Wednesday, 1 October 2014

Bayani kan Amosanin Ka

BAYANI AKAN AMOSANIN KA

Da farko dai ya kamata da kai da sauran masu karatu su fahimta cewa amosanin kai ba ciwo ba ne, wato ba cuta ba ce wadda wata kwayar cuta ke iya sa wa. Kamar matsalar saba ta sauran fatar jiki da wasu suke ganin kamar ciwo ne, amosani shi ma saba ce da kan faru a fatar kai wadda take karkashin suma. To idan tana barbashewa za a ga fari-fari na zuba kamar gari, musamman idan an zo taje kai ko kitso ko an zo yi wa mutum aski.

Bari mu fara dora bayanin a kan ita kanta fatar jiki tukuna, sa’annan ka gane cewa ba matsalar da za ka damu da ita ba ce sosai. Dama fatarmu canzawa take daga lokaci zuwa lokaci, kusan a ce wata-wata, dangane da irin abinci da muke ci da yanayin gari wato, zafi ko hunturu ko rani ko damin, da irin abin da muke shafa mata da kuma
yawan shekaru, wato tsufa ko kuruciya. Duka fatar kowa tana son abinci mai lafiya isasshe, mai dauke da sinadarin abinci mai gina jiki wato protein, wanda daga shi ne fatar kan sarrafa sinadaran keratin da collagen da elastin, wadanda su ne ginshikan ita kanta fatar. Sai kayan marmari masu dauke da bitaman masu sa fata sheki da
walwala. Akan iya samun wasu sinadaran a man da muke shafawa, wanda shi ma fata kan tsotse su idan an shafa. Don haka za ka ga fatar wadanda suka faye samun wadannan irin abinci da mai daban da ta wadanda ba su cika samun hakan ba kuma a iya cewa fatarsu ta fi lafiya kuma ta fi rashin nuna matsaloli.

Dangane da yanayi kuma wasu fatarsu ta fi son zafi, wasu kuma ta fi son yanayin danshi, a wasu kuma ta fi son yanayin sanyi. Babu fatar da ke son busasshen yanayi irin na hunturu. Misali, shi ya sa kusan kowa yakan samu matsalar fata a wannan lokaci, tun daga kaushi zuwa faso zuwa saba zuwa tsagewar lebe, zuwa waskane, har zuwa
amosanin ka.

To amma duk da cewa amosani ba ciwo ba ne, yana daya daga cikin abin da kan sa mutane da yawa damuwa musamman ma mata, don haka dole a saurari mai korafin wannan matsala.

Matsalar kan shafi kusan rabin mutanen duniya, ba bambanci a tsakanin jinsinan duniya. Wasu lokuta yakan sa kaikayi, mutum ya yi ta sosa kai, wanda wannan ma idan a cikin mutane ne sai
kunya ta fara kama shi. Idan ana sosawa kuma barbashin kan biyo kai a gan shi a saman suma ko a kafada.

A gaskiya babu abin da zai warkar da amosanin ka, tun da ba ciwo ba ne, sai dai abin da zai rage shi. Kamar yadda muka fada a baya, yanayin abinci da na wuri suna taimakawa, haka ma man wanke kai wadanda ga su nan birjik a kasuwanni da manyan shaguna ba sai a kyamis ba. Da mutum ya je ya ce a ba shi maganin shamfo na amosani za a ba shi mai kyau. Mutane da dama sun fi ganin amfanin wani wai shi head and shoulders fiye da sauran. A mafi yawan lokuta da an fara amfani da shi za a fara ganin saukin barbashewar suma da kuma kaikayi. Ba wai hana fatar marmashewa yake ba, a’a yakan ba fata laushin da ba za a san lokacin da ta canza ba, tunda dole ne duk bayan ’yan makonni sai ta sama ta marmashe ta karkashi ta tofo. Ka ga ke nan babu tabbas din idan ka daina amfani da shi
ba zai dawo ba.

Babu kanshin gaskiya game da cewa idan kurar kai ta mai amosani ta sauko ta shiga ido tana illa ga lafiyar idon.

BAYANI GAME DA CUTAR HAWAN JINI

Bayani akan CUTAR HAWAN JINI

Cutar Hawan jini ta yawaita matuka a cikin mutane harda al’umarmu ta jinsin bakaken fata, kuma tana jawo mana illoli masu yawa. Babban abin damuwa da bakin ciki shine, da yawa daga cikin al’umarmu basu da cikakken bayani game da wannan cuta; wasu kuma sun sani amma basa bada himma wajen neman magani.

MENENE CUTAR HAWAN JINI?
Ana cewa mutum ya kamu da wannan cuta ne idan an auna shi da na’urar awon karfin bugun jini (wato spygmomanometer) wadda ta nuna awon jininsa ya kai, ko ya wuce, dari da arba’in bisa casa’in (wato > 140/90mmHg) kuma awon ya dauwama a haka. Sai dai wannan adadi da aka ambata yana sabawa saboda bambancin shekaru, jinsi (wato namiji ko mace), halin da mutum yake ciki, da sauransu. A takaice dai, sai
an je asibiti za’a iya tabbatarma mutum ko yana da cutar ko baya da ita.

MENENE YAKE KAWO CUTAR?
Ta la’akari da yadda wanna cuta ke faruwa ga mutane, an raba wannan cuta zuwa gida biyu.

Kashi na farko - Sama da kashi casa’in (>90%) na mutane dake fama da wannan cuta, har yanzu ba’a san takamaiman dalilin da za’ace shi ya kawo masu wannan cuta ba sai dai akwai wasu abubuwa ko al’amura da aka alakanta ga faruwar wannan cuta ga wadannan mutane na kashin farko.
Wadannan abubuwan sun hada da:
· Yanayin kwayoyin halittar dan-adam, ma’ana ana iya gadon wannan cuta.
· Jinsin dan-adam (anfi samu a bakaken fata)
· Yawaita shan gishiri fiye da kima.
· Yawaita shan barasa (giya).
· Kibar jiki mai tsananin yawa.
· Rashin motsa jiki, da dai sauransu.

Kashi na biyu - A wannan bangare, an gano wasu cututtuka na musamman da suke kawo wannan cuta. Cututtukan sun hada da:
· Cututtukan dake shafar kodar mutum.
· Cututtukan dake shafar kwakwalwa.
· Wasu daga cikin magunguna na bature.
· Wasu cututtuka dake shafar jijiyoyin jini, da dai sauransu.

TA YAYA AKE GANE ALAMOMIN WANNAN CUTA?
Wasu daga cikin mutanen da suka kamu da wannan cuta basu da wasu alamomi da suke ji, wasu kuma sukan ji kamar yawan ciwon kai, fargabar zuciya, raguwar gani ko gani dishi-dishi. Wasu kuma suna zuwa asibiti ne da alamomi na illolin da cutar ta haifar musu (za’a yi bayani nan gaba). Wasu kuwa sai sunje asibiti dalilin wata cutar, wurin bincike sai a gano cewa suna da cutar hawan jini.
Karin bayani a nan shine, ba wai ance da mutum yaji yana fama da daya ko wasu daga cikin alamomin can na sama kawai sai yace ya kamu da cutar ba. Wannan kuskure ne. Mutum ya bari sai yaje an auna shi domin a tabbatar masa ko yana da cutar ko bashi da ita, domin tabbatacciyar hanyar sanin mutum ya kamu da cutar hawan jini ita ce ta auna jinin da na’urar asibiti.

ILLOLIN CUTAR HAWAN JINI.
Wannan matsaloli zasu iya faruwa ga wanda bai dade da kamuwa da cutar hawan jini ba ko kuma ga wanda ya dade da ita. Sun kunshi:
· Ciwon koda wanda zai iya jawowa ta daina aiki.
· Raguwar gani ko makancewar ido.
· Ciwon shanyewar wani bangare na jiki kamar rabin jiki (wato Paralysis).
· Ciwon zuciya, da dai sauransu.

Sai dai abinda ya kamata a fahimta game da wadannan matsaloli shine, ba cutar hawan jini kawai ke kawo suba. Za’a iya samun su ta wasu cututtuka kamar ciwon suga (wato Diabetes Mellitus) da sauransu. Wadannan illoli sun fi faruwa ga mutanen da suke da wannan cutar kuma basa shan magani ko kuma basa sha kamar yadda likita ya umarta.

