Friday, 1 February 2013

HUJJOJIN MAULUDI DAGA LITATTAFAN WAHABIYYA D



HUJJOJIN MAULUDI DAGA LITATTAFAN WAHABIYYA
Daga Muhammad Sani Zakariyya, Kwamitin  nazari da bincike na Mu’assasatush-Shaikh Khamis Alkhairiyya K/Kabuga, Kano State Nigeria.
            Godiya ga wanda ya zabi Annabi Muhammadu ya zama Annabi lokacin Annabi Adamu yana tsakanin ruwa da yunbu. Gaisuwa ga wanda bayyanarsa ta zama rahama ga talikai da ahlin gidansa da sahabbansa da wadanda suka bi shi da kyawawan aiki.
            Da yawa malamai suna fito da hujjoji da suke nuna halarcin Maulidi domin kara karfafa gwiwar masoya Annabi (SAW) bisa hidima da suke a wannan wata na Mauludi; Sai na ga ya dace na fito da hujjojin yin mauludin daga cikin litattafan su masu inkarin Mauludin domin ya zama hujja a kansu idan sun ce bata ne to malamansu ne suka fara; Idan kuwa sun ce bidi’a ne to ya ya suke da shaihunansu?
            Bari mu fara da babban shehun na su wanda shi ne abin koyin su wato SHAIKUL ISLAM AHMAD IBN TAIMIYYA wanda ya rayu a karni na shida zuwa na bakwai, ku ga abin da yake cewa akan Mauludi.
“Haka abin da sashen mutane suka farar da shi don koyi da kirista a haihuwar Annabi isa AS ko kuma domin kauna ga Annabi (SAW) da girmamashi. Hakika, Ubrangiji zai ba su lada a bisa wannan soyayyar da kuma ijtihadin da suka yi, ba a bisa bidi’ar da suka yi ba ta rikar mauludin Annabi (SAW) kamar idi tare da cewa malamai sun sami sabani bisa mauludi”.

IBN TAIMIYYA YANA YABON MASU MAULUDI DA KYAKKYAWAR MANUFA
Hakika  dai Shehul Islam Ibn Taimiyya ya ci gaba da yabon masu Mauludi da tabbatar musu da lada mai girma da kuma kawo hujja da cewa mauludin bidi’a ce mai kyau ga Mazhabin Imamu Ahmad ga dai abin da yake cewa:
“Lallai girmama Mauludi da rikonsa ya zama wani taro. Hakika a cikin mutane akwai masu yin hakan, lada mai girma kuma ya kasance a tare da su, saboda me? Saboda kyakkyawar manufarsu da kuma girmamawarsu ga Annabin Allah (SAW).
Malamin ya ci gaba da cewa:
Kamar yadd aya ce a baya wani abun ya na zama mai kyau ga sashen mutane wanda zai iya zama mummuna ga munin mai taka-tsantsan, saboda haka aka ce da Imamu Ahmad don Hambali menene hukumcin wani shugaba da ya fitar da kudi dinare dubu domin buga Alkur’ani? Sai ya ce ku kyale shi wannan abin da ya yi shi ya fi a cikin abin da ake ciyarwa na dinare. Tare da cewa makaruhi ne a Mazahabar shi Imamu Ahmad din kawata alkur’ani.
To ‘yan uwa wannan fa shi ne babban shehin  wanda daga gareshi ne dukkan akidar wahabiyya, salafiyya, sunniyya, izala ta fito dubi inda da bakinsa yake fadar hujjar mauludi. Da sakamakon mai yinsa. (Don Karin bayani dubi littafin Iktida’usiradal mustakin shafi  na 312-317).
 To, daga dai kin gaskiya sai bata, yakamata masu makauniyyar biyayya su sake nazari su ji abin da malamansu suke fada ko sa gane abin da iyayen gidansu na yanzu suke musu ‘yar burun-burun.
YADDA SHEIKH IBN KASIR YA FAHIMCI MAULUDI
Shi ne sheikh Abil fadal Alhafiz Ibn Kasir ya fadi ra’ayinsa ga Mauludi wanda azahiri ma yana nuna halaccin yin mauludin kuma ya goyi bayan masu yinsa cikin littafinsa ‘ALBIDAYA-WANNIHAYA’ mujalladi na bakwai shafi na dari da Ishirin da uku (123) inda yake yabon Sarkin Muzaffar kan hidima da yake yi a watan Mauludi.Ga dai abin da yake cewa:
Sarkin muzaffar ya kasance yana yin Mauludi mai girma a cikin watan Rabiul Awwal.Yana  yin gagarumin taro, kuma ya kasance mutum ne jarumi, mai Juriya, mai tunani adali, Allah ya jikansa yasa Aljanna makomarsa.
Ibn kasir ya ci gaba da cewa
Hakika shehu Abdul Khadab Ibn Dahiyya ya wallafa littafi mujalladi  a kan Mauludi ya sa masa suna ATTANWIR FI MAULIDIL BASHIRIN NAZIR. Sai Sarki ya sa aka ba shi dinare dubu saboda abin da ya yi.

