Saturday, 5 April 2025

AL-USMAIYYUN (Littafi Na Daya) 2002


AL-USMANIYYUN

Littafin Daya Qunshi Tarihi Da Zuriyar

Malam Shehu Usman Hussaini Ayagi

Xan Asalin Garin Kumurya Dake

Qaramar Hukumar Bunkure Jihar Kano

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Wanda ya rubuta

 

AUWALU ZAKARIYYA MUHAMMAD USMAN AYAGI

 

 

 

 

Haqqin Mallaka (M) Al-Azmiyyah Ventures

 

 

An fara bugu wa 2002/1423

 

 

Sadaukarwa

Na sadaukar da wannan Littafi ga iyayena Alhaji Zakari Muhammad Usman Ayagi (Alh Amasha) da Mahaifiyata Hajiya Rakiya Usaini Lawan (Inna) Allah ya qara mata Lafiya. Da kuma xaukacin Musulmi musamman masu sada Zumunchi da umarni da sadashi

 

 

TSARA RUBUTU A COMPUTER

Beta Bussiness Centre, Kabuga

B.U.K Road, Kano

 

 

BUGAWA

Al-Azmiyyah Printers A Division of Al-Azmiyyah Ventures, Kogar Kabuga Quarters

POBox 13808 Kano.

E-mail: alazmiyya@gmail.com

 

Ta’aliqi

Ina godiya ga Allah Tabaraka wa Ta'ala, daya wajabta sadar da zumunci da kuma bada lada mai xibbin yawa ga duk wanda ya sadardabshi, da kuma yabo da salati ga Shugabamınu Annabi Muhammad (SAW) da Sahabbansa da 'ya'yan Gidansa.

Bayan Haka haqiqa wannan littafi ya qunshi tarihin Malam Usman Kumurya, Dan Malam Husaini Dan Uwan Malam Hasan. Dukkansu haifaffun Kumurya ne, domin shi Malam Usman wanda aka fi sani da Malam Shchu, wanda dalilin haka ne ma, ake cewa da mahaifina Malam ldi xan Shchu, Mahaifinsa an haife sune su biyu kamar yadda Tarihi ya nuna, wato 'Yan Tagwayc, sai dai wanda ya haifi Mallam Usman Kumurya shi ne Malam Husaini Kumurya.

Hakika wannan tunani da wannan xa namu mai albarka yayi na binciko asalin mu, (wato Auwalu Zakari Muhd Usman Ayagi) da tushemu yana da kyau kwarai, Saboda Malaman Tarihi sun ce "Tarihi Mudubi nc na Al'ummar da suka shige" Ta inda za'a san irin rayuwar da suka yi.

To hakika mu sai muce san barka domin rayuwar magabatanmu rayuwa ce ta ilimi da cinikayya: kuma mu 'yan-Kano ne lyaye da Kakanninmu.

Saboda da haka wannan littafi ya na da kyau, ya kuma kunshi haqiqanin Zuriyar Malam Usman Kumurya 'ya'yansa da jikokinsa na wajen 'yaya mata da na wajan 'ya'ya maza da 'yayansu, da kuma suma 'yayansu.

A qarshe nake cewa Allah yayi wa zuriyar Malam Usman Kumurya Albarka, ya kuma haxa kansu, Amin summa Amin.

Husaini Idi Dan-Shehu Ayagi

Shugaban Makarantar Primary Ta

Danlami Ibrahim Islamiyya Ayagi

09-08-2002

 


 

Godiya

Da sunan Allah mai yawan Rahama mai yawan Jinkai.Tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad (SAW) da Alayensa da Sahabbansa baki daya.

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin Talikai, da ya bani dama harna rubuta wannan littafi.

Bayan godiya ga Allah da salati ga Annabi (SAW) dole ne iny godiya ga wasu mutane saboda irin kwarin gwiwa. da shawarwari da suka bani wajen wallafa wannan littafi da kuma tarihai da suka bani da kuma sunayen da suka taimakamin wajen zakulowa.

Da farko dole ne in mika cikakkiyar godiya ta ga babbar jikar Mal. Usman wato Hajiya Jummai saboda irin tarihan da ta rinqa bani, da shawarwari da dama. Sannan ina mika godiya ta ga mahaifina Alh. Zakari Muhd (Amasha) da mahaifiyata suma saboda shawarwarin da suka bani.