MAGANIN CUTAR HAWAN JINI.
Akwai magunguna kala-kala da ake bayarwa ga masu wannan cuta. Suna yin amfani ne wajen tabbatar da daidaitar awon jini na mutum ta yadda ba zai yi yawa har ya kai ga samar da wadancan illoli da muka ambata ba. Wadannan magunguna za’a same su idan anje asibiti wajen likita.
Haka kuma kula da wadannan abubuwa da zamu zana wadanda ke da alaka da wannan cuta suna taimakawa matuka wajen kiyaye kai daga samun wannan cuta ko rage matsalolinta ga wadanda suke da cutar. Abubuwan sune:
· Barin shan barasa.
· Rage yawaita shan gishiri a abinci.
· Motsa jiki akai-akai.
· Rage kiba mai tsanani, ta hanyar rage yawaita cin abinci fiye da kima, rage cin man kitse, motsa jiki da sauransu.
· Yawaita cin kayan lambu da ababen marmari kamar su lemo, yalo, karas, alaiyahu, zogale, rama, da danginsu.

KAMMALAWA DA SHAWARWARI.
Tunda mun fahimci wani abu daga wannan cuta, kamar abubuwan da aka alakanta ta da su, matsalolin da take jawowa da sauransu, to ya kamata mu tashi haikan, mu nemi kariya daga gareta kamar yadda Allah (SWT) da ManzonSa suka umurta, ta kiyaye abubuwan da ke iya jawota.
Ba karamin kuskure neba ga mai wannan cuta ya ki shan magani, wato yace ya warke, domin ba shi jin alamomin ta. A yanzu babu wani magani da ke warkar da ita gaba daya har abada, sai dai a sami saukin da zai bada dammar rayuwa kamar yadda mai Lafiya yake yi. Tabbas, mun yi imani da bayanin Annabi Muhammadu (SAW) inda yake cewa “kowace cuta tana da magani”, amma muna fata Allah cikin rahamarSa zai fahimtar da likitoci maganin da zai warkar da ita nan gaba. Saboda haka sai a dauki wannan cuta a matsayin kaddara daga Allah, a kuma nemi lada daga wajenSa, a cigaba da shan magani domin a samu
rayuwa cikin kwanciyar hankali kamar kowa.
Kada mutum ya tsaya a zuwa kemis kawai ya ki zuwa asibiti. Illar wannan shine, za’a iya bada maganin da bai dace da mutum ba, ko kuma wanda zai iya kawo masa babbar matsala ga jiki.
A kuma lura, kada a tsaya a yi ta shan magunguna na gargajiya, a ki zuwa asibiti domin wadannan magunguna basu da tabbas, kuma za su iya taimakawa wajen kawo matsaloli da zasu shafi koda, hanta da sauran sassa na jiki.
A karshe ina tunatar damu game da fadin Allah Madaukakin Sarki a cikin surar bakara “…kada ku jefa kawunanku cikin halaka…”, wato mutum kiri- kiri ya zauna ya bari ciwo yayi masa illa ya ki shan magani, karshe a zo ayi ta wahala da jidali akan zuwa asibiti, sabanin inda mutum ya tashi tunda farko ya nemi magani. Muna yin addu’a duk wadanda basu da Lafiya, Allah Ya basu sauki. Masu Lafiya, Allah Ya kara kiyaye su, Amin summa Amin.

Friday, 29 August 2014

Cutar Sankarar Mama

Memene sankaran mama?

Sankaran mama na afkuwa ne a yayin da kwayoyin halittar jikin mama suka fara girma a kan kansu ba tare da jiki ya umarce su ko ya bukace su da su yi haka ba.

Me yake jawo sankaran mama?
Mutane da dama sukan so su san abinda yake jawo wannan cuta ta sankaran mama.  Har ma sukan tambayi kansu, me yasa na gamu da wannan cuta?  Ko me ya sa matata ko kanwata ko ya ta ko kawata ta gamu da wannan cuta?  Ko akwai wani abu da na yi ko suka yi, da ya kamata su yi, ko na yi, da banyi ba, ko basu yi ba domin kare kai na ko kansu daga wannan cuta?.

Babu wani sanannen dalili da za a iya kawowa kai tsaye wanda za a ce shi yake kawo wannan cuta.  Sai dai akwai wasu dalilai da sukan sanya wannan cuta ta fi saurin kama wasu matan a maimakon wasu.  Waɗannan dalilai su ne:

Shekaru – karfin zaton kamuwar mace da sankaran mama, yana karuwa ne da yawan shekarun mace.

Sinadarin iyistirogin – Yawan Sinadarin iyistirogin da yake jikin mace. Shi wannan sinadari na iyistirogin yana ɗaya daga cikin sinadaran da jikin mace ya kunsa kuma yana da kyau a ce jikin mace yana  da wannan sinadari isashshe. Sai dai kuma bai kamata a ce jiki yana fitar da shi ba tare da hutu ba.

Wannan hutun yana zuwa ne a lokacin da mace take da ciki ko take shayarwa. Don haka  dalilan da suke haifar da kasancewar sinadarin iyistirojin a jiki suna jefa jiki cikin haɗarin kamuwa da cutar sankaran mama.  

Daga ciki akwai fara jinin al’ada da wuri (kafin a kai shekara goma sha biyu), yin al’ada har a wuce shekara hamsin da biyar, rashin haihuwa, da kuma jinkirin haihuwa da wuri har a wuce shekara talatin.  Waɗannan abubuwa ba yin kanmu ba ne, kuma za a iya saisaita yawan wannan sinadari a jiki ta hanyar shan magungunan hana ɗaukar ciki da na sa haihuwa da sauransu.

Girman Jiki da sura- Mace mai tsaho da mace mai kiba ta fi faɗawa hadarin kamuwa da wannan cuta.  Matan da sukayi kiba kuma basu rame ba har bayan sun daina jinin al’ada haɗarin kamuwarsu da sankaran mama yafi yawa. Haka kuma komai shekarun mace, wanda suke da tarin kitse a tumbin su ko kuma a kugun su suma hadarin kamuwarsu da sankaran mama yafi yawa

Tarihin cuta a cikin ‘yan uwa – Macen da a cikin yan uwanta an taɓa samun wata kamar mahaifiyarta, ko yarta, ko ‘yarta ta tana da wannan cuta, ta fi fadawa haɗarin kamuwa da wannan cuta.

Tarihin Kamuwa da cutar Sankaran mama: Macen da cutar  sankara ta taɓa kama ta a mamanta guda ɗaya, cutar za ta iya kama ɗaya maman ma

Wasu cututtukan mama da ba sankara ba: Wasu matan da aka taɓa cire musu tsiro a mamansu wanda likita ya ce musu ba sankara bane.  Dole sai suna zuwa a na duba wannan mama akai-akai domin irin wannan tsiro  zai iya juyawa ya koma cutar sankara daga baya

Akwai tabbacin cewa kamuwa da cutar sankaran mama ba laifin mutum ba ne. Bata da alaka wacce take kai tsaye da abincin da muke ci, kuma ba cuta bace mai kwayoyi da za’a iya kamuwa dasu ba.  Haka kuma ba a daukar ta ta hanyar jima’i, ko ta hanyar hulda da wanda yake da wannan cuta.

Ta ya ya ake gane sankaran mama?

Abu na farko da za a fara lura a tabbatar da cewa jiki ya kamu da cutar sankaran mama shine samuwar wani dan tsiro a cikin nonon maras ciwo.
Shi wannan tsiro za a ji shi kamar kurjin maruru sai dai ba ya  ciwo.  Duk macen da ta ji irin wannan a jikin mamanta sai ta garzaya wajen likitanta nan take. Dole ne a cire duk ilahirin irin wannan tsiron sannan a gwada a asibiti.
Maman da cutar sankara ta fara kamashi in an kalle shi a ido ba za a ga wani canji ba, haka kuma a jiki ma ba za a ji komai ba.  Ba ya kawo ciwo, baya sa zazzabi, amai, gudawa ko rashin cin abinci kuma ba ya hana ayyukan yau da kullum.  Ba lallai ba ne a ce kin taɓa ganin ko jin labarin cutar ba, domin mai yiwuwa ne a ce bata taɓa kama wata yar uwarki ba ko wadda kika sani.  A wannan mataki na farkon shigar wannan cutar akwai fatan cewa in dai aka yi maganin wannan cutar za a iya warkar da ita.

