Tuesday, 17 June 2014

CIN RUBA TANADIN YAKI DA ALLAH DA MANZON SANE

Cin Riba Tanadin yaki da Allah da Manzon sane
Daga Auwal Zakari Ayagi

Da suna Allah mai Rahama mai jinkai, tsira da aminci sukara tabbata ga fiyayyen halitta cikamakin Annabawa, shugabannin manzanni, tare da sahabbansa da suka taimaka masa wajen kafuwar  addini, da Ahalin gidansa da matayensa da dukkan wadanda suka bishi da kyautatawa har zuwa ranar Alkiyama.

Bayan haka Ubangiji mai girma da daukaka yana fada cikin Alkur’ani mai girma:

{ یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ ٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَذَرُوا۟ مَا بَقِیَ مِنَ ٱلرِّبَوٰۤا۟ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِینَ (278) فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُوا۟ فَأۡذَنُوا۟ بِحَرۡبࣲ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۖ وَإِن تُبۡتُمۡ فَلَكُمۡ رُءُوسُ أَمۡوَ ٰ⁠لِكُمۡ لَا تَظۡلِمُونَ وَلَا تُظۡلَمُونَ (279) }

[Surah Al-Baqarah: 278-279]

Ma'ana

“YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KUJI TSORON ALLAH KU BAR ABIN DA YAYI SAURA DAGA RIBA IN KUN KASANCE MUMUNAI, IN HAR BAKU AIKATABA (barin cin ribar) INA MUKU IZINI DA YAKI DA ALLAH DA MANZONSA, IN KUKA TUBA ASALIN DUKIYARKU NA GAREKA BAKU YI ZALUNCI BA BA’A ZALINCE KUBA”  (Bukara Aya ta 272-279)
Wannan aya tana tsoratar damu game da Mu’amala da Riba, inda Allah da kansa yake cewa duk wanda bai bar cin Ruba ba yana masa izinin yin yaki dashi da Annabinsa (SAW), kamar yadda yazo a labari cewa: Ranar Alkiyama Ubangiji zai bawa masu cin Ruba makami ya umarce shi da yayi yaki da shi, Allah ya kiyayemu, Allah yace: amma in kuka tuba to sai ku debi asalin Dukiyarku (jarinku) ragowar kudin sai ku rabar in kukai haka bakuyi zalunci ba kuma ba’a zalunce kuba.

Menene Ruba?
Ruba tana nufin dadi abisa abubuwa da kebantar Karin kudi

Rabe-Raben Ruba
Ruba ta kasu izuwa kashi biyu wato:
* Rubar Dadi
* Rubar jinkiri

* Rubar Dadi: Rubar dadi tana nufin cinikin jinsi daya kamar (Gero da Gero, Dawa da Dawa, Naira da Naira da sauransu) amma tare da dadi akan cinikin, kamar asayi Gero kwano daya amma sai ace sai ka dada rabin kwano akan kwano dayan, ko sayan sababbin kudi, misali na Naira dari biyar amma ace sai an dada Naira Hamsin akai, da sauransu.

* Rubar Jinkiri: Rubar jinkiri ta kasu kashi biyu,:
* Ruba Ninkawa
* Ruba mai daduwa don dogon lokaci.

Ruba mai ninkawa: Ruba mai ninkawa itace ake cewa Rubar Jahiliyyah, wannan itace ubangiji ya haramtata da nassin Alkur’ani mai girma, inda yake cewa: “YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KADA KUCI RUBA NINKIN-BANINKIN: (Ali Imram Aya ta 130).

Yanda wannan Ruba take, Shine a baiwa wani bashi zuwa wani lokaci abin ayyanawa, idan lokacin yayi bai samu damar biya ba, sai ace dashi ko ya biya ko kuma a karamasa kudi sannan a kara masa lokacin biyan, haka za’a rika karamasa kudi ana karamasa lokacin biyan, har kudin sun ninninka kansu.