IBN KASIR YANA JINJINA WA SARKI MUSAFFAR SABODA CIYARWAR DA YAKE A RANAR MAULUDI
            Ibn kasir ya yaba wa Sarki muzaffar saboda irin ciyarwar da yake da hidima ga jama’a domin tunawa da ranar haihuwar shugaban halitta (SAW) ga abin da Ibn Kasir yake cewa:
An rawaito daga sashin wadanda suka halarci mauludin Sarki Muzaffar ya ce: Sarki Muzaffar yana fito da nau’in abinci kamar farfesun naman kai sama da guda dubu biyar da soyayyun kaji dubu goma da kabakin man shanu ko curi guda dubu goma kayan taba-ka-lashe sama da dubu talatin, ya ce manyan malamai masana da sufaye suna halartar mauludin tare da shi. Sarki Muzaffar ya kasance kowacce shekara yana kashe dinare dubu dari uku domin hidima ga mauludi.
            To duba ya kai dan uwa yadda Ibn Kasir yake yabon wannan Sarki, wanda wannan Sarki shi ne Sirikin baban mujahidin nan da ya kwato baitul Mukaddas wato SALAHUDDIN AL AYUBIY (RTA). Shi kuwa Ibn kasir kowa ya san shi; Shi ne babban waziri kuma babban almajirin Ibn Taimiyya, masoyinsa wanda ya karfafa akidarsa, to amma ga abin da yake cewa game da Mauludin, kai hasali ma shi Ibn kasir ya yi littafi a kan mauludi mai suna: MAULUDI RASULULLAHI (SAW) wanda har sashin ‘yan uwa suna karanta shi a dararren mauludin domin ya yi shi ne a tsarin irin litattafan da ake karantawa a dararen mauludi kamar Barzanji, Kamalul fatahi, Faidul Ahmad, Mauludul kabari da sauransu. Ga ma abin da yake cewa a farkon littafin:
‘Bayan haka, wannan ambaton wani abu ne daga ambaton Hadisai da kissoshi da suke da dangantaka da haihuwar Annabi SAW) wanda aka cirosu da ingancinsu daga malaman Hadisi masana kwararru. Abin da muke nufi a nan lallai daren haihuwar Annabi (SAW) ya kasance dare ne mai girman daraja mai albarka da amfanarwa ga muminai…”.
A cikin mukaddamar wannan littafi ne malamin ya yi tahakkin littafin Sheikh Salahuddin Almunjid wanda shi ma salafiyi ne yake cewa:
Abin lura da rubuta wannan littafi da Ibn Kasir ya yi, cewa su mutanen Sham sun kasance suna taron mauludi a masallacin Hambila a masallacin da Ibn Taimiyya yake karatu. Saboda haka shi ladanin masallacin wanda shi malami ne kuma almajirin Ibn Taimiyya ya nemi Ibn kasir ya rubuta masa littafi kan mauludi da za su rinka karantawa, sai Ibn kasir ya rubuta musu wannan littafin.
Saboda haka, wannan littafi da Ibn kasir ya yi yana nuna cewa ya yarda da halarcin Mualudin baya ganin laifin yinsu. Inji fa shi Sheikh Salahuddin Almunjid Assalafi.
To dan uwa da kake takama da kai salafi ne kake haramta mauludi ga abin da malaman malamanka suke fadi ga mauludi.