Sankaran mama kuma tana iya farawa  ta hanyar fitowar ciwo a kan mama ko fatar da ta zagaye kan maman.

A wasu matan kuma, kan nonon ne zai fara shigewa ciki. Za’a ga mazaunin sa ba daya yake dana ɗaya ɓangaran ba.

Idan aka kyale tsiron, ci gaba zai yi tayi da girma. Zai iya girma daga cikin maman har ya ratso fatar maman ya zamo gyambo (ciwo) wanda yake fitar da ruwa  da jinni mai wari, kuma ba zai warke ba sai anyi maganin wannan cuta.

A sa’ar da wannan cuta ta cigaba da bunkasa, ta kan bazu zuwa wasu sassa na jiki kamar kwakwalwa, hunhu, kasussuwa da hanta ta wata hanya da ake kira (Metastasis) da turanci.  Ita wannan bazuwar zuwa ga wadannan gabobin ne ke cutarwa, kuma da zarar hakan ta faru, duk da cewa bayar da magani ya zama dole, samun waraka abu ne mai wahala. 

Za  a iya gane irin wannan buzuwar cutar ta hanyar samuwar tari, haki, kumburin ciki, ciwo a kasussuwa musamman ma baya, rashin karfin kafafu da rashin iya motsa su.

Shin za a iya gane cutar sankaran mama da wuri?

Za’a iya gane wannan cuta da wuri ta hanyar lura da halin da maman ke ciki.  Wannan wadansu matakai ne da mace zata rika bi sau daya a wata domin ta duba mamanta ko akwai wani tsiro, kumburi, ko wata cuta a jikin maman.  Ya kamata ki bukaci likitarki ta koya miki yadda zaki rika duba mamanki ita ma kuma ta duba miki mamanki a kalla sau daya a shekara.  Daukan hoton mamman a asibiti don binciken cutar, na iya taimakwa wajen gano ta da wuri.

Matakan Sankaran Mama

Ana iya fahimtar tsanin bazuwar da wannan cuta tayi a jikin marar lafiya ta hanyar matakin da cutar take a wannan lokacin. Waɗannan matakai su ne:

Mataki na I: Tsiron cikin maman da bai  kai sentimita biyu ba, ko kuma yana daidai da sentimita biyu.  Kuma idan aka gwada kaluluwar hammata za’a ga babu wannan cuta.

Mataki na II: Faɗin tsiron cikin maman yana tsakanin sentimeta biyu zuwa biyar tare da kaluluwar hammata wacce ta nuna akawai cuta ko kuma wacce ta nuna babu cutar. Zai kuma iya kasancewa faɗin tsiron cikin maman ya wuce sentimeta biyar tare da kaluluwar hammata wacce ta nuna cewa akwai cutar.

Mataki na III: Wannan matakin an kasa shi zuwa gida biyu A da B.

A: A nan faɗin tsiron cikin maman ya fi sentimita biyar, kuma akwai kaluluwar hammata masu motsi waɗanda suke dauke da wannan cuta.  Ko kuma girman kumburin zai iya zama ko ma ya ya da kuma kaluluwar wacce kaluluwar hammata waɗanda suka maƙalewa juna kokuma suna maƙale da wata tsoka dake wannan gurbin.

B: A nan faɗin tsiron cikin maman zai zama ko yaya amma ya bazu zuwa fata, bangon kirji, ko kaluluwa da suke can kasan nono kuma a can cikin kirji.

Mataki IV: A nan faɗin tsiron cikin maman ko ma ya girmansa yake anan ya bazu zuwa wurare masu nisa kamar ƙasussuwa, hunhu, ko kaluluwar jiki da suke nesa da mama.

Mataki na I da na II su ne farkon kamuwa da wannan cuta amma mataki na III da IV cutar ta riga ta bunkasa.

Yaya ake maganin cutar sankaran mama?

Ana maganin sankaran mama sabuwar kamu ta wadannan hanyoyi:

Surgery (Fiɗa): Wannan shine a cire maman gaba daya ko wani ɓangarensa ta hanyar fida.  Amma yin wannan fiɗa ya danganta da abubuwa da dama wanda zaki tattauna da likitanki.

Chemotherapy - Shine yin amfani da magani domin a kashe kwayoyin da suka gina wannan cuta, wadda ta riga ta bazu zuwa wasu ɓangarori na jiki ko a kankantar da wannan kumburi na mama.  Duk da dai waɗannan magunguna su na da illoli, amma akwai hanyoyin da likitoci sukan bi domin taimakawa mai wannan cuta wajen samun saukin waɗannan illoli.

Hormone Treatment - yin amfani da wannan sinadari na homon domin su hana kwayoyin wannan cuta girma.  Za a iya yin wannan ta hanyar fiɗa, radiotherapy, ko shan da magunguna.

Radiotherapy - yin amfani da kwayoyi na wuta wajen kashe kwayoyin wannan cuta.

Akwai hanyoyi da dama da ake bi a warkar da wannan cuta, sai dai ya danganta da bazuwarta a jiki,  zabin mai ɗauke da wannan cuta, kuɗin da za’a iya kashewa, da yadda za a iya daurewa bin ka’idojion shan magani, da kuma kayan aiki da ake da su.

Yin maganin wannan cuta ya kan ɗau lokaci mai tsaho kuma ana bukatar yawan zuwa asibiti.  Yana da tsada kuma yakan dau lokaci.  Duk wadannan abubuwa ne da suka zama dole a tattauna su da likita.

Haka kuma yana da kyau mai ɗauke da cutar sankaran mama ta tattauna da ‘yan uwanta domin su gane yadda cutar take domin su ba ta goyon baya da kwarin gwiwa, kuma su taimaka wajen faɗakarwa game da lura da mama.

Sakamakon magani

Karbar magani ga jiki ya bambanta daga mutum zuwa mutum kuma ya danganta da:-

·  Matakin cutar a lokacin da aka gano ta: Cutar da aka gano ta tunda wuri tafi saukin warkarwa.

· Yanayin cutar sankara: Saukin  warkewar ya danganta da irin cutar sankarar da ta kama mutum.  Ana gane irin cutar ne bayan an yi gwaje-gwaje akan tsiron da aka ciro daga jikin mai ɗauke da cutar.

· Bin ka’idojin magani ba tare da kuskerawa ba.

Idan babu kumburi a hammata kuma girman sankaran bai wuce girman sentimita uku ba ko kasa da haka, kashi casa’in da tara cikin dari na waɗannan majinyatan sukan rayu har tsahon shekara biyar.  Haka kuma kashi sittin  cikin dari na  majinyatan da suke da kaluluwar hammata guda biyu zuwa hudu za su iya rabuwa da cutar a cikin shekara biyar in aka haɗa da kashi arba’in cikin dari na masu ɗauke da kaluluwa shida zuwa goma.

Idan kuma cutar ta riga ta bunkasa fa? A na nufin kenan ba za ta warke ba? To in da rai da robo.  Domin kididdigar da aka bayar a sama, ta samu ne ta hanyar hada sakamakon mutane da yawa da aka yi.  Babu likitan da zai ce lallai yadda aka samu din nan, haka ne zai faru a kanki, koda a ce an yi ta maganin amma cutar ta ki warkewa, likita zai iya bakin kokarinsa wajen bada magunguna waɗanda za su rage zafin cutar.

To magungunan gargajiya fa? Abun sani anan shine, duk wanda yake jinyar mai ɗauke da cutar sankara, fatansa ne a samu sauki da wuri saboda mai cutar ta daina shan wahala. Abin takaici shine, cigaban da aka samu akan  shawo kan cutar a kimiyyance bai taka kara ya karya ba. Amma duk da haka, yafi amfani nesa ba kusa ba, yafi rashin cutarwa, kuma yafi tabbaci fiye da kowane irin hanyar magani da wani ko wata zai zo miki dashi a yanzu. A karshe, mutum zai iya taimakawaa ckin  binciken samo maginin da yafu na yanzu aiki ta hanyar ba da gudunmawa da haɗin kai ga masu bincike a asibiti.

