Thursday, 7 February 2013

HAKKOKIN MAKWABTAKA A MUSULUNCI

HAKKOKIN MAKWABTAKA A MUSULUNCI
 Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da aminci su kara tabbata ga Shugaban halitta da Ahlin gidansa da Sahabansa, da dukkan wadanda suka bi shi da kyautatawa har zuwa Ranar Karshe.
Bayan haka, a yau jama'a da dama ba sa kulawa da hakkokin da Musulunci ya shimfida wa makwabtaka da irin yadda ya tsarawa kowane makwabci ya zauna da makwabcinsa da yadda zai girmama shi da kuma yadda zai gujewa cutar da shi.Don haka, na ga ya dace in dan fadakar ko in tunatar da 'yan uwana Musulmi da suka rafkana ga irin wadannan Hakkoki tare da fatan wannan rubutu zai amfanar da masu karatu.
Da farko, wajibi ne kowane Musulmi ya san hakkokin makwabcinsa da suke kansa,
tare da sanin ladaban zama da shi, idan ya san hakan, shi zai sa ya zauna da
makwabtansa  kamar yadda addini ya tsara.Domin Ubangiji mai girma da daukaka
ya fada  cikin littafinSa mai girma, cikin suratul Nisa'i aya ta 36 cewa: 
"GA IYAYE A KYAUTATA MUSU, DA MAKUSANTA, DA MARAYU, DA MABUKATA, DA MAKWABCI NA KUSA".
 Da kuma fadin Manzon Allah, Sallallahu Alaihi wasallam cewa; "JIBRILU BAI GUSHE
BA YANA YI MIN WASIYYA KAN MAKWABCI HAR NA ZACI ZAI GAJENI" (Buhari
da Muslim).
Har ila yau, da fadinsa Alaihis-salam "WANDA YA KASANCE YA BAYAR DA GASKIYA DA ALLAH DA RANAR LAHIRA YA GIRMAMA MAKWABCINSA" (Buhari da Muslim).
Idan muka yi duba ga wannan Aya da wadannan Hadisai za mu fahimci girman
kyautata wa makwabci da girmama shi, domin girmama shi ma yana nuna cewa
mutum ya bayar da gaskiya da Allah da ranar Lahira.
WANENE MAKWABCI
Malamai sun bayyana makwabci cewa shi ne wanda in ka kidaya gidaje arbain daga jikin gidanka hagu da dama gaba da baya.
RABE-RABEN MAKWABTA DA HAKKOKIN KOWANE
            A tsarin Musulunci makwabta sun kasu zuwa kashi uku, kowanne da
irin hakkokin da ke kansa, akwai mai hakki daya da mai hakkoki biyu da kuma mai
hakkoki uku.
1.         Makwabci Musulmi, makusanci (Dan'uwa): Shi wannan yana da hakkoki uku, hakkin Musulunci ga hakkin makwabtaka, ga kuma hakkin 'yanuwantaka, wanda yake tsan-tsan ya ga ya auke dukkan wadannan hakkoki.
2.         Makwabci Musulmi:  shi wannan yana da hakkoki biyu ne kawai, wato hakkin makwabtaka, sai kuma hakkin Musulunci.
3.         Makwabci wanda ba musulmi ba: shi ma nan yana da hakki daya ne kawai wato hakkin makwabtaka.