Har ilayau ina mika godiya ga mutanen kul-kul, Iyalan Baba Uba Musamman dansa Ibrahim, sannan da mutancn Zariya kamar Baba Sani, Ladi, Shchu da sauransu, sannan godiya ta musamman ga Baba Yalwa da Hassan da Husaini da Safiya da Haj. Karama, da Lami, da kuma gabaxayan mutancn Fagge kamar su Ladidi, Zulaihat da Maimuna, da sauransu. Kai dama wanda duk ya taimaka da farin-cikinsa ko shawararsa, da duk abokaina da Malamaina da dalibaina da suka taimaka wajen fitowar wannan Littafi.

Daga karshe ina mika cikakkiyar godiya dayabo da jinjina ga Gwarzo na kuma Masani akan aikin sa Abdulkadir Ali Ahmad Kabara wanda da cikakkiyar gudummawarsa da nuna qwarewarsa ne wannan Littafi ya samu fitowa, dakuma Malamina Mai tarbiyata Wato Malam Auwalu Isa Yakasai Da kuma Malam Maisunan Malan Allah ya saka musu da Alheri, kuma Allah ya cika musu burinsu a duniya da Lahira.

Wassalamu Alaikum Warahmatullah

Auwal Zakari Muhammad Ayagi

Al-Azmiyyah Ventures

No. 852 Kofar Kabuga,

Kano State.

 

Gabatarwa

Da sunan Allah mai Rahma Mai jinkai, Ubangiji Mahaliccin Sammai da qassai, tsira da Aminci su tabbata ga Annabinmu Annabin Rahma, shugabanmu Annabi Muhammadu (SAW) Allalh ya qara tsiransa ga sahabbansa da Alayensa da masoyansu da mabiyansu har zuwa ranar Al-qiyama, Innamal A'amalu Binniyati, wa'inn ma likulli Imri'in ma nawa (Hadis Ash-sharif).

Bayan haka acikin wannan dan taqaitacccn littafi wanda ya qunshi Tarihi da kasuwanci da zuriyar Mal. Usman da na wallafa, nayi shine musamman don ganin na zaburar da jama'a (musamman zuriyarsa) zuwa ga sada zumunci, musamman domin ganin yadda jama'ar wannan zamani sukai sako-sako da zumunci, sai kaga dan'uwa da dan'uwa sun hadu amma basu san ccwa su 'yan-uwa ba ne.

Kuma gashi Allah da Manzon Allah (SAW) sun yi umarni da lalląi mu sada zumunci kuma mu guji yanke shi. Kamar yadda Manzon Allah yace:- "MAI YANKE ZUMUNCI BAZAI SHIGA ALJANNA BA"

Sannan yace: - YANA DAGA MANYA-MANYAN FALALOLI KA SADAR DA ZUMUNCI GA WANDA YA YANKE MAKA"

Har ila yau ya kara da cewa:- "HAQIQA ARRAHIM (Wato zumunci) TSAGI NE DAGA SNAN ALLAH ARRAHMAN (wato mai yawán Rahma) ALLAH YACE: WANDA YA SADA SHI (Zumunci) ZAN SADASHI DA RAHAMA WANDA YA YANKE SHI (Zumunci) ZAN YANKE SHI DAGA RAHMA".

Har ilayau dai yace:- "ABUBUWA HUDU ( SUNA DAGA TASKOKIN ALJANNA: -

1. SIRRINTA YIN SADAKA

2. BOYE MUSIBA

3. SADA ZUMUNCI

4. FADIN "LAHAULA WALA KUWATA ILLA BILLAHI'

Da sauran Hadisai da dama, kuma ya tabbata cikin Hadisin Annabi cewa: "Kasan Allah kafin ka bauta masa" saboda haka wanda duka bai san 'yan-uwan sa ba, to bazai iya sada zumunci ba, don haka na himmatu wajen wallafa wannan littafi da fatan Allah (SWT) ya sa wannan littafi ya zama sila ko wata hanya ta sada zumunci, kuma ya zama izna ko jankunnc ga masu yanke zumunci, su dawo ga sadashi, Allah (SWT) ya sakamu cikin masu sada zumunci kuma ya sadamu da Rahamarsa, ya shiryar

da masu yake zumunci su zama daga cikin masu sada zumunci don su sami Rahmar Ubangiji, Amin.