Misali kan wannan shine kamar bashin da kasashe suke ciyowa bisa yarjejeniyar zasu biya zuwa Shekarun da aka ayyana, idan lokacin yayi basu biya ba, sai kudin suyi ta karuwa gwargwadon tsowon lokacin da kasar tayi bata biyaba, sai aga kudin sun ninka kansu ninkin ba ninkin. To wannan itace Rubar da wannan aya take Magana akai.

Ruba mai daduwa don dogon Lokaci; Wannan itace Rubar da ake bada bashi da kari don bashin zai dauki dogon lokaci, misali: abada bashin naira Dubu daya amma za’a biya dubu da dari daya a tsawon kwanaki ishirin.
Ko sayen wani abu da kari kan asalin kudin sa don daukan dogon lokaci, misali sayen Sha’ir ko Dabino ko kwaya kamar wake, masara, gero da makamantansu, amma da Karin kudi in zai kai wani lokaci, misali: ana sayar da Masara Naira 300 a ko wacce kasuwa, sai abada ita bashi akan Naira 350 don za'a biya a watanni biyu, ko biya biyu ga ma’aikata, da makamantansu.

HUKUMCIN RUBA
Ita dai Ruba haramunce, sabo da fadin Ubangiji madaukakin sarki cikin suratul Bakara Ayata 275 cewa:
“Allah ya halatta ciniki ya haramta ruba”
Da fadinsa “YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KADA KUCI RUBA NINKIN-BANINKIN: (Ali Imram Ayata 130).

Ga kuma fadin Annabi Alaihissalam cewa:

1. “Allah ya tsinewa mai cin Ruba da wakili akan Ruba da masu shaida akan Ruba da marubucin Ruba” (As-habu Sinan)

2. “Sisi na Ruba da mutum yake cinsa yana sani shi yafi tsananin Azaba da Zina Talatin da mutum zaiyi" (Ahmad da Hakim)

3. “Ruba kofa Saba’in da Uku ce mafi saukinsu shine mutum ya auri mahaifiyarsa" (Hakim)

4. "Ku nisanci abubuwa bakwai mafiya ukuba, sai akace yarasulullahi menene? Sai yace: Yin tarayya da Allah, da sihiri da kashe ran da Allah ya haramta da cin Ruba, da cin dukiyar marayu da juya baya (Guduwa) Ranar yaki, da yin kazafi ga mumina katangaggiya” (Buhari da Muslim) 

UKUBAR MASU CI RUBA
Ubangiji madaukakin sarki yafada cikin Suratul Bakara Ayata 275:

“Wadannan da suke cin Ruba basa tashi (yayin tashi daga kaburbura) sai kamar misalin wadanda shaidanu suke bubbugewa (tashin su kamar na masu fyarfyadiya) da shafa (ta Aljanu) wadannan don cewa su suna cewa shi ciniki kamar Ruba ne”.

Idan Ubangiji ya tashi mutane ranar Alkiyama zasu fita suna masu gaggawa, sai masu cin Ruba su zasu tashi suna faduwa kamar masu fyarfyadiya, don cewa su yayin da suke cin Ruba Ubangiji yana tarata a cukkunansu har ta rinjayesu ranar Alkiyama duk yayin da suka tashi sai su fadi, suna son suyi gaggawa kamar sauran mutane amma baza su iyaba.

Katadatu yace Mai cin Ruba za’a tasheshi ranar Alkiyama yana mahaukaci.
An karbo daga Abi Sa’idul Khudri (RTA) cewa Manzon Allah (SAW) yace yayin da akai Isra’i dani, na shude ga wasu Jama’a cukkunansu yana gabansu ko wane mutum cikinsa kamar katon gida, cikin nasu yana karkatar dasu suna masu kururuwa a bisa kwararowar azabar Jama’ar Fir’auna ana bijiro musu da azaba safe da yamma, sai yace: sai a bijiro musu da Azaba kamar misalin gudajjen Rakumi basaji basa gani, yayin da wadannan masu cukkunan sukajisu sai su tashi, amma sai cikkunansu su rinjayesu bazasu iya tashi ba, har sai jama’ar fir’auna sun samesu sai subi ta kansu, suyi gaba dasu suyi baya da su, haka za’ai ta yi musu wannan Azaba. Sai Ma’aikin Allah yace su wnene wadannan ya dan’uwa Jibrilu? Sai yace sune masu cin Ruba.

An karbo daga Ibn Mas’ud daga mahaifinsa cewa: Idan zina da Ruba suka bayyana a Alkarya, sai Ubangiji yayi izinin halakar da ita.

Manzon Allah (SAW) yace: Ruba bazata bayyana a al’umma ba face hauka ya bayyana  a cikinsu. Zina bazata bayyana ga Al’umma ba face Mutuwa ta bayyana a garesu, Al’umma baza su tauye ma’auni da mudu ba face Allah ya hana su ruwan sama.

Har ilayau Manzon Allah Alaihissalam yace: Jama’a hudu Allah bazai shigar dasu Aljanna ba, ba zasu dandani Ni’imarta ba.
i. Mai narka Giya
ii. Mai cin Ruba
iii. Mai cin dukiyar marayu bada hakki ba.
iv. Mai sabawa iyayen sa.

An karbo daga Abubakar Siddik (RTA) yace: Mai dadi da wanda aka dadawa yan wuta ne, (ma’ana Mai bada Ruba da mai karbarta)

Wadannan Ayoyi da Hadisai suna nuna girman laifin Ruba, da irin Azabar da zata riski masu mu’amala da ita, da kuma mahimmancin barinta.

HIKIMAR HARAMTA RUBA
Haramcin mu’amala da Ruba na dauke da hikima kamar sauran ibadu, an haramta ta ne sabo da jarraba imanin bawa don ganin yayi biyayya a cikin aikatawa ko cikin hani, sannan yana daga cikin haramcin Ruba:

* Kiyaye wa abisa dukiyar Musulmi, don kada yaci dukiya yana mai barna.
* Fuskantowar musulmi cikin yaduwar dukiyarsa cikin hali madaukaki ba tare da cutar da sauran musulmi ba, cikin sana’arsa da Moman sa da Kasuwancin sa da sauransu.
* Toshe hanyoyin masu sa kiyayya ga musulmi, domin kiyayya ga musulmi tana wahalshe shi, sababinta kuma abin hani ne.
* Tseratar da musulmi bisa ga abin da zai kaishi ga halaka don cin Ruba zalunci ne kuma halakane.
* Bude kofofin biyayya ga musulmi don suyi guzuri sabo da lahira.

KAMMALAWA
Kamar yadda muka karanta Ayoyi da Hadisan Manzo Alaihissalam masu hani ga yin mu’amala da Ruba, don haka ya zama lallai a garemu da mu barta, domin in har bamu barta ba abubuwan da Allah zai yiwa musu mu’amala da ita lallai zasu tabbata ga masu mu’amala da ita daga cikin mu, domin  a yau akasarin mu’amalarmu da Ruba a ciki, a Bankuna ne, ko a Kasuwanni, ko a wuraren ayyukanmu na yau da kullum, ada mutum sai dai shi da kansa yakai kansa wajen mu’amala da Ruba, Amma a yanzu biyoshi ake har wajen kasuwancinsa ko wajen aikinsa ana tura masa bashi mai dauke da Ruba, tare da yi mata kwaskwarima, don haka ya zama wajibi mu rika tantancewa tsakanin cinikayya (Kasuwanci) da Ruba.
Domin zakaji wasu suna cewa ai lalurace tasa ni karbar bashin Banki mai dauke da Ruba don babu yanda zanyi, ko a’a gidana zan karasa ginawa, ko abin hawa zan siya da makamantan haka, to shima Ubangiji a lalurar zai hukun ta shi sabi da mu;amalar da yayi da Rubar.

Dafatan Allah Ta’ala zai datar damu, ya tsarkake mana hanyoyin neman mu daga Ruba da makamantanta, ya shiryar damu ya karamana tsoronsa da biyayya agareshi, ya karamana Lafiya da zaman Lafiya da kwanciyar hankali a garunmu da sauran garuruwan musulmi. Allah ka kara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi Muhammad da ahalin gidansa da dukkan sahabbansa, da wadanda suka bishi da kyautatawa har zuwa ranar karshe.

Alhamdulillah.

Auwal Zakaria Ayagi

No comments:

Post a Comment