Yana da mutukar amfani mutum ya je asibiti da wuri da zarar ya lura da waɗansu canje-canje don neman magani.

TARIHIN SHAIK AHMADU TIJJANI (RTA)

An haifi Shaihu Ahmad Tijjani, wanda ya kafa darikar Tijjaniyya, a garin Ainu Mali a shekara ta 1150 BH. Mahaifinsa ya rasu a lokacin yana da shekaru goma sha shida a duniya.Shaihu Tijjani ya haddace Alkur’ani yana dan shekara bakwai a hannun wani malami da ake kira Abu Abdullahi Muhamamd binu Hamu.

Sa’an nan ya ci gaba da neman ilmi inda ya karanta fannoni dabam-daban a hannun malamai masu yawa. Daga nan kuma sai ya karkata zuwa ga tafarkin Sufanci,ya shagala da yakar kai da hore dare da gudun duniya da sauran abubuwan dake hawa wuyan wanda ya bi tafarkin Sufanci.

A lokacin da Shaihu Tijjani ya yi nufin shiga sha’annin Sufanci tsundum, sai ya rabu da matarsa ta aure don ya zama ya samu damar tattara hankalinsa a kan abinda ya sa a gaba. Kuma a bayan da ya gamsu da cewa ya samu abinda ya samu a cikin wannan sha’ani, watau ya kai wani mukami babba a Sufanci, sai ya sayi kuyangi guda biyu, ya ‘yanta su, kana ya daura aure da su. Ya sanya wa dayarsu suna Mabruka dayar kuma Mubaraka.

Allah ya arzuta Shaihu Tijjani da ‘ya’ya maza guda biyu da kuma mata masu yawa. Babban dansa shi ne Muhammad Kabir, dan wajen matarsa Mabruka, na biyun kuwa shi ne Muhammad Sagir wanda aka yi wa lakabi da Habib. Shi wannan matarsa Mubaraka ce ta haifa masa shi, kuma shi ne ya zama halifar Shaihin na farko a bayan rasuwarsa.

Shaihu Ahmad Tijjani ya yi tafiye-tafiyeda dama wajen neman ilmin Sufanci, kuma ya shiga dariku masu yawa kafin daga bisani ya zauna a wuri guda ya kafa tasa darikar ta kansa. A lokacin dayake zaune a Moroko, Shaihin ya shigadarikun Qadiriyya da Nasiriyya da kuma darikar Shaihu Abul Abbas Ahmad Habib wanda aka fi sani da lakabin Algimari. Bayan ya bar wadan nan dariku duka, ya tashi daga Moroko ya nufi cikin hamadar Sahara inda ya ya da zango a zawiyar Shaihu Abdulkadir binu Muhammad Al’abayal.

Daga nan Shaihu Tijjani ya fita zuwa Hajji. A kan hanyarsa ta zuwa Makka, ya wuce ta kasashen Tilmisan da Tunis da Masar. Ya isa Makka a shekara ta 1187 BH, inda ya sauke farali kuma ya sadu da malamai masu yawa. Bayan kammala aikin hajji, ya komo ta kan hanyarsa ta Masar da Tunis, sa’an nan Tilmisan wurin da ya ya da zango kadan kafin ya wuce zuwa birnin Fas, inda ya ziyarci kabarin Maula Idris kakan Sharifan Moroko a shekara ta 1191 BH. A wannan tafiya ne har ila yau, a wani kauye da ake kira Wajda, Shaihu Tijjani ya gamu da babban alamajirinsa, Shaihu Ali Harazimi.

A shekara ta 1196 BH, Shaihu Tijjani yakafa darikar Tijjaniyya a wani gari da ake kira Abu Samgun wanda a yanzu yake cikin kasar Aljeriya. Sa’an nan ya yi kaura daga wannan garin ya koma birnin Fas, a cikin kasar Moroko, inda Sarkin Moroko na wannan lokaci, Sarki Sulaiman, ya ba shi gida wanda ya zauna a cikinsa har zuwa karshen rayuwarsa. A nan ne kuma ya kafa zawiyarsa, ya tattaro alamajiransa, kuma ya ci gaba da aikin yada darikarsa. Shaihu Tijjani ya rasu a shekara ta 1213 BH. Ya bar matan aurebiyu, ‘ya’ya maza biyu da mata masu yawa.Sabanin Sidi Abdulkadir, Shaihu Tijjani ya mutu bai bar wani littafi da ya tattare lamuran darikarsa ba.

Amma mutane uku daga cikin manyan almajiransa sun rubuta littafai wadanda suka kunshi tarihin Shaihin da ka’idojin darikarsa da kuma ra’ayoyinsa dangane da tafarkin Sufanci. Wadan nan alamajirai su ne, Shaihu Ali Harazimi wanda ya rubuta littafin Jawahirul Ma’ani, Shaihu Muhammad binu Mushri wanda ya wallafa Aljami’u fil Ulumil Fa’ila da Shaihu Muhammad Dayyib Assufyani, wanda ya rubuta Al’ifadatul Ahmadiya. Daga wadan nan littafai ne mai bincike zai iya samun kusan duk abinda yake bukata dangane da darikar Tijjaniyya da tarihin Shaihinta.

Darikar Tijjaniyya tana da sharadai guda bakwai wadanda su ne harsashen da aka gina ta a kansa. Sharadan su ne kamar haka:

1. Wanda ya shiga darikar Tijjaniyya, yakarbi wurdinta, to ba ya fita har abada.

2. Kar ya gama ta da wata darikar dabam, watau kada ya zama yana Tijjaniyya kuma yana yin wata darikar alokaci guda.

3. Kada ya ziyarci wasu waliyyai, na raye ko mamata, sai dai Sahabban Annabi (SAW) kawai, da Shaihu Tijjani da sauran Shaihinnan Tijjaniyya.

4. Ya lazimci tsoron Allah a ko wane hali.

5. Ya lazimci kaunar Shaihu Tijjani da zuri’arsa da almajiransa.

6. Ya debe kauna daga abinda yake hannun mutane na samu, sai dai abinda suka kawo suka ba shi ba tare da ya roka ba.

7. Har abada ya rika sada zumunci da sasanta tsakanin ‘yan uwa.

Wurdin Tijjaniyya kuwa ya kasu gida uku:•

Na Farko: Wurdi Lazimi, watau wurdin farilla.
Wannan ya kunshi istigfari kafa dari, salatin Annabi dari, da hailala dari.
Ana yin wannan wurdi safe da yammaci.
Lokacin wurdin safe shi ne tun daga bullowar alfijir har ya zuwa lokacin walaha.
Lokacin wurdin yammakuma, daga bayan La’asar zuwa sallar Isha. Wanda lokacin safe ya wuce shi bai yi wurdin a cikinsa ba, to wannan zai iya ramawa a sauran wuni duka.
Wanda lokacin yamma ya wuce shi kuwa, yana iya ramawa a sauran dare duka. Haka nan, wanda wurdin rana guda (watau safe da yamma gaba daya) ya wuce shi, to dole ya biya wannan wurdi har abada.
Watau ana bin sa bashin wannan wurdi har tsawon rayuwarsa. Wannan shi ne wurdin farilla, ko kuma Lazimi.•

Na Biyu: Wurdin Wazifa.
Wannan ya hada da istigfari kafa dari, Salatul Fatihidari ko hamsin, Hailala dari ko dari biyu, da kuma wata addu’a da ake kira Jauharatul Kamal kafa goma sha daya.
Ba’a karanta Jauhara sai da cikakkiyar alwala, kuma taimama ba ta isarwa wajen karatun ta.
Wazifa ba farilla ba ce, saboda haka ana iya yin ta a safe da yamma ko kuma a lokaci daya kawai.•

Na Uku: Zikirin Jumma’a.
Wannan anayin sa ne ranar Jumma’a kawai, kuma ba ya inganta sai a cikin jama’a.
Lokacinsa shi ne daga bayan sallar La’asar har zuwa faduwar rana. Baya inganta mutum daya ya yi zikirin jumma’a sai fa in ya zama a garin babu‘yan Tijjaniya. Zikirin Jumma’a ya kunshi Hailala ne kawai, kuma bai da wani adadi kayyadajje.

Darikar Tijjaniyya ta watsu a sassa da dama na duniyar Musulmi. Daga cikin kasashen da ake samun mabiyan darikar akwai Masar, Turkiya, Muritaniya, Sudan, Senegal, Nijeriya, Gini, Gambiya da sauransu.

Thursday, 28 August 2014

Ciwon Sarke Hakora (Tetanus)

Ciwon sarke hakora ko tatanas kamar yadda wasu suka fi sanin sa da shi, shi ma nau’in ciwo ne da kan iya kama kowa, manya da yara, kuma kwayoyin cuta na bacteria da ake kira Clostridium tetani ke haddasa shi, kuma suna nan a kowane yanki na duniya.

Su wadannan kwayoyin cuta a cikin kasa suka fi rayuwa, amma iska kan kwashe su su bazu, wasu su hau fatar jiki. Idan suka samu suka shiga jiki sai su rika samar da wata guba da kan kama jijiyoyin jiki, su hana wurin motsi.

An yi kiyasin cewa duk shekara wannan ciwo na halaka mutane kusan dubu dari uku, yawancinsu jarirai, musamman a kasashe irin namu.

Yadda ake kamuwa da ciwon sarke hakora:
kwayoyin za su iya shiga jiki ne yayin da mutum ya ji rauni komi kan kantarsa (ko yanka ko kujewa ko gyambo ko kuna ko cizon wata dabba), idan  ba a dauki matakin kariya ba.

Jariri kan iya dauka a jikin abin da aka yanke cibi da shi, in ba mai tsabtaba ne. Bayan kamar kwanaki hudu zuwa mako biyu da yankan cibi ko yin rauni, gubar da kwayoyin cutar ke saki ta fara barna, za a ga jariri yana ta amai da zazzabi da yawan kuka da kin karbar mama. Wadannan su ne alamu na farko, in ba a dau matakin kai wa asibiti ba, za a ga wani bangare na jikin jariri ko kuma duk jikin gaba daya yana jijjiga, ko yana sandarewa.

A manya kuwa za a fara jin mukamukai sun cije, hakora sun sarke, sai wuya ya sandare, a kasa hadiyar ruwa ko abinci, sanadiyar wannan guba ta kwayoyin cutar. In ba a dauki mataki ba, haka za a ga duk jiki ya sandare daga sama zuwa kasa, wato daga kai har zuwa kafa, mara lafiya na bankarewa.

Kashi 40 zuwa 80 cikin dari na masu wannan karkarwa da sandarewa ba sa kai labari ko an je asibiti.

Hanyoyin kariya daga wannan ciwo: Allurar riga-kafin kamuwa da ciwon sarke hakora ita ce hanyar da aka tabbatar za ta kare kamuwa daga wannan ciwo.
Saboda haka:

1. Kowa da kowa ya samu a yi masa allurar riga-kafin sarke hakora akalla sau daya a cikin shekaru goma.

2. Mata masu ciki su rika zuwa awo domin a wurin ne ake ba da allurar riga-kafin wannan ciwo. Jaririn da ke ciki kan samu nasa rabon ta mahaifa.

3. A kai yara daga wata biyu ga cibiyoyin riga-kafi, a basu wannan allura, a sake komawa in sun kai wata hudu da wata shida, sannan duk yara daga shekaru 3-7 domin su suka fi yin rauni a yau da kullum ba tare da iyaye sun sani ba.

4. Idan yaro ko wani babba ya yi rauni, bayan zuwa asibiti an wanke ciwon, an ba da magunguna, to a tabbata an karbi allurar tatanas don yin riga-kafi.

5. A tabbatar ungozoma mai karbar haihuwa a gida tana amfani da sabuwar reza ko aska wajen yanke cibi, ba tsohuwar reza ko aska ba, domin ko tafasa reza da askar baya kashe kwayar cutar tatanas.

6. Manoma su yawaita zuwa karbar wannan allura, su kuma rika amfani da takalmin ruwa irin na roba domin wani zubin sukan yi rauni da lauje ko fartanya ba tare da ma sun sani ba.

7. A yi hanzarin kai jariri mai yin jijjiga ko mai nuna alamomin da aka zayyana a sama asibiti mafi kusa, ko da mai gida ba ya kusa, musamman in a gida aka haifi jaririn.

8. A yi hanzarin kai duk wani babba da hakoransa ko mukamukansa suka cije, ya kasa magana ko cin abinci asibiti mafi kusa.

Allah ya kara mana lafiya.

Friday, 20 June 2014

HUKUMCIN AZUMIN YA MACE A SHARIA

BAYANI AKAN HUKUMCIN AZUMIN MACE A SHARI’A

Daga www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah mai yawan Rahama,  Mai yawan jin kai, tsira da Aminci su kara tabbata ga fiyayyan halitta Annabin rahama, tare da saabbansa da iyalan gidansa, da duk masu binsa da kyautatawa har zuwa ranar Alkiyama.

Bayan haka Azumin watan Ramadan wajibi ne akan kowanne musulmi Namiji da musulma mace, kuma yana daya daga cikin manya manyan ginshikan musulunci, kuma daya ne daga cikin rukunansa, kamar fadin Allah (SWT) cikin littafinSa Mai tsarki cewa: "Yaku wadanda kuka yi imani, an wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi ga wadanda suka gabace ku, don kuji tsoron Allah" (Bakara aya ta 283).

Kamar yadda shari'a ta dora yin azumi akan namiji, haka ta dorawa ya mace yinsa, na Ramadanne ko na nafila, amma kuma shari'a ta rwangwantawa mace game da yin azumin a wasu wurare ko kuma ace awasu lokuta, wannan saboda kasancewar mace mai rauni ta fanin shari'a da hankali,

Idan watan ramadan ya tsaya to ya wajaba akan ko wanne musulmi da musulma, baligai, kuma masu lafiya, mazauna gida su yi azumi, ma'ana su kame bakinsu daga ci ko sha ko saduwar aure daga fudowar alfijir har zuwa faduwar rana, wanda kuma ya kasance mara lafiya ko yazamo matafiyi acikin kwanakin azumin ramadan, to ya halata agare shi da ya sha azumin sa'annnan ya rama adadin kwanakin da ya sha acikin kwanakin da bana ramadanba.

Allah (SWT) yace: "Wanda ya riski wata dag a cikin ku, to sai ya azumce shi, wanda kuma ya zamo maras lafiya ko matafiyi, to sai ya rama a kwanaki na gaba..." (bakara aya ta 185).

Don haka duk wanda watan Ramadan ya riske shi amma ya tsufa tukuf, ko kuma mara lafiya dake a kwance, da ba'a sa ran zai warke daga rashin lafiyar, mace ko namiji, to ko wanne daga cikin wadannan zai sha azumin, amma sai ya ciyar da miskini daya rabin sa'i, ma'ana mudu biyu na galibin abincin kasar, amaimakon ko wace rana, wacce ya sha azumi acikin ta. kamar yadda Allah maigirma da daukaka ya bayyana cikin suratul bakara aya ta 184.

To anan mace ma shari'a ta bata damar shan azumi saboda wadansu uzururuka wadanda ke faruwa agareta wadanda basa faruwa ga da namiji, wadannan uzururruka sune kamar haka:-

1. JININ HAILA DA JINI BIKI:- 
Ya haramta ga mace mai jinin biki ko na haila tayi azumi, amma kuma wajibi ne ta rama azumin awasu kwanaki da ba na ramadana ba, sabanin salloli su baza ta rama su ba.
Saboda Nana A'isha (RA) tace:- "Mun kasan ce ana umurtar mu da rama azumi amma ba'a umurtar mu da mu rama salla. Awata ruwayar ta imam muslim yace, "Mu'azatu tace na tambayi Nana A'isha nace saboda me mai haila zata rama azumi amma bazata rama sallah ba, sai tace:- ke 'yar (khawarijawa ce) sai nace ni ba ita ba ce nadai tambaya ne kawai, sai tace dani hakan na samun mu, sai aka umurce mu da mu rama azumi, amma ba'a umurce mu da mu rama salla ba, kuma ta kara da cewar wadannan al'amura ne da mutum yake tsayawa inda aka tsai da shi, ba ra'ayi ake bi ba a’a nassi ake bi. idan kuma mace taga farar kassa, wato wani ruwa da mahaifa take fitarwa bayan karewar jinin haila, wacce mace ke gane samun tsarkinta idan ta gan ta, to sai ta daura  niyya don daukan azumi. idan kuwa bata da wata takamaimiyar hanyar samun tsarki sai tayi kunzugu da Auduga ta gargajiya ko 'yar kanti, ko dai wani abu makamancinta kamar tolet paper, idan ta cirota da ganta tsaf babu jini ta tsarkaka kenan, to sai ta dauki azumi, amma kuma idan bayan ta dauki azumi sai jinin ya dawo mata a wannan ranar, to sai ta sha azumin, amma idan bata sha ba sai jinin ya dauke kafin magariba, to azuminta ya ingan ta. sa'annan matar da taji alamar fitowar jinin haila amma sai bai fito ba, sai bayan magariba to ita ma azumin ta yayi.
Matar da take haila sai jinin ta ya dauke tun dare sai tayi niyar yin azumi, kuma ta kasance bata yi wanka ba har alfijir ya keto to azumin ta ya ingan ta, bisa mazhabar daukacin malamai.
matar da tasan cewar gobe ne jini zai zo mata, amma sai ta tashi da azumi to ba zata ci abinci ba har sai idan jinin ya zo mata, sannan sai ta sha azumin, idan kuma bai zo mataba sai taci gaba da azuminta.
Mai biki idan ta samu tsarki kafin kwanaki Arba'in da haihuwar ta, to sai tayi wanka tayi niyyar azumi, amma idan jinin ya haura kwana Arba'in bai dauke ba to sai ta dauki jinin a matsyin jinin istihada (wato jinin cuta) sai dai kuma idan jinin ya yi dai dai da lokacin al'adarta wadda take yi duk wata, to wannan kam sai ta dauke shi amatsayin jinin haila.

2. Mace mai ciki da mai shayarwa:- Itama mace mai ciki ko mai shayarwa idan har yin azumi gareta zai cuce ta, ko ya cuce jaririn ta, ko kuma duka su biyun zasu cutu, to ita ma anyi mata rangwame akan ta sha azumi a cikin halin cikin ko shayarwar.
Amma kuma idan yin azumin zai cutar da jaririn ta ne kawai ban da ita, to zata rama azumin kuma ta ciyar da miskini daya maimakon azumin da duk ta sha aduk lokacin da tazo ramawa, amma idan yin azumin zai cutar da ita ne ita kadai to zata rama azumin kawai banda ciyarwa.Top of Form Domin Ayar da ke yin bayani akan wanda ke iya yin azumi amma da kyar to lallai akwai mace mai ciki da mai shayarwa idan suka jiwa kansu ko jaririn su tsoron cutuwa.
Don haka zance mafi rinjaye anan shine anyiwa mace mai ciki da mai shayarwa kiyasin marar lafiya don haka ya halatta da su sha azumin kuma ba su da kaffara sai dai ramuwa, ya Alla suna jiwa kan su tsoro ko suna jiwa 'ya'yan su tsoro, hujjar wannan itace ruwayar Imamu Tirmizi yace: Annabi (SAW) yace: Allah madaukakin sarki ya daukewa matafiyi wani yanki na azumi (wanda ya sha alokacin tafiyar sa) da wani yanki na sallah (yana nufin yin kasaru) kuma ya daukawa mace mai ciki, da mai shayarwa yin azumi.

3. Jini rashin lafiya:- ko kuma jinin ISTIHADHA macen da jini yake zuwar mata bana haila ba, azumi wajibi ne akan ta, bai halatta ta sha azumi saboda wannan jinin domin shi jinin rashin lafiya ne kamar zuwan kumallo ne ko fitar jini saboda rauni, ko fitar ruwan kurji, duk wadannan abubuwa ne wadanda basu da lokaci kayadadde na zuwan su, balantana ace mace tabar azumi domin su, ma'ana zuwan su ba zai hana mata yin azumi ba. 4. Matar aure:- Bai Halata ga Macar aure tayi Azumin Nafila ba, alhali mijin ta na gida sai da izinin sa ko idan baya gari ya yi tafiya, amma kuma ban da na ramadan, macen da azumi ya wajaba akan ta idan ta dauki azumin ramadan sai mijinta ya tara da ita da rana alhali tana dauke da azumin ramadan, kuma bisa yardarta, to dukkan su zasu yi ramuwa da kaffara, amma idan tilasta mata ya yi, to tayi iyakar kokarin ta na hana shi, amma bata yi nasarar hana shi ba, to ita babu kaffara a kanta sai dai ta rama azumi. Amma idan mace tana barci acikin watan ramadan sai mijinta ya tara da ita, to malamai sunce ita ma babu kafara akan ta sai dai ta rama azumi.

Anaso ga mace budurwa ko wacce mijinta ya yi mata izinin yin Azumin da ta rika yawan yin azumin nafila, ko yin Azumin mustahabbi (wato abin da aka so) da kuma yin azumin a ranakun litinin da Alhamis, da kwanaki shida na watan shawal, (wato Sittu Shawwal) da kwanaki goman farko na zulhijja, (Wato Ashara Zulhijja) da azumtar ranar Arafat da ranar Tasu'a da Ashura, sai dai kuma bai kamata ba gareta da tayi azumin nafila ba, alhali ana binta ramuwar wani azumin, har sai ta rama azumin da ake bin ta. kuma ya kamata ga duk matar da ta san cewa mijin ta baya iya danne sha'war sa a duk lokacin da dama ta samu, to ta nisanci mijin ta acikin azumi, kuma ta daina yin ado ko kwalliya a cikin watan azumi.

Akarshe malamai sun ce wajibe ne akan mace ta ramuwa azumin da ake binta kafin kamawar wani azumin, sai dai idan da wani uzuri mai girma, amma idan bata rama ba har wani azumin ya kama, ba tare da wani uzuri ba, to duk yayin da tazo rama wa, bayan ta rama sai ta ciyar da miskini daya. Kamamalawa Abin da akeso agare ki ya ke 'yar'uwa Musulma, idan kina Jinin haila to ki zauna bisa al'adarki tayin jini a duk wata, ki yarda da abinda Allah (SWT) ya hukunta agareki, kada kiyi kokarin shan wani abu da zai hana jinin fitowa, ki karbi abin da Allah ya yarje miki, na shan azumin akwanakin haila da yin ramuwar su bayan salla, domin kuwa haka matan Annabi (SAW) iyayen muminnai, da matan salihan bayin Allah, suka hakura.Amma idan kika ki, kika sha wani magani domin hana fitar jinin haila a watan azumi, jinin kuwa ya dauke kika samu tsarki kika cika azumin ki cif cif, batare da kin sha ko daya ba, to babu kommai amma baki yi koyi da iyayen muminai ba, kuma baki samu ladan yin koyi da salihan bayi ba.

Wannan shine dan abi da ya sawwaka game da hukumcin da shari'a ta dorawa mace game da azumi, da fatan zamu amfana, abin da akji na daidai daga Allah ne na kuskure kuma daga gareni ne, ina sauraron gyara,

Akulu kauli hadha wa astagfilullaha li wa lakum Wassalamu alaikum warahamatullah.

ADDUA TAKOBIN MUMINI

Addu’a takobin mumini
Daga www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jinkai.  Dukkan yabo da godiya su tabbata ga  Allah, Ubagijin halittu baki daya.  Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga mafificin halittu, Annabi Muhammadu sallallaahu alaihi wasallam, tare da alayensa da sahabbansa  baki daya, da duk wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar karshe.   Bayan haka, a yau inaso in dan yi tsokaci ne a kan addu’a a matsayinta na takobin mumini.  Za mu ga ma’anarta da falalarta da lokuta da guraben da ake karbarta, sannan da ladubbanta.  Haka nan akwai nau’in wadanda ake karba musu addu’a da kuma wadanda ba a karba musu ko kuma ake jinkirta musu. Sannan da bayanan a kan dalilan dasuke sawa ba a karbar addu’a  duk daga abin da aka cirato daga zantuka da bayanan magabata na kwarai, Allah Ya jikansu da rahama.  Sai kuma wani waige a kan Istikharah. Bismillah! MA’ANARTA A Larabce addu’a na nufin kiran wani, ko neman miko wani abu.  Suna cewa: da’aa bil kitabi, ma’ana ya nemi a miko masa littafi.  A isdilahi  kuma addu’a tana nufin tarin kalmomin yabon Ubangiji, masu nuni ga neman wani abu daga gare Shi, ko neman tsarin wani abu (sharri) daga gare Shi. FALALARTA “An karbo daga dan Abbas, Allah Ya yarda da shi cewa Yahudawan Madina sun tambayi Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) suka ce: ‘Ta yaya Ubangijinmu Zai ji addu’armu, bayan kai kana zaton cewa tsakaninmu da sama kimanin tafiyar shekara dari biyar ne.  Kuma tsakanin kowace sama da ’yar uwarta ma haka ne ?’  Sai Allah Ya saukar da:  “Duk lokacin da bayiNa  suka tambaye ka game da Ni, to Ni Makusanci ne. ina amsa addu’ar mai roko in ya roke Ni.”  Bakara aya ta 186 ( daga Algunya ta Sidi Abdulkadir Shafi Na 373). Ma’aiki, sallallahu alaihi wasallam,  ya ce “Addu’a ita ce ibada.”  Kamar yadda aka fitar a littafin Riyadhussalihin na Imam Nawawi a Kitabul – da’awati . A wata riwayar kuma ya ce: “Hakika Ubangiji na mu’amala irin ta jin kunya.  Idan bawa ya buda hannu ya roke Shi, Ya ki amsa masa,  ko dai ya gaggauta masa a amsawar tun a duniya, ko ya jinkirta masa sai a ran kiyama.” LOKUTA DA GURABEN AMSA ADDU’A Ana karba (amsa) addu’a a wurare da lokuta da kuma guraben yanayi kamar haka: 1- Yayin sujjada. 2- Lokacin alwala. 3-Lailatul kadri. 4- Yayin saukar ruwan sama. 5- Tsakar dare. 6- Tsakanin kiran sallah da ikama. 7- Ranar Juma’a 8- Ranar  Arfa. 9- Yayin kiran sallah.        10- Bayan kiran sallah. 11- Bayan jifan shaidan.      12- A Safa da Marwa. 13- Sallolin farilla.        14- Watan Rajab. LADUBBAN ADDU’A Yana daga cikin ladubban addu’a mutum ya kasance yana da: 1- Ikhlas – wato ya kasance yana da tsarkin zuciya, ya fuskanci Allah kadai a cikin abin da yake bukata. 2- Kyakyawan zaton amsa ta. 3- kankan da kai da sassauta sauti. 4- Shiga (suturarsa) da ci da shansa su kasance na halal. 4- Fuskantar alkibla.   5- Naci a addu’ar. 6- Cudanyata da yabon Ubangiji da kirari gare Shi. 7- Salatin Annabi farko da tsakiya da karshe. 8- Fadada abin nema ga sauran musulmai. 9- Yin ta a tsanani da walwala. 10- Halarto zunubi da bayyana tuba. 11- Bijiro ni’imomi da bayyana godiya ga Allah. 12- daga hannu sama da shafar fuska da shi bayan addu’ar. WADANDA BA A KIN AMSA ADDU’ARSU 1- Mai azumi yayin buda baki.   2- Wanda aka zalinta. 3- Shugaba nagari.   4- Matafiyi kan yardar Allah. DALILIN kIN AMSA ADDU’A Wofintar addu’a ga ladaban amsa ta na jawo kin amsa ta.  An tambayi Shehi Ibrahim  dan Adhama, Allah Ya yi masa rahama, cewa ‘ko me ya sa muke rokon Allah ba Ya amsa mana?’ Sai ya ce saboda :- 1- Kun san sunnar Ma’aiki, sallallahu alaihi wasallam, ba ku bi. 2- Kun san Alkur’ani ba ku aiki da shi. 3- Kuna cin ni’imomin Ubangiji ba ku godiya. 4- Kun san Aljanna ba ku nemanta. 5- Kun san wuta ba ku tsoranta. 6- Kun san shaidan kuna binsa. 7- Kun san mutuwa ba ku yi mata tanadi ba. 8- Kun san mamata ba ku tunawa da su. 9- Kun bar abinku kun shagalta da na mutane. Haka nan Allah Yakan jinkirta wa bawa addu’rsa don soyayya, kamar yadda hadisi ya bayyana cewa, “Bawa kan roki Allah Ya biya masa da wuri, saboda ba Ya son jin muryarsa; wani (bawan kuma) ya roka a jinkirta masa, saboda son jin muryarsa da Allah Yake .” TSAWAITA  ADDU’A KO TAKAITA TA Nana A’ishah, Allah Ya yarda da ita, ta ce Manzon Allah,  sallallahu alaihi wasallam, yana son  dunkulalliyar addu’a, yana barin watanta (ma’ana ba ya tsawaita mai wuce haddi), kamar yadda aka fitar a littafin Riyadhussalihina a Kitabul da’awati shafi na 264). ISTIKHARAH Wannan na nufin neman zabin Allah kan wani al’amari da bawa yake so ko zai aikata. Sayyadina Jabir, Allah Ya kara masa yarda, ya ce “Ma’aikin Allah, sallallahu alaihi wasallam, ya kasance yana koya mana istikhara a duk al’amari , tamkar sura daga Alkur’ani.  Yana cewa, ‘idan dayanku ya nufi wani al’amari, sai ya yi sallar nafila raka’a biyu, sai ya ce: Allahumma inni astakhiruka bi ilmika wa astakdiruka bi kudratika wa as’aluka min fadlikal azim fa innaka  takdiru wala akdiru wa ta’alamu wala a’alamu wa anta allamul guyub; allahumma in kunta ta’alamu anna hazal amra khairun li fi dini wa ma’ashi  wa akibati amri fakdirhu li wa yassirhu li summa barik li fihi; wa in kunta ta’alamu anna hazal amra sharrun li fi dini wa ma’ashi wa akibati amri fasrifhu anni wasrifni anhu wakdir liyal khaira haisu kana summa ardhini bihi  (sai mutum ya ambaci bukatarsa) – Imamul Bhukari. Tabbas Allah na fushi da bawanSa in ba ya rokonSa.  Allah Ka daukaka Musulunci da musulmai, Ka rusa kafirci da kafirai.  Ka yalwata mu da soyayyar Ma’aikinmu, sallallahu alaihi wasallam, Ka sa al’amarinmu ya kasance a ranar mutuwarmu muna masu cikawa da kalmar la’ilaha illallah muhammadur rasulullah

Tuesday, 17 June 2014

Bayani akan Aikin Hajji a takaice

Takaitaccen bayani kan aikin Hajji
Daga: www.sautulazimiyyah.blogspot.com

Da sunan Allah mai yawan Rahama mai yawan jinkai, tsira da aminci sukara tabbata ga Shuhaban Halitta da dukkanin sabansa baki daya.

Bayan haka Shi dai aikin Hajji ya kasu kashi uku ne:
1. Hajjin Tamattu’i.
2. Hajjin Kirani.
3. Hajjin Ifradi.

1. Hajjin tamattu'i: Shi ne wajibin wanda yake zaune a nesa da garin Makkah, nisan da ya kai mil 48, yayin da Hajjin Kirani da Ifradi sune wajibin wanda yake zaune a garin Makkah da kewayenta, wato nesansu da garin Makkah bai kai mil 48 ba. To amma a aikin Hajjin bakance, ko na mustahabbi, ya halatta ga mazaunin Makkah da wanda ke nesa da Makka ya zabi duk aikin Hajjin da ya ga dama tsakanin raben-raben da aka ambata a sama.
To bisa la’akari da cewa aikin Hajjin Tamattu’i shi ne wajibin mafiya yawa mutane, musamman mutanenmu, don haka za mu yi bayani ne kan wannan nau’i na aikin Hajji.

Ga yadda ake yin Umurar Tamattu’i: Da farko mutumin da ya yi niyyar yin aikin Hajjin Tamattu’i zai fara ne da daura harami a daya daga cikin wararen da ake daura haramin guda biyar, ko kuma abin da ake ce wa ‘mikati,’ wato: 

(1) Zul Hulaifa 

(2) Akik 

(3) Juhfa 

(4) Yalamlam 

(5) Karnil Manazil.


1. Harami: Shi ne sanya kyallen tufafin nan guda biyu da Alhaji zai sa yayin aikin Hajjin. 

Yadda ake daura harami shi ne: Mutum zai yi niyyar yin harami da Umurar Tamattu’i na Hajjin wajibi, sannan ya sanya tufafin haraminsa guda biyu, zai daura guda, ya kuma yafa guda, wato ya yi mayafi da shi. Daga nan sai ya fara ‘talbiyya’ wato fadin: Labbaikallahumma labbaik, labbaika la sharika laka labbaik, innal hamda, wan ni’amata laka wal mulk, la sharika laka. To idan mutum ya yi haka ya zamanto muhrimi (wanda ya daura harami) kenan da aikata wasu abubuwa suka haramta masa kamar su kusantar mace, shafa turare, sanya kewayayyen tufafi ga namiji, farauta da makamantansu. Akwai kuma wasu ayyuka na mustahabi da ake so mutum ya aikata, misalin yin wanka kafin daura harami da makamantan hakan. 

2. Dawafi: Abu na biyu cikin aikin Umrar Tamattu’i shi ne Dawafi, wato kewaya Dakin Ka’aba. Yadda kuma ake yin sa shi ne: Mutum zai fara da yom niyyar Dawafin Umurar Tamattu’i ne,sai ya fara zagaya Dakin Ka’aba har sau bakwai, zai fara ne daga inda Hajrul Aswad yake, wato Dakin Ka’aba na hannunsa na hagun. Idan ya fara daga wajen Hajrul Aswad ya zagayo ya zo wajen da ya fara, to ya yi guda kenan, haka-haka har sau bakwai.

3. Sallar Dawafi: Idan mutum ya gama dawafi wato ya kewaye Dakin sau bakwai, sai ya yi sallar Dawafin raka’a biyu a Makama Ibrahim. Wannan shi ne wajibin Umura ta Tamattu’i.

4. Sa’ayi: Wajibi na hudu shi ne Sa'ayi, wato tafiya tsakanin Safa da Marwa, yadda ake yin ta kuwa shi ne: Mutum ya yi niyyar yin Sa'ayi na Umrar Tamattu’i na Hajjin wajibi, sai ya fara tafiya daga Safa ya zo Marwa, daya kenan, sannan daga Marwa ya zo Safa, biyu kenan har sau bakwai. Wato tafiya daga Safa zuwa Marwa sau hudu, daga Marwa kuma zuwa Safa sau uku, wanda karshen tafiyar za ta kare ne a Marwa.

5. Aski: Wajibi na biyar kuma na karshe a Umurar Tamattu’i shi ne: Aski, ko kuma saisaye, mutum ya aske wani abu daga cikin gashin kansa ko gemunsa, ko gashin bakinsa, ko kuma ya yanke farcensa. Da hakan ne ake kare aikin Umurar Hajjin Tamattu’i, wanda hakan na nufin kenan dukkan abubuwan da aka haramta masa saboda harami a halin yanzu ya halatta a gare shi, misali kusantar mace, sanya turare da sauransu. Daga nan sai mutum ya jira lokacin daura haramin Hajjin Tamattu’i.

HAJJIN TAMATTU'I: 

Ayyukan Hajjin Tamattu'i Su ne: 

1. Saka harami a Makka.

2. Tsayuwa a Arafa.

3. Tsayuwa a Mash'arul Haram.

4. Jifan Jamratul-Akaba (jifan shaidan).

5. Yin hadaya.

6. Aske gashin kai ko rage shi.

7. Kwana a Mina a dare na sha daya.

8. Jifan jamrori(shedanu) uku a rana ta sha daya.

9. Kwana a Mina a dare na sha biyu.

10. Jifan jamrori (shedanu) uku a rana ta sha biyu.

11. Dawafin hajji.

12. Sallar dawafi.

13. Sa'ayi (Safa da Marwa).

14. Dawafin mata.

15. Sallar dawafi.

HUKUNCE - HUKUNCEN HAJJIN TAMATTU'I

An shardanta wa hajjin tamattu'i abubuwa kamar haka:

Na daya: Niya, ita ce nufin aikata irin wannan nau'in hajjin yayin daura ihramin umarar. Idan ba haka ba, bai inganta ba.

Na biyu: Ya zama umrar da hajjin ya yi su a watannin aikin hajji.

Na uku: Tilas ya yi hajji da umrar a cikin shekara guda.

Na hudu: Ya zama mai yin hajjin da umrar mutum guda ne.

Da zai dauki hayar mutum biyu su yi wa mamaci hajjin tamattu'i, watau daya ya yi umra dayan kuma ya yi masa hajjin, bai isar masa ba.

CIN RUBA TANADIN YAKI DA ALLAH DA MANZON SANE

Cin Riba Tanadin yaki da Allah da Manzon sane
Daga Auwal Zakari Ayagi

Da suna Allah mai Rahama mai jinkai, tsira da aminci sukara tabbata ga fiyayyen halitta cikamakin Annabawa, shugabannin manzanni, tare da sahabbansa da suka taimaka masa wajen kafuwar  addini, da Ahalin gidansa da matayensa da dukkan wadanda suka bishi da kyautatawa har zuwa ranar Alkiyama.

Bayan haka Ubangiji mai girma da daukaka yana fada cikin Alkur’ani mai girma:

{ یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ ٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَذَرُوا۟ مَا بَقِیَ مِنَ ٱلرِّبَوٰۤا۟ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِینَ (278) فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُوا۟ فَأۡذَنُوا۟ بِحَرۡبࣲ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۖ وَإِن تُبۡتُمۡ فَلَكُمۡ رُءُوسُ أَمۡوَ ٰ⁠لِكُمۡ لَا تَظۡلِمُونَ وَلَا تُظۡلَمُونَ (279) }

[Surah Al-Baqarah: 278-279]

Ma'ana

“YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KUJI TSORON ALLAH KU BAR ABIN DA YAYI SAURA DAGA RIBA IN KUN KASANCE MUMUNAI, IN HAR BAKU AIKATABA (barin cin ribar) INA MUKU IZINI DA YAKI DA ALLAH DA MANZONSA, IN KUKA TUBA ASALIN DUKIYARKU NA GAREKA BAKU YI ZALUNCI BA BA’A ZALINCE KUBA”  (Bukara Aya ta 272-279)
Wannan aya tana tsoratar damu game da Mu’amala da Riba, inda Allah da kansa yake cewa duk wanda bai bar cin Ruba ba yana masa izinin yin yaki dashi da Annabinsa (SAW), kamar yadda yazo a labari cewa: Ranar Alkiyama Ubangiji zai bawa masu cin Ruba makami ya umarce shi da yayi yaki da shi, Allah ya kiyayemu, Allah yace: amma in kuka tuba to sai ku debi asalin Dukiyarku (jarinku) ragowar kudin sai ku rabar in kukai haka bakuyi zalunci ba kuma ba’a zalunce kuba.

Menene Ruba?
Ruba tana nufin dadi abisa abubuwa da kebantar Karin kudi

Rabe-Raben Ruba
Ruba ta kasu izuwa kashi biyu wato:
* Rubar Dadi
* Rubar jinkiri

* Rubar Dadi: Rubar dadi tana nufin cinikin jinsi daya kamar (Gero da Gero, Dawa da Dawa, Naira da Naira da sauransu) amma tare da dadi akan cinikin, kamar asayi Gero kwano daya amma sai ace sai ka dada rabin kwano akan kwano dayan, ko sayan sababbin kudi, misali na Naira dari biyar amma ace sai an dada Naira Hamsin akai, da sauransu.

* Rubar Jinkiri: Rubar jinkiri ta kasu kashi biyu,:
* Ruba Ninkawa
* Ruba mai daduwa don dogon lokaci.

Ruba mai ninkawa: Ruba mai ninkawa itace ake cewa Rubar Jahiliyyah, wannan itace ubangiji ya haramtata da nassin Alkur’ani mai girma, inda yake cewa: “YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KADA KUCI RUBA NINKIN-BANINKIN: (Ali Imram Aya ta 130).

Yanda wannan Ruba take, Shine a baiwa wani bashi zuwa wani lokaci abin ayyanawa, idan lokacin yayi bai samu damar biya ba, sai ace dashi ko ya biya ko kuma a karamasa kudi sannan a kara masa lokacin biyan, haka za’a rika karamasa kudi ana karamasa lokacin biyan, har kudin sun ninninka kansu.

Misali kan wannