk wata mu’amala da ke da ƙarin kudi bisa wani jinkiri ko lokaci, to wannan Riba ce. Ya kuma jaddada da cewa: "Ko da mutumin yana da niyyar taimako ne, muddin ya ce za a dawo da bashin da ƙari – to wannan haramun ne." Malamin yanuna cewa in har za’a bada bashi da sunan taimako. In har da qari aciki to wannan Haramunne.[31]

3. Sheikh Dr. Yusuf Al-Qaradawi (Rahimahullah)

Fatawa: Ya bayyana Riba a matsayin babbar hanyar da ke halakar da tattalin arzikin al’umma, kuma ya ce: "Riba ba wai kawai haramun ce bane, amma tana da illoli da dama ga al'umma, ana ƙara talauci, hana taimako, da karya jinkai[32]."

4. Malaman Azhar – Masar

Malaman jami'ar Azhar da majalisar fatawa ta Masar sun haɗu kan cewa Riba haramun ce – komai ƙanƙantarta. Sun ce: "Riba tana daga cikin abin da Qur’ani ya bayyana a fili cewa haramun ne, kuma wanda ya ci gaba da cin Riba bayan ya samu bayani, Allah zai yi masa yaƙi. [33]" (Duba: Suratul Baqara: 278-279)

 

5. Sheikh Ibrahim Inyass (RA) – Senegal

Fitaccen jagoran Tijjaniyya, Sheikh Ibrahim Inyass, yana da rubuce-rubuce da kalamai kan haramcin riba:

Ya ce: "Riba tana haifar da rugujewar arziki da lalata zamantakewa, kuma Musulmi ya wajaba ya kauce mata gaba ɗaya."

Ya ƙarfafa mutane su dogara ga halal, su yi kasuwanci da gaskiya, su guji cin amana da riba[34].

Fatawowin Wasu Daga Malaman Najeriya

1.   Sheikh Ja'afar Mahmud Adam (Rahimahullah)

A cikin karatuttukansa, Sheikh Ja'afar ya bayyana cewa duk wata mu'amala da ke da fa'ida ko ƙari akan bashin kuɗi – ko da sun canza sunanta, Riba ce.

Ya ce: "Bari mu sani cewa Riba ba sai mutum ya je banki bane. Idan ka bai wa mutum kuxi ya ce zai dawo da shi da ƙari wannan Riba ce."

Ya bayyana kuma a cikin wasu darussan cewa:

"Duk wani bashi da ƙari, Riba ce. Ko da mutum ya ce 'na baka dubu, ka dawo da dubu da ɗari' – wannan Riba ce."

Ya ƙara da cewa: "Riba tana da matuƙar haɗari a addinin Musulunci. Allah da Manzonsa sun yi wa mai cin riba tayin yaƙi. [35]"

Dalili: Suratul Baqarah, aya ta 278–279.

2. Sheikh Dahiru Usman Bauchi (Rahimahullah)

A cikin wa’azinsa, ya bayyana cewa:

"Riba tana daga cikin babbar haramun da take haddasa fushin Allah. Idan mutum yana da Riba a asusun sa – ya fitar da ita ba da niyyar lada ba, domin haramun ce."

Ya kara da cewa: "Cin Riba ko mu’amala da ita ba abun barin Musulmi ba ne. [36]"

 

3. Sheikh Qaribullahi Nasiru Kabara (Kano) – Jagoran Qadiriyya

A wata fassara da ya yi, ya bayyana cewa:

"Wajibi ne Musulmi ya tsarkake kasuwancinsa daga duk wata hanyar haram. Riba tana hana albarka kuma tana jawo halakar arziki."

Ya kuma ce: "Ma’aikata a bankunan Riba su nemi halal domin kada su shiga cikin la’anar Manzon Allah. [37]"

4. Sheikh Muhammad Sanusi Kerau (Kaduna) – Malamin Darikar Tijjaniyya

"Riba yana da ruɗi, amma mai cin riba yana haddasa halakar kansa da al’ummarsa. Yin kasuwanci cikin gaskiya da tausayi shi ne hanya mafi dacewa da Musulunci. [38]"

5. Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Gumi (Kaduna)

Ya bayyana cewa: "Riba a bankuna haramun ce, domin suna ba da kudi da ƙari ba tare da wata halal muamala ba. Wannan shine abin da aka haramta a Qurani."

Amma ya yi bayani: a wasu lokuta na matsananci (necessity) ana iya buɗe asusu na banki ko karɓar albashi ta banki, amma ba da riba ko karɓar riba haramun ne[39].

6. Sheikh Kabiru Gombe

"Riba na daga cikin laifuffuka masu girma. Kowa yana neman karin kudi, amma idan ya wuce hanya – ya shiga cikin riba – ya shiga cikin haddi."

Ya fadi cewa ko da aka sauya sunan mu'amala, misali a kira ta “service charge” ko “interest,” idan da ƙari ne akan bashi riba ce[40].

7. Sheikh Sani Yahaya Jingir (Jos)

"Ko da gwamnati ce ko kamfani ne ya ce zai ba da bashin da ribar kashi 5%, hakan haramun ne. Domin bai banbanta da abin da aka hana ba."

Ya ce, “Wanda ke karbar riba da wanda ke bayarwa da wanda ke rubutawa da wanda ke shaida – duka Allah ya la’anta su kamar yadda Hadisi ya nuna. [41]

Manyan Malamai da dama suna jaddada cewa:

•        Bankin da ke bayar da riba yana haramta duk wata fa’ida da Musulmi zai samu ta hakan.

•        Wanda ke da kuɗi a irin wannan banki, ya nemi hanyar halal don cirewa, ba tare da karɓar ribar ba.

Duk malamai – ko na Darika ne ko na Izala ko Salafiyya – sun amince da cewa Riba babbar haramun ce, kuma tana da illoli masu yawa a rayuwar Musulmi da al’umma gaba ɗaya. Wannan ya dogara da nassoshin Qur’ani da Hadisi, da kuma ijma’in malamai.

Ka'idodin Gabaɗaya na Malamai:

1.       Riba haramun ce da ƙarfi ba kawai makruh ba ce.

2.       Fa'ida akan bashi na kuɗi ko kayayyaki riba ce – ko da da yardar mai karɓar bashi ne.

3.       Babu bambanci tsakanin riba ta banki da riba ta mutane kai-tsaye.

4.       Riba ba za ta halatta ba saboda bukata – sai dai in akwai matsanancin hali (ƙarancin abinci ko rayuwa).

Riba a Bankuna

Riba a Bankuna (Interest a Turance), na nufin ƙarin kuɗi da ake bayarwa ko karɓa bisa wani lokaci da aka amince da shi akan kuɗin da aka ajiye ko aro.

Ga cikakken bayani:

1. Interest a matsayin Riba da Banki ke bayarwa:

Idan ka ajiye kuɗinka a banki (misali a asusun ajiya), bankin zai iya ba ka ƙarin kuɗi a kowane wata ko shekara bisa adadin da ka ajiye. Wannan ƙarin ana kiransa interest. Misali:

•        Ka ajiye 100,000

•        Banki ya ce zai ba ka 5% interest a shekara

•        Bayan shekara ɗaya, za ka samu 105,000 (ƙarin 5,000 ribar da banki ya ba ka)

2. Interest a matsayin Riba da Banki ke karɓa:

Idan ka ciwo bashi daga banki, bankin zai ce dole ka biya da ƙari akan kuɗin da ka aro. Wannan ƙarin shi ake kira interest. Misali:

•        Ka aro 100,000

•        Banki ya ce interest ɗin bashin ya kai 10%

•        Bayan shekara, dole ka biya 110,000 (wato asalin bashin da ƙarin 10,000)

A Taƙaice:

Ka ajiye kuɗi        Banki ya ba ka riba (interest)

Ka ciwo bashi       Kai ne za ka biya riba (interest)

A Mahangar Musulunci:

A cikin Musulunci, riba (interest) ana kallonta a matsayin haramun, saboda tana da nasaba da cin hanci da zalunci a ciniki. Wannan ya fito a cikin Alkur’ani da Hadisai da dama.

 

Babi Na Hudu

(4)

Wasu daga Nau’o’in kasuwanci Halatttatu

1. Muḍāraba

Ma’ana:
Mu
ḍāraba ita ce yarjejeniyar kasuwanci da ake yi tsakanin mai jari (rabbul-māl) da mai aiki (muḍārib), inda mai jari ya ba da kuɗi, mai aiki kuma ya yi kasuwanci da su, riba su raba bisa yarjejeniya.

Yadda take aiki:

·         Mai jari shi ne yake samar da kuɗi gaba ɗaya.

·         Mai aiki shi ne yake bibiyar kasuwanci, saye-da-sayarwa, ko zuba jari.

·         Idan an sami riba: a raba bisa kaso da aka yi yarjejeniya tun farko (misali 60% ga mai jari, 40% ga mai aiki).

·         Idan asara ta samu: mai jari ne ke ɗaukar asarar, mai aiki asarar tasa ce wahalar da ya yi ba ya karɓar komai.

Sharudda:
A fayyace kaso na riba tun farko.
Mai aiki ba shi da garanti akan riba.
Ba a haɗa kasuwar halal da haram.
A amince akan nau’in kasuwanci.

Dalilin halaccin Muḍāraba:
An yi ta tun zamanin Annabi SAW, shi kansa ya yi wa Khadija ciniki cikin irin wannan tsarin.

2. Murābaa

Ma’ana:
Murabaha ita ce saye-da-sayarwa da bayyana tsadar jari da riba ta halal da mai siyarwa ya amince ya kar
ɓa.

A tsarin bankin Islama, murabaha ita ce lokacin da:

·         Abokin ciniki ya nemi kaya,

·         Banki ko mai jari ya saya da kansa,

·         Sai ya sayar masa da tsadar da ya saya da ƙarin riba da aka yi yarjejeniya, kuma mafi yawanci a biya a hankali.

Misali:
Kana son siyan mota.
Banki ya saya da
3,000,000
Sai ya sayar maka da ita da
3,500,000 a biyan wata-wata.
An bayyana jari da
ƙarin riba (margin profit), ba laifi idan an bi tsari na sharia.

Sharudda:
Banki ya mallaki kayan kafin ya sayar.
A bayyana jari da ƙarin riba ba tare da ɓoye komai ba.
Biyan bashin ya kasance na halal ba tare da tara tara ba (late payment interest haram ne).

3. Mushāraka

Ma’ana:
Musharaka ce ha
ɗin gwiwa tsakanin mutane biyu ko fiye wajen:

·         zuba jari

·         aiki

·         raba riba

·         raba asara

Kowa yana da kaso a jari, kuma riba a raba bisa yarjejeniya, amma asara a raba bisa kaso na jari.

Nau’o’i:

1. Musharaka al-Aqd

Haɗin gwiwa na yau da kullum, kowa ya kawo jari ko baiwa da aiki.

2. Musharaka Mutanaqisa (Diminishing Musharaka)

Ana amfani da ita a ginin gida ko manyan ayyuka:

·         Kungiya ko banki su yi gini tare da mutum.

·         Ɗan lokaci-lokaci mutum yana biyan wani ɓangare har sai ya mallaki sabon ginin kafaɗa ɗaya.

Misali:
Ka kawo 40%, banki 60%.
Riba a raba bisa yarjejeniyar ku.
Idan asara, kowa ya
ɗauki rabon da ya yi dai-dai da jarinsa.

4. Qarul-asana – Bashi na alheri

Ma’ana:
Wannan shi ne bashi da ake bayarwa a Musulunci ba tare da wani
ƙarin riba ba, ko da kuwa ƙanƙanin ƙari ne.

Manufarsa:

·         Taimako

·         Jinƙai

·         Gujewa matsalar kuɗi da wahala

Halaye:
Ba a ƙara komai akan kuɗin da aka bayar.
Ba a ɗora tara idan mai bashi ya yi jinkiri, sai dai idan lalaci ne.
An so a yi kyauta ko sassauci idan mai bashi ya tsinci kansa cikin wahala.
Musulmi yana da lada mai girma idan ya bayar da Qarzul-Hasana.

Dalili daga Alkur’ani:
“Wanda ya ba Allah bashi na alheri, to zai ninka masa.” – Surat Al-Baqarah 245

Kammalawa

A ƙarshe, wannan littafi ya yi ƙoƙarin fayyace maanar riba, nau’o’inta, da yadda malamai na fikihu suka yi ittifaqi a kan haramcinta bisa hujjojin Alƙurani da sahihan hadisan Manzon Allah (SAW). Riba tana daga cikin manyan laifuka da ke lalata tattalin arziki, rushe zumunci, da jefa alumma cikin talauci da rashin adalci. Wannan ya sa Shari’ar Musulunci ta yi tsaurin hani a kanta, domin kare rayuwar mutane, tsaron dukiya, da tabbatar da musayar amana a cikin al’umma.

Hujjojin da suka fito daga Alƙurani sun yi nuni kai tsaye da cewa riba tana kawo yaqi daga Allah da Manzonsa, tare da gargaɗi mai tsanani ga masu mu’amala da ita. Haka hadisai sahihai sun tabbatar da la’antar mai cin riba, mai bayarwa, wanda ya rubuta, da wanda ya shaida, dukkansu ana ɗaukar su a matsayin masu haɗaka a wannan laifi. Wannan ya nuna cewa Musulunci ba wai kawai ya haramta riba ba ne, har ma ya rufe duk wata ƙofa da za ta kai ga aikata ta.

Saboda haka, musulmi ya kamata ya nisanci duk wata mu’amala da ta ƙunshi riba, yana neman halal cikin sanaoi, kasuwanci, da musayar kuɗi. Samun halal ko da kaɗan ce tafi arzikin da aka samu ta hanyar riba wanda arzikin ya ƙunsa laana da fushin Ubangiji. Sharia ta buɗe hanyoyi masu tsabta irin su mudaraba, murabaha, musharaka, da qarzun hasana, domin tabbatar da cika bukatun al’umma ba tare da cin zarafi ba.

Allah Ya sa wannan aiki ya zama hujja mai kyau ga marubuci da mai karatu, Ya sa mu daga cikin waxanda ke bin halal su guji haram, Ya kuma kare mu daga jarabar riba a dukkan siffofinta. Ameen.

Takaitawa

Wannan littafi ya yi bayani dalla-dalla game da riba: ma’anarta, nau’o’inta, da yadda malamai suka yi ittifaqi a kan haramcinta. An kawo hujjoji daga Alƙurani da hadisai waɗanda suka yi tsaurin hani ga mai cin riba da mai bayarwa, tare da yin nuni da illolinta ga tattalin arziki da rayuwar al’umma. Littafin ya kuma nuna hanyoyin mu’amala na halal da Musulunci ya shar’anta domin kare al’umma daga zalunci, ya tabbatar da adalci da amana a cikin harkokin kuɗi.

 

Shawarwari

1. Nisantar Mu’amalar Riba: Musulmai su kauce wa duk wata hulɗa da ta ƙunshi riba, ko da tana ɓoye, saboda tsananin haramcinta a Shari’a.

2. Neman Halal a Harkokin Kasuwanci: Ya dace al’umma su mai da hankali kan hanyoyin da Shari’a ta halatta kamar mudaraba, musaraka, murabaha, da qarzun hasana.

3. Ƙarin Ilimi: Ana bada shawara ga masu kasuwanci, ɗalibai, da malamai su zurfafa karatu kan fikihun mu’amalah domin fahimtar bambanci tsakanin riba da halal mu’amala.

4. Tattaunawa da Malamai: Idan mutum ya shiga mu’amala mai rikitarwa, ya kamata ya tuntuɓi malaman Shari’a domin samun hukunci mai tsafta.

5. Ƙarfafa Bankunan Islama: Akwai buƙatar goyon bayan bankunan Islama domin samar da zaɓuɓɓuka na halal ga al’umma, su kauce wa tsarin ribace-ribace.

6. Gyaran Al’umma: Masu wa’azi da malamai su ci gaba da wayar da kai kan illolin riba, domin kare al’umma daga shiga hanyoyin da za su cutar da su a nan duniya da lahira.



[1] - Suratul-Al-Baqara aya ta 278

[2] - Suratul Baqata ayata 279

[3] - Suratu Ali Imran ayata 130

[4] - Sahih Muslim, Hadisi mai lamba 1587

[5] - Sahih Muslim, Hadisi mai lamba 1587

[6] - Suratul Bakara Ayata 275

[7] - Suratul Bakara Ayata 130

[8] - As-habu Sinan  

[9] - Ahmad da Hakim

[10] - Hakim

[11] - Buhari da Muslim

[12] - Suratul Baqara Ayata 275

[13] - •    Sahih Muslim, Hadisi 1598

[14] - •    Sahih Bukhari, Kitab al-Buyu, Hadisi 2084

[15] - •    Sahih Muslim, Hadisi 1599

[16] - •    Sahih Bukhari, Hadisi 2075

[17] - •    Sahih Muslim, Hadisi 1597

[18] - •    Abu Dawud, Hadisi 3584

[19] - •    Tirmidhi, Hadisi 1287, Hadisi Sahih

[20] - •    Sahih Muslim, Hadisi 1598

[21] - Sahih Bukhari, Hadisi 2085

[22] - Abu Dawud, Hadisi 3582

[23] - Sahih Muslim

[24] - Sahih Muslim

[25] - Tirmizi Ibn Mahja Sahihul Na’ani

[26] - Muwaxxa Al-Malik

[27] - Al-Muwaxxa Kitabul Biyu’u

[28] - Al-Muwaxxa Kitabul Biyu’u

[29] - Al-Muwaxxa Kitabul Biyu’u

[30] - Shaik Ibn Baz RA

[31] - Sheik Muhammad Salih Al-Uthaymin RA

[32] - Sheik Dr. Yusuf Al-Karadawi RA

[33] - Malaman Jami’ar Azhar dake Masar

[34] - Sheik Ibrahim Nyas RA

[35] - Mallam Ja’afar Mahmud Adam cikin Karatuttukan

[36] - Mallam Xahiru Uthman Bauchi cikin Karatuttukan

[37] - Mallam Qaribulla Sheik Nasiru Kabara cikin Karatuttukansa

[38] - Mallam Muhammad Sunusi Qerau cikin Karatuttukansa

[39] - Mallam Dr. Ahmad Gumi cikin Karatuttukansa

[40] - Mallam Kabiru Gombe cikin Karatuttukansa

[41] - Mallam Sani Yahaya Jingir cikin Karatuttukan