HAKKOKIN MAKWABTAKA
Akwai hakkokin makwabtaka da dama, amma za mu dauko wasu daga
ciki mu yi bayaninsu.
KAYUTATA MASA: Yana daga cikin hakkokin makwabtaka a kyautata masa ta kowanne hali, kamar aika masa da abin da ka dafa, bashi shawarwari da za su amfane shi, a kansa ko iyalansa, ko 'ya'yansa, tsawatarwa 'ya'yansa a kan abin da aka ga zai cuce su, domin kyautata wa makwabci yana kai mutum zuwa Aljanna "wani mutum ya je wajen Manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: "Ya Ma'aikin Allah shiryar da ni a bisa wani aiki, idan na tabbata a kansa zan shiga Aljanna, sai ya ce: Ya Ma'aikin Allah ta ya ya zan san ni mai kyautatawa ne? Sai ya ce: Tambayi makwabtanka idan suka ce kai mai kayutatawa ne to shi ne, amma idan suka ce kai ba mai kayuatatawa ba ne, to ba shi ba ne". Wannan Hadisi yana
nuna mana cewa idan mutum yana son ya san matsayinsa, to ya tambayi makotansa sune shaidarsa a kan shi mai kyautatawa ne ko a'a, don haka wajibi ne mu zamo masu kyautata musu don mu samu kyakkyawar shaidar cewa mu masu kyautatawa ne, don in muka zamo masu kyautatawa, to mun kama hanyar zuwa Aljanna.
Ibn Umar ya kasance yana da makwabci Bayahude, idan ya yanka akuya sai ya ce: ku kai wa makwabcina Bayahude wannan (Abu Dawud da Tirmizi).
Har ila yau, ki ya ye mutuncinsa da na iyalinsa da dukiyarsa suna daga cikin kyautatawa, domin Annabi Alaihissalam ya ce: "Mutum ya yi zina da mataye goma shi ya fi sauki a gare shi da yin zina da matar makwabcinsa, mutum ya yi sata a gidaje goma shi ya fi sauki a gare shi da ya yi sata a gidan makwabcinsa" (Ahmad).
Ya zo cikin sunani Abu Dawud daga Aba Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: "wani mutum ya zo wajen Ma'aikin Allah ya kawo karar  makwabcinsa, sai ya ce da shi, ka je ka yi hakuri, sai ya sake zuwa na biyu ko na uku, sai Manzon Alla ya ce: jeka ka debo kayanka ka zuba a kan hanya, sai ya je ya sanya duk lokacin da mutane suka zo  wucewa sai suka tambaye shi bisa halin da ya ke aiki, sai ya basu labarin irin cutar da makwabcinsa yake yi masa. Sai suka rinka la'antar makwabcin, sai makwabcin ya zo gare shi ya ce: ya dan uwana mayar da kayanka gidanka ba za ka kara ganin wani abu na rashin kyautatawa ba daga
gareni har abada".
2. RASHIN CUTAR DA SHI: Har ila yau, yana daga hakkin makwabcin a kan makwabci kada ya cutar da shi ta kowanne hali, wurin magana ne, ko a wani aiki ko a katangarsa, ko ya sa indararon ruwan gidansa, ya rika zuba musu ruwa cikin gidansa, ko saka murhun girki a jikin bangonsa ya rika zafafa masa bango, ko hayakin girki  ya rika shiga gidansa yana tirara masa daki. Ko rariyar sa ta biyo ta gidan ka ka toshe ta, ko ya rinka kora masa kazanta, ko yaki tsaftace ta wurinta ya rika cutarsa, ko ya daure dabbobi a cikin kadangarsa su rinka bugun bangonsa. Ko ya rika kiwon kaji a jikin gidansa warinsu ya rika cutarsa. Da dai sauran cutarwa ta kowane hali. Domin Manzon Allah sallallahu Alaihi wassalam ya ce : Bai yi imani ba! Aka ce wane ne ya Ma'aikin Allah? Sai ya ce: wanda makwabcinsa bai aminta daga cutarwarsa ba". A cikin wata ruwayar ya ce: "Ba zai shiga Aljanna ba wanda makwabcinsa bai aminta daga cutarwarsa ba (Muslim)  da fadin Manzon Allah Alaihis Salam "Wanda ya kasance ya bayar da gaskiya da Allah da ranar Lahira, kada ya cuci makwabcinsa (Buhari da Muslim). Da kuma fadinsa (SAW). "Ita tana wuta gashi ita tana azumtar yini, tana tashi da daddare amma tana cutar makwabtanta" (Ahmad da Hakim). Wadannan Hadisai duk suna zuwa ga guje wa cutar da makoci.

3. GIRMAMA SHI: Girmama makoci shi ma yana daga cikin hakkokin makwabtaka. Kada ka wulakanta shi, ko ka yi masa kallon banza aa ka girmama shi da duk wani sanadi da ka sani, ka yi alheri a gare shi, domin Manzon Allah Alaihis Salam ya ce:  "YA KU MATAN MUSULMI KADA MAKWABCIYA TA WULAKANTA MAKWABCIYARTA" da fadinsa ga Abi Zarrin: YA ABA ZARRIN IDAN ZA KA DAFA MIYA KA KARA YAWAN RUWANTA KA AIKA WA MAKWABTANKA". Da kuma fadinsa (SAW) ga Aisha lokacin da ta ce ina da makwabta biyu ga wanne daga ciki zan shiyar? Sai ya ce zuwa wanda kofarsa tafi kusa gareki (Buhari da Muslim).
Yana daga cikin girmama shi da karrama shi, kada ka hana shi jingina gini a gininka, ko dora wani abu a kan katangarka, kamar rumfa, ko azara da sauransu, kuma kada ka sayar da wani abu naka ko ka bayar da jinginarsa face ka fara tuntubarsa, in ba ya bukata, sannan sai ka sayar wa da wani domin fadin Annabi Alaihis Salam cikin Hadisin Buhari da Muslim cewa: 'WANDA YA KASANCE YANA DA MAKWABCI KO ABOKIN MU'AMMALA KADA YA SAYAR DA WANI ABU NASA HAR SAI YA BUJURO GARE SHI (Ma'ana sai ya tambaye shi ko zai saya in ba zai saya ba sannan ya kai wa wani). (Buhari da Muslim).
4. JURIYA GA CUTARSA: Yana da kyau ga makwabcin da Allah ya jarrabe shi da makwabci mara kirki da ya jure ya yi hakuri kamar yadda muka ambata a Hadisin da ya gabata na Aba Huraira na mutumin da ya kai karar makwabcinsa wurin Manzon Allah, sai ya ce da shi ya yi  hakuri daga cutar makwbcin nasa, yin hakuri daga cutar makwabci bin umarnin Manzon Allah ne, kuma rashin hakuri daga cutar tasa, da daka ta tasa kullum rigingimu iri-iri to wannan saba Umarnin Annabi Alaihis-salam ne, rashin bin umarninsa kuwa babban laifi ne kuma halaka ne. Wajibi ne ga makwabci ya hakura da cutar makwabcinsa ko da kuwa ba Musulmi ba ne, domin an rawaito daga Sahih dan Abdullahi Attusturi (Allah ya yi masa rahama) cewa shi ya kasance yana da makoci wanda yake zuba ruwan kazanta daga gidansa zuwa gidan Sahih, sai shi Sahih ya sanya wani daro duk lokacin da ya zubo wannan kazantar sai ya tare a daron, idan dare ya yi sai ya je ya zubar yadda babu wanda zai gani.
Haka ya zauna cikin wannan hali har lokaci mai tsawo, har lokacin da ajalinsa ya tabbata, sai ya kira wannan makocin nasa kafiri ya ce da shi, zo ka shiga gidana ka ga abin da yake cikinsa, da ya shiga sai ya ga daro cike da kazanta a ciki, sai ya ce da shi mene ne wannan nake gani? Sai Salihu ya ce ai wannan ya dade yana zuba gidana sai na tare shi da rana, in dare ya yi sai in zubar, to kuma yanzu ajali ne ya gabato ina jin tsoron in na rasu kada ku samu sabani da wani ba ni ba, in ka aikata masa wannan abu, sai kafurin ya ce; ya kai wannan malami yanzu haka ka yi hakuri da ni na tsawon lokaci ga shi kuma ni kafuri ne? To miko min hannunka, take ya yi kalmar shahada ya musulunta.
            In muka duba ga wannan kissar za mu fahimci darusa da dama, kamar juriya da hakuri da wannan malami ya yi da cutar makocinsa kafiri, har tasa ya ranauta zuciyar kafirin, ya musulunta.
Ina rokon Allah Subhanahu wata'ala da ya gyara halayenmu, ya sanya mu cikin masu kyautata wa makotanmu, da girmamasu da kauce wa cutar da su Ya Ubangiji ka kara mana juriya daga cutar makota, ka sanyamu cikin masu babban rabo Duniya da Lahira. Ka kara tsira da aminci ga Shugaban halitta Annabin rahama sallallahu alaihi wasallam.
Wassalamu Alaikum warahmatullahi ta'ala wabarakatuhu
Dan uwanku a Musulunci 
Auwalu Zakari Muhd Ayagi
E-Mail auwalzakari@yahoo.com
Tel: 07038775781, 08023615685


No comments:

Post a Comment