GULMA
DA ILLOLINTA
Da sunan
Allah mai yawan Rahama Mai yawan jinkai, gaisuwa da yabo su kara tabbata ga
manzon Allah (SAW) da Alayansa da sahabbansa baki daya.
Bayan haka na yi kokari gabatar da wannan
takaitaccen bayani ne sabo da ganin yanda yan uwa mata da maza muke cikin
wannan mummunan dabi'a ta gulma, a inda ada mata kadai akasani da gulma amma
yanzu har mazanma suna neman su kere matan, dafatan Allah zai amfanar damu mu
gane mu kauce mata.
MENENE GULMA?
Gulma a shar'ance tana nufin mutum ya dauki maganar
wani ya kaiwa wani da nufin hada husuma a tsakaninsu, ko cutarwa, amma idan da
nufin alhairi aka kai babu laifi.
HUKUMCIN GULMA A MUSULCI
Gulma haramun ce da nassin Alkur'ani da Hadisan
Shugaba Alaihissalam, kuma dayace daga cikin manyan zunubai.
Daga cikin dalilai na haramcin Gulma akwai fadi
Allah (SWT) cikin littafinsa mai tsarki cikin suratulKalam Aya ta 11 cewa:
"MAI YAWAN AIBATA MUTANE, MAI YAWAN GULMA (TSAKANIN MUTANE)" Har
iala yau da fadinsa "SHIN DAYAN KU YANA SON YA RIKA CIN NAMAN
DAN'UWANSA ALHALI YANA MUSHE? TO KUN KYAMACI HAKA...(HUJRAAT:12)
Sannan kuma Manzo (SAW) yce: "DUKKAN
MUTUM ANNAMIMI (MAI GULMA, MAIHADA HUSUMA DA TSAKANIN MUTANE BAZAI SHIGA ALJANNA BA" ( Buhari Da Muslim)
Wata
rana manzon Rahama ya wuce wasu Kaburbura Biyu, sai yace ana yiwa na cikin
Kaburburan azaba a halin yanzu, kuma su awajensu ba akan wani babban laifi
bane, lokacin da suke aikata laifukan sun ganin ba manya bane, daya daga cikin
su ya kasanci in yayi Fitsari baya tsarkaka, wato idan ya gama fitsari baya bari
ya dige gaba dayansa sai ya rika a jikin sa ba tare da rashin lafya ko wani
uzuri ba, na biyun kuma ya kasance mai yawan yawo tsakanin mutane da
annamimanci" (Buhari da Muslim)
Sannan
Manzo Alaihissalam yace: " Zaka samu daga cikin mafiya sharri a cikin mutane,
sune masu fuska biyu wadanda zasu zowa wadannan mutane da wata fuska sannan su
ewa wadannan da wata fuskar" (Buhari da Muslim ne suka rawaito)
Har
ila yanzo Manzo yace: "Dukkan wanda ya kasance yana da harshe biyu a
gidan duniya (wato Magulmaci) to Allah zai sanya masa harshe biyu na wuta a
ranar Alkiyama" (Abu dawud ne ya rawaito:4873)
Sannan
Ka'ab yana cewa: "Ku tsoraci annamimanci (wato Gima) domin ma'abocinta
baya hutawa daga azabar Kabari.
Mansur ya rawaito daga Mujahd dangane da matar
abi Lahab wadda asalin sunanta Arwa, sannan ana mata Alkunya da Ummu Jamil inda
allah Madaukakin sarki ya ke cewa: "Da matarsa ina nufin magulmaciya"
(Suratul Madas aya ta 4)
wannan mata Mummunace mai ido daya amma ba'abin
da ta ke yi da shi sai zunden Manzon Allah(SAW) da tsara baitocin waka don keta
alfarmar sa.
HALAYEN MAGABATA A
LOKACIN DA AKA JE MUSU DA GULMA
An rawaito cewa wata rana wani mutum ya je wajen
Umar Ibn Abdul'aziz ya kai masa Gulmar wani mutum, sai umar Ibn Abdul'aziz yace
masa: Yakai wannan mutum idan naga dama zan duba lamarinka, idan ka kasance mai
gaskiya, to kana daga cikin wanda Allah yake cewa: "Idan fasiki yazo muku
da wani zance to ku yi binciki.." (Hujurat:6 ). Idan kuma ka kasance
makryaci, to kana daga cikin wadanda Allah yake cewa: " Mai yawan aibata
Mutane, mai yada Gulma" (tsakanin mutane) Kalam: 11.
Inaga dama in yafe maka, sai wannan mutum yace:
Kayafe min ya sarkin muminai, bazan sake aikata haka ba.
Wani mutum yazo waje aliyu dan Hussain (RTA) yace
masa: Wane ya zageka, kuma yace kaza da kaza, sai yace: zanje wajensa, sai suka
tafi wajensa tare da tsammanin zaije ne ya kare kansa< lokacin da suka isa
wurinsa, sai yace: Ya dan'uwa na idan abin da ka fada tare dani gaskiyane, to
allah ya gafarta mini, idan kuma abin da kafada gane dani ba gaskiya bane , to
allah ya gafarta maka.
ABN DA AKE SO KA AIKATA LOKACIN DA A KA ZO MAKA
DA GULMA
A kwai abubuwa da dama da akeso ka aikata lokacin
da wani ya zo maka da Gulma, kadan daga ciki sune:
1.
Kada ka
gaskata labarin da aka zo maka, domin wanda yazo da labarin ya zama Annmimi,
fasiki, kuma mai mayar da alheri.
2. Ka hana wanda ya kawo maka Gulmar ci gaba da
Gulmar, kuma kayi masa nasiha sannan ka kyamaci aikata hakan.
3. Ka nuna masa kaji haushin sa domin Allah, don
Allah yana fushi da aikinsa, kuma yin fushi domin allah wajibi ne.
4. kada kayi mummunar zato
dangane ga wanda aka kawo maka gulmarsa, donin Allah (SWT): KU NI SANCI MAFI
YAWA DAGA CIKN ZATO.." (Hujurat:12)
5. kada mutun yace zai yi
bincike don gano abin da aka fada masa
karya ce gaskiya ne, domin Allah(SWT) tace: "Kuma kada kuyi
bincike.." (Hujurat:12).
6. Kada mutun yaci gaba da
labartarwa da wasu abin da aka kawo masa na gulma, domin shima sai ya koma
matsayin wanda yazo masa da gulman.
Wadannan sune kadan daga bayanai akan Gulwa, da fatan Allah
ya karemu daga aikata wannana mummunan dabi'a, ya shiryemu da dukkan musulmi
baki daya.
Wassalamu alaikum warahamatullah.