MALAMAN HADISI DA SUKA YI LITATTAFAI A KAN MAULID
Masu musun mauludin suna cewa wai salaf ba su yi ba. Wai su wane ne salaf din? ga malamai masana Hadisi wadanda duniyar ilimi ta tabbatar da su sun yi litattafai a kan Mauludi misalinsu sune:
1.      ALHAFIZ IBN NASIRIDDIN ADDIMASHKIY (777-842) ya kasance yana girmama Ibn Taimiyya yana sonsa amma ya yi littafi a kan Mauludi mai suna: JAMI’UL ASAR FI MAULUDI NABIYIL MUKHTAR Mujalladi uku da kuma ALLAFAZU RAIK FI MAULIDI KHAIRUL KHALIK.
2.      ALHAFIZUL IRAKI 9725-808) mawallafin Alfiya ta hadisi kuma babban Malami a fannin shi ma ya yi littafi a kan mauludi mai suna AL MAURIDUL HANA FIL MAULIDIS-SANA.
3.      ALHAFIZ ASSHAUKANIY (831-902) shi ma ya yi littafi a kan mauludi kamar yadda mai Kashifuz-zunin ya ambata.
4.      ALHAFIZ MULLA ALIYUL KHAIRI 91014) ya yi littafi a kan mauludi mai suna ALMAURIDUR RAWI FI MAULUDIN-NABAWI
5.      AL HAFIZ IBN KASIR 9774) ma’abocin tafsir mai yawan Ilimi kuma almajirin Ibn Taimiyya (Kamar yadda muka fada a baya) shi ma ya yi littafi a kan mauludi mai suna MAULIDI RASULULLAHI (SAW) tahakikin Salahuddin Almunjid.
Kadan kenan daga malaman Sunna-salaf da suka yi littattafai a kan mauludi.

SHEIKH USAIMIN DA MAULID
Shi ma Sheikh Usaimin (Muhammad Ibn Dalha Al-usaimin) daya daga malaman Wahabiyya ne na baya-baya kuma masu tsananin suka ga mauludi, Allah ya sa ya yi bayani kan mauludi. Haka kuwa ya faru ne a tambayar da aka yi masa a kan halarcin mauludi bayan ya haramta shi, sai kuma  ya yi subutar baki gaskiya ta fito. Ga abin da yake cewa:
“Babu kokwanto cewa wadanda suke taron mauludin Annabi (SAW) suna yin haka ne domin girmama Annabi (SAW) da kuma bayyana soyayyarsa da kuma karfafa himma domin motsa ‘adifa’ (karsashi) na son Annabi (SAW) sababin wannan taro. To dukkan wadannan abubuwa ibada ne domin son annabi (SAW) Ibada ne; kai bari ma Imani ba ya cika sai mutum ya zamo yana son Annabi SAW fiye da kansa da ‘ya’yansa da iyayensa da mutane baki daya, kuma shi ma girmama Annabi SAW Ibada ne, haka kuma motsa adifa a kan Annabi (SAW) yana cikin addini saboda a cikinsa akwai karantuwa izuwa bin shari’arsa (Saboda haka yin taro na mauludin Annabi (SAW) domin neman kusanci izuwa ga Allah da kuma girmamawa ga Annabi (SAW) ibada ne. to idan kuwa ya kasance ibada ne har abada ba ya halarta a kagi wani abu cikin Addinin Allah da ba ya cikinsa (saboda wannan dalilai da ya kawo ya ce, wai Mauludi bidi’a ce muharrama).
Dan uwa dubi inda Allah ya sa ya rinka zubo hujjojin mauludi da kuma yaba wa mai yin maulidi amma akarshe sai ya ce wai bidi’a ce. Allah ya shirye mu mai so karin haske sai ya nemi wadannan litattafai:
1.      Ikitida’us siradil mustakin muhalifatu Ashabul jahin (92-317).
2.      Fatawal Akida (382-384)
3.      Al biday wannihaya mujalladi na bakwai shaf 9123-124)
Allah ya sa mu gane gaskiya gaskiya ce; ya sa mu yi aki da ita ya sa mu gane karya karya ce, ya sa mugujeta.

Daga dan uwanku a musulmi
Muhammad  Sani Zakariyya
A madadin kwamitin Nazari da
Bincike na Mu’assasatush-Sheik
Khamis Alkhairiyyah
Kofar Kabuga, Kano, Nijeriya

1 comment:

  1. Aslm malan dan allah kadaina wahalar da kanka akan abinda bayada amfani. Koda dukkanin malaman duniya suka goyi bayan maulidi idan har basuda hujja ta shari'a to wallahi aikin banzane idan kanaso mugane maulidi to kakawo aya ko hadisi kaitsaye akan maulidi to shikenan zamu yarda.

    ReplyDelete