Auwal Zakari Muhd Ayàgi

ABUBUWAN DA KE CIKI

ABUBUWAN DA KE CIKI                    Shafi

Shafin Farko ………….…………………………..…1

Sadaukarwa……………………….……,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,2

Ta’aliqi……………………………………,,,,,,,,,,,… 3

Godoiya…………………………………,,,,,…,,…4

Abubuwan da ke ciki……………………………,,…7

Gabatarwa…………………………………………,..8

Babi Na Farko:

Taqaitaccen Mal. Usman………………,,,,,,.…,…. 10

Matansa……………………………………,………11

‘Ya’yansa……………………………………...,,….12

Jikokinsa,,,………,,,,,,,,…………………/….,,,,,,,..,14

‘Ya’yan Jikokinsa …………………..…,,,……,,…17

Tattava Kunnensa…,,………,,,,,,,,,…………….… 20

‘Yayan Tattava Kunnensa ……,,,,, ………….……27

Babi Na Biyu

Kammalawa……,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,29Fadakarwa………………………….,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,30

 

 

 

 

 

 

 

 

BABI NA FARKO

Kasuwanci A Zamanin Da

Kano ta Dabo Tumbin Giwa, Yaro koda me kazo an fika. Wannan shi ne kirarin da ke yiwa Kano, saboda shahararta ta kowanne bangare musamman kasuwanci, don haka ne ma ake cewa da Kano cibiyar kasuwanci wato (Center of Commance) kamar yadda yake a rubuce a kowacce lambar mota ta Kanon. To duk wannan ya samo asaline tin zamanin daya shuxe, lokacin da ba jiragc, ba motoci ba kekuna sai jakuna da dawakai da Raquma sama da shekaru dubu da suka wuce.

Daga cikin sana'o'in da Kano ta shahara da su a a zamanin da can, sun hada da Noma, Saqa, qira, Fatauci, Kiwo, Gini da sauransu. To amma Noma da fatauci sune suka fi shahara a wancan zamanin, don a da ance Kano ba abin da zai fara zuwa zuciyarka, sai Dalar Gyada, Kano ta shahara sosai da wannan sana'a.

Haka ma fatauci daxaxxiyar sana'ace ta mutanen Kano, Fatauci ya kasu daban-daban akwai gajcren Fatauci, inda mutum zai tafi kusa da garinsu yayyo siyayya ya dawo garinsu ya sayar, akwai kuma wanda zai tafi gari mai nisa, ya kwashe watanni ko shekaru, wasu ma in suka tafi sun tafi Kenan, acan zasu yi aure su hayayyafa, don hakane ma ba garin da zakaje ba ka ga Bahaushe ba, to wannan ya samo asali ne ta hanyar Fatauci. Galibi fatauci ana yinsa ne ta hanyar Ayari a karkashin jagoracin Madugu, dole ne ya zama shi Madugun yafi kowa shiri sabo da hatsarin da ke cikin sana'ar kamar Yan-Fashi, Barayi, Almatsutsai Namun Daji da suke kan hanyar. Har hausawa kan yi masa kirari da "Madugu Uban Tafiya".

 

 

BABI NA BIYU

Taqaitaccen Tarihin Mal. Usman

Malam Usman wanda aka fi sani da Shehu, cikakken sunansa shine Shehu Usmanu dan Hussaini Mutumin Garin Kumurya.

An haife shi a wani garı mai suna Kumurya wanda a yanzu yake cikin karamar hukumar Bunkure ta jihar Kano. Malam Usmanu ya taso cikin karatun Addinin Mlusulunci, sannan kuma ya na sana'ar Noma (Kamar yadda ta shahara a wancan zamanin) Allah ya daukaka Mal. Usman a wannan sana'ar ta Noma, inda ya mallaki nanya-manyan gonaki, kuna yake noma su.

A inda daga bisani ya fara sana'ar fatauci ta hanyar siyan kayayyaki ya tafi dasu wadansu garuruwan ya sayar ya sayo wasu acan ya kai garinsu. Har daga baya sai ya fara barin kasar Kano ya na wannan tafiye-tafiye ne ta hanyar Ayari na Fatake, suna wannan Fataunci ne akan Jakuna, zasu dorawa Jakunan Kaya su kuma su bisu a kasa, suna daukan watanni kafin su isa, da sunje sun siyar sai su sayo wadanda akce bukata a wannan garin su tawo da su. Idan sun iso sukan yada Zango a wani guri mai yawan ruwa da bishiyoyi, su tsaya su wanke jikinsu, su ba Jakunansu ruwa suyi kiwo, su huta saboda gurin ya yi kama da can kudancin kasarnan inda suke zuwa wato Kurmi, to in sun tsaya su na hutawa, sai Jama'a su dinga zuwa suna sayan kayayyaki, abin ya na ci gaba, wasu ma anan kayansu suke karewa sai su koma.

Ana halin haka saí ya zama kamar Al-ada da Sun dawo sai su ce, mu tafi Kurmin Kano, to da zarar sun zo sai Mal. Usman ya wuce gidan wani Abokinsa ya sauka da yake a wata unguwa kusa da wannan Kurmin mai suna Mararraba, in ya siyar da kayansa da wuri sai ya yi sauri yaje garinsu Kumurya ya dawo kafin ayari ya tashi.

Ana cikin wannan hali sai wannan Abokin nasa ya bashi shawarar cewa kamata ya yi, ya sa yi gida a nan kusa da Kurmin, shi ma, idan suka sauka, sai ya sauka a gidansa, idan ayari ba zai tashi da wuri ba, sai yaje Kumurya garisu, in kuma da wuri zasu tashi, shi ke nan sai ya koma, sai Mal. Usman yai na'am da wannan shawarar kuma ya danka komai a hannun abokin na sa, akan ya nemo masa gida, idan ya dawo sai ya bashi kudin (a lokacin ana lissafi da keso ne, ba Naira ba) haka kuwa aka yi, yana dawowa, sai ya samu Abokin nasa ya sai mai gida akusa da unguwarsu a wata unguwa mai suna Ungwar Ayagi, suka je ya ga gida ya yi farin-ciki, da ya sai da kayansa ya kawo kudin sa ya bashi, inda daga baya sai ya debo iyalansa ya dawo dasu gidansa. To wamman shine dalilin zamansa a Unguwr Ayagi.

A wani Labarin kuma cewa akayi, ya zo cikin Kano ne neman Ilimin Addini, bayan ya Sauke Alkur’ani a can Kumurya, sai ya shigo Birni qarin neman Ilim, yana neman Ilimin ne ya fara sana’ar Fatauchi, har ya sa aka nema masa gidan ya siya, ya xebo iyalan sa suka dawo.

Haka Mal. Usman ya cigaba da wannan sana'a har lokacin da girma ya zo masa, sai ya dene Fatauci ya zauna a gidansa daya siya ya cigaba da kasuwanci a wannan waje, wanda a yanzu akewa lakabi da kasuwar Kurmi har zuwa lokacin da Allah ya karbi ransa, Allah, ya jikan sa da Rahamrsa Amin.

 

BABI NA UKU

ZURI’AR MAL. USMAN

Kusan wannan shine maqasudin rubuta wannan littafi, domin Allah ya albarkanci Mal. Usman da zuriya masu yawa, ko da yake sai da haifi ‘ya’ya takwas suna rasuwa, sai ta Taran ce Ayashe ta tsaya,. Don haka na kasa wannan kasha gida shida, kamar yadda zai zo a qasa.

 

 

 

Kashi na Farko

Matansa

 

Mal. Usman ya rasu ya bar Mata Huxu kamar haka:

1.              Fadimatu

2.              Hassana

3.              Hassana (Iya Masa)

4.              Amina (Aisa)

Kashi na Biyu

‘Ya’yansa

Mal. Usman ya rasu yabar ‘ya’ya ne guda Bakwai a raye, amma kafin ya rasu ya binne wasu da dama kamar yadda ita Hajiya Jummai ta tabbatar min, amma bakwai (7) sune wadanda ya rasu ya bari a duniya.

‘Ya’yansa sune kamar haka:

1.              Aishatu Usman (Ayashe)

2.              Hauwa’u Usman (Inna ta Fagge)

3.              Muhammad Usman (Baba Mai Goro)

4.              Amina Usman (Inna Amina)

5.              Sulaiman Usman (Baba Mai Lemo)

6.              Idris Usman (Idi Dan Shehu)

7.              Furera Usman (Hajyan Anchau)

Wadannan sune ‘ya’yan Mal. Usman guda bakwai, a inda daga cikin Mazan wasu sun gajeshi a sana’arsa ta fatauci.Kamar Muhammad yayi Sana’ar fatauci a Ikko inda ya zauna acan har yayi aure ya haifi wasu daga ‘ya’yansa a can, har sai da ya rike sarkin Hausawan acan iko ko Shagamu.

Allah ya jiqansu Ameen.

Kashi Na Uku

Jikokinsa

Yayan Aishatu Usman (Ayashe)

1. Hauwa’u (Hajiya Jummai)

2. Atine      (Tarasu)

‘Ya’yan Hauwa Usman (Inna ta Fagge)

2. Musa               (Ya Rasu)

‘Ya’yan Amina Usman

1. Sa’idu    (Baba Na Kafi) Ya Rasu

2. Abubakar (Uba na Kul-kul) Ya Rasu 9/12/2002

‘Ya’yan Furaira Usman

1.              Abubakar (Garba Kyauta)

‘Ya’yan Sulaiman Usman (Mai Lemo)

 1,      Garba        (Uban Kano)

2.              Inuwa          (Ya Rasu)

3.              Idris            (Dan Zaria) ya Rasu

4.              Fatima         (Jummai)    

5.              Muhammadu Sani

‘Ya’yan Muhammad Usman (Mai Goro)

1.              Zakariyya    (Amasha)

2.              Sadiya         (Asabe) Ta Rasu

‘Ya’yan Idris Usman (Idi Dan Shehu)

1.              Aisha          (Inna Yalwa)

2.              Saude          (Ta Rasu)

3.              Hassan       

4.              Hussaini     

Wadannan sune jikokin Mal. Usman Goma sha Bakwai (17), Goma (10) suke raye, Allah ya gafartawa wadanda suka rasu Amin.

Kashi Na Hudu:

‘Ya’yan Jikokinsa

Jikokin Aishatu Usman (Ayashe)

Yayan Hauwa’u (Hajiya Jummai)

1. Zulaihat (Yar Mallam)  Ta rasu

2. Sadiya (Hajiya Karama)

3. Sadiya (Lami)

‘Ya’yan Atine

Tarasu kafin ta haihu

Jikokin Hauwa’u Usman (inna ta fagge)

Yayan Musa (Baba na Fagge)

1.              Nasidi                             7. Ruqayya

2.              Ishak (Alh. Maikudi)      8. Ibrahim

3.              Isa                                   9. Idris (Dantalata)

4.              Adamu                           10. Usamatu

5.              Kadija  (Gambo)             11. Aliyu

6.              Fatima (Asabe)                12. Abdulkadir

 

Jikokin Amina Usman

‘Ya’yan Sa’idu (Baba Agwa)

1.              Auwalu (Lawan)  

2.              Adamu                 

3.              Zulaiha

4.              Abubakar

‘Ya’yan Abubakar (Uba Na Kul-Kul)

1.              Habiba                  6.Binta

2.              Dauda                   7. Ibrahim

3.              Furera (Laraba)     8. Musa

4.              Aliyu                              9. Amina

5.              Auwalu                

       

Jikokin Furaira Usman

‘Ya’yan Abubakar (Garba Kyauta)

1.              Furaira (Mammy) 

2.              Sulaiman (Abba)  

3.              Saliha (Ummi)     

4.              Hadiza (Baby)      

5.              Abdulmumin       

6.              Hafsatu

* Yayan Abubakar Sune Yayan Jummai

*Suna Zaune a Banzazzau Kusa da Gidan Kogi, Zaria Jihar Kaduna

Jikokin Sulaiman Usman (Mai Lemo)

Yayan Inuwa Sulaiman Usman

1.              (Ladi) Tarasu                  6. Maryam (Mama)

2.              Shehu                             7. Tukur

3.              Umar                                        8. Adamu

4.              Tanimu                           9. Musa

5.              Rukayya (Gaje)               Hadiza

                 

‘Ya’yan Idris Sulaiman Usman (Dan Zaria)

1.              Maryam     

2.              Bashari       

3.              Tukur         

4.              Hauwa

Yayan Jummai Sulaiman Usman

1.              Furaira (Mammy)

2.              Sulaiman (Abba)  

3.              Saliha (Ummi)     

4.              Hadiza (Baby)      

5.              Abdulmumin       

6.              Hafsatu

v   Yayan Jummai Sune Yayan Abubakar

Jikokin Muhammad Usman (Mai Goro)

Yayan Zakariyya Muhammad Usman

1.              Muhammad Auwal        

2.              Muhammad Sani

3.              Muhd. Salisu       

4.              Rukayya (Lami)   

5.              Hauwa’u (Hajiya)

6.              Muhd. Rabi’u      

7.              Saifullahi             

8.              Abdulrashid         

9.              Zakariyya (Halifa)

10.         Aliyu (Baffa)

 

Jikokin Idris Usman (Idi Dan Shehu)

‘Ya’yan Saude Idris Usman

1.              Aishatu (Yar yaye)                   5. Abdulrashid (Yarasu)

2.              Rabi’u                            6. Suwaiba (Ta Rasu)

3.              Misbahu                         7. Ummahani

4.              Asma’u                          8. Hauwa (Jummai)

‘Ya’yan Hassan Idris Usman

1.              Idris (Halifa)        

2.              Usman                 

‘Ya’yan Husaini Idris Usman (Yarasu)

1.                 Aisha (Ummi)     

2.                 Muammadu        

3.                 Fatima

Wadannan Sune Yayan Jikokin Mal. Usman, wadanda suka rasu Allah ya gafarta musu Amin.

 

 

 

Kashi Na Biyar

Tattaba Kunnensa

‘Ya’yan Jikokin Aishatu Usamn (Ayashe)

Jikokin Hauwa’u (Haj. Jummai)

‘Ya’yan Zulai (Yar Mallam)

1.              Ibrahim                

2.              Safiyya                

Yayan Sadiya (Hajiya Karama)

1.              Jamila          (Ta Rasu)    6. Abadiyya

2.              Yasin          (Yarasu)      7. Ubayyu

3.              Kudsiyya                        8. Wasilu

4.              Mujibur-Rahman           9. Saddiqa

5.              Mansulu                        

Ya’yan Sadiya (Lami)     

1.              Tijjani                            6.Aisha                

2.              Abubakar                        7. Kabiru

3.              Salamatu                         8. Aminu

4.              Fatima                            9. Aminu

5.              Bilkisu                                              

‘Ya’yan Jikokin Hauwa Usman (Inna Ta Fagge)

Jikokin Musa (Baba Na Fagge)

‘Ya’yan Nasidi

1.              Jamila (Tarasu)

2.              Maryam (Tarasu)

 

‘Ya’yan Ishak Musa (Alh. Maikudi Sarkin Fata)

1.              Hauwa (Maituwo) Tarasu 12. Ruqayya

2.              Binta (Ladidi)                 13. Hadiza

3.              Bashir                             14. Muhd (Yaya)

4.              Hauwa (Maijidda)           15. Ishaq (Alhaj)

5.              Aisha (Mai Riga)            16. Ibrahim

6.              Babangida                      17. Amina

7.              Ahmad                           18. Mahmud

8.              Habiba                            19. Hauwa (Momy)

9.              Musa (Abba)                   20. Aisua

10.         Zulaihat                          21. Bulyaminu

11.         Abdul-Hamidu               22. Nuraddin

‘Ya’yan Isa Musa

1)             Hannatu                          7. Khalil

2)             Jamila                             8. Isa (Babannan)

3)             Aminu                           9. Fatima

4)             Musa (Abba)                  10. Muhammad

5)             Ishak (Alhaji)                  11. Rabi

6)             Zainab                            12. Zakariyya

‘Ya’yan Adamu Musa

1.              Hauwa’u               4. Musa

2.              Aisha                    5. Muhammad

3.              Umar                     6. Abubakar

‘Ya’yan Khadija (Gambo) Musa

1.              Auwalu                 4. Fatihu

2.              Ibrahim                 5. Sulaiman

3.              Maryam                6. Aisha

‘Ya’yan Fatima (Asabe) Musa

1.              Maimuna              4. Faisal

2.              Rabi’u                  5. Muhd Sani

3.              Aina’u                  6. Umar

Ya’yan Rukayya Musa

1.              Kabiru                  4. Idris

2.              Halima                  5. Salmanu

3.              Aisha                    6. Sukairaju

‘Ya’yan Ibrahim Musa

1.              Hafsiyya     

2.              Abdullahi

3.              Furaira

4.              Usman

5.              Binta (Ummi)

 

‘Ya’yan Jikokin Amina

Jikokin Sa’idu (Baba Agwa)

Ya’yan Lawan Sa’idu

1.              Maryam

2.              Zubaida

3.              Zahara’u

Ya’yan Adamu Sa’idu

1.              Hamza        

2.              Saidu (Abba)                 

3.              Furera (Balaraba) 

‘Ya’yan Zulai Sa’idu

1.              Salisu

‘Ya’yan Abubakar Sa’idu

1.              Ibrahim (Halifa)

Jikokin Abubakar (Uba Na Kul-Kul)

Yayan Habiba Abubakar

1.              Saadiku                5. Hauwa’u (Ummi)      

2.              Fatihu                             6. Ibrahim

3.              Kamalu                 7. Aba Yazid

4.              Alawiyya              8. Sadiya

‘Ya’yan Dauda Abubakar

1.              Abdulrahaman

2.              Mustafa

Yayan Furaira Abubakar (Laraba) (09039151977)

1.              Zahara’u     

2.              Yakuba      

3.              Aminu       

4.              Shamsuddin         

5.              Mikidaru    

6.              Marakisiyya

7.              Maryam     

8.              Amina        

Yayan Binta Abubakar

1.              Aminu

2.              Zainab (Ummi)

3.              Aisha                    (08104066354)

‘Ya’yan Jikokin Sulaiman Usman

Jikokin Inuwa Sulaiman Usman

‘Ya’yan Amina (Ladi) Inuwa Sulaiman Usman

1.               Amina

2.               Abubakar

3.               Sadiya

4.               Hauwa

5.               Muzakkir

‘Ya’yan Tukur (Alhaji) Inuwa Sulaiman

1.              Amina

2.              Abubakar (Halifa)

‘Ya’yan Adamu Inuwa Sulaiman

1.              Muhd. Inuwa (Alhaji)

‘Ya’yan Hadiza Inuwa Sulaiman Usman

1.              Samha         (07032099857)

2.              Aminu

‘Ya’yan Rukayya (Gaje) Inuwa Sulaiman

1.              Sa’idu

2.              Sumayya

3.              Badamasi (Halifa)

‘Ya’yan Maryam Inuwa Sulaiman Usman

1.              Imran

2.              Asma’u

‘Ya’yan Jikokin Muhammad Usman

Jikokin Zakariyya Muhammad Usman

‘Ya’yan Rukayya Zakari Muhammad Usman

1.              Hafasat                 

2.              Sadiyya               

‘Ya’yan Jikokin Idris Usman

Jikokin Saude Idris Usman

‘Ya’yan Aishatu (Yaryaye)

1.              Amina                 

2.              Zainab                 

‘Ya’yan Rabi’u

1.              Fiddausi     

2.              Fatima (Momy)

3.              Habiba

‘Ya’yan Misbahu

1.              Rukayya    

‘Ya’yan Asma’u

1.              Fatima  (Ummi)

2.              Aisha         

3.              Sa’adatu     

4.              Khadija      

‘Ya’yan Ummahani

1.              Abdulhamid

‘Ya’yan Hauwa (Jummai)

1.              Aisha (Tarasu)

Wadannan sune tattaba kunnensa.

 

 

 

KASHI NA SHIDA

YA’YAN TATTABA KUNNENSA

Tataba Kunnen Aisha Usman

‘Ya’yan Jikokin Hauwa (Haj. Jummai)

Jikokin Zulai (Yar Malam)

‘Ya’yan Ibrahim

1.              Abubakar             

2.              Abdulrahman       

‘Ya’yan Safiya

1.              Hafsat                    5. Sahlat

2.              Aisha                    6. Umar

3.              Ramlatu                7. Maimunatu

4.              Muhammad                   

Jikokin Sadiya (Haj. Karama)

‘Ya’yan Kudsiyyah

1.              Amina

2.              Ahmad

3.              Muhammad

Jikokin Sadiya (Lami)

‘Ya’yan Salamatu (Magajiya)

1.              Mariya

  

Tattaba Kunnen Hauwa’u Usman

Yayan Jikokin Musa na Fagge

Jikokin Ishak (Alh. Maikudi)

‘Ya’yan Hauwa (Maituwo)

1.              Abubakar (Abba)           4. Shafa’atu

2.              Zahara’u                         5. Mubarak

3.              Maryam                          6. Najib

‘Ya’yan Binta Ishak Musa (Ladidi)

1.              Maryam (Ummi)

2.              Idris

3.              Muhammad Sani

4.              Hasiya                 

5.              Hauwa (Mamy)    

‘Ya’yan Bashir Ishak Musa

1.              Ishak (Khalifa)

2.              Salihu

3.              Muhammad Arab

‘Ya’yan Hauwa Ishak Musa (Maijidda)

1.              Khadija (Yariny)

2.              Ishak (Amir)

‘Ya’yan Aisha Ishak Musa (Meriga)

1.              Ahmad

2.              Muhammad

Jikokin Isa Musa

‘Ya’yan Hannatu Isa Musa

1.              Bashir

‘Ya’yan Jamila Isa Musa

1.              Rumasa’u

2.              Rabi

Jikokin Rukayya Musa

‘Ya’yan Kabir

1.              Adamu

Tattaba Kunnen Amina

Yayan Jikokin Sa’idu

Jikokin Lawan

‘Ya’yan Maryam

1.              Rabi’a

‘Ya’yan Jikokin Abubakar (Uba)

Jikokin Furere Abubakar (Laraba)

‘Ya’yan Zahara’u

1.              Bilkisu

2.              Salisu

Wadannan sune Yayan Tattaba Kunnensa

 

  

 

FADAKARWA

lna fadakar da sauran dangi cewa duk wanda yaga wani gyara ko kuskuren arubuta suna ko ragi ko qari na wasu Sunayen., ko yake da wani karin bayani da zai daxa kyautata littafin da ya sanar da ni cikin gaggawa, in za'a buga na biyu sai a shigar da su.

Da fatan Abin da nayi Allah ya karba, ya mika ladan ga shi Shehu Usman da ‘ya’yayensa da jikokinsa da suka rigamu gidan gaskiya, muma in munzo cikawa, Allah ya sa mu cika da Imani, Amin. Abin da aka yi na kuskure kuma Allah ya yafe mana, Amin.

 

KAMMALAWA

Alhamdulillahi, Alhamulillahi, Godya ta tta ga Ubangijin da ya halicci hallita ya kuma daidaitata, snnan ya sanya mata tsarin da zata tafi a kansa, kuma ya wajabta zumunci ya sanya lada mai dinbun yawa ga wanda ya sadar da shi, Tsira da amini su qara tabbata ga fiyayycn halitta, wanda ya tsamo mu daga duhun vata, zuwa hasken shiriya na Addinin Musulunci, Annabi ma’abocin cikar kalama da sada zumunci, shugaban da yake cewa: ‘Wanda yake so Allah ya yalwata masa (a cikin rayuwar sa), kuma a qara masa acikin arzikinsa, to yabi iyayen sa, kuma ya sadar da zumunci'  Sallallahu alaihi wasallam, Manzo yayi gaskiya. Allah cikin salatin ka hada da iyalan gidan sa, da sahabbansa baki daya.

Bayan haka, ina mai daxa godewa Allah daya bani damar kammala wannan litafi dana fara rubutawa Ranar 20-02-2001 zuwa yau Albamis 01-08-2002.

ALHAMDULILLAH

Sai Mun Haxu a Littafi Na Biyu

AUWAL ZAKARI MUHD AYAGI

(2 JUMADA THANI 1423)

01-AUGUST 2002

 

No comments:

Post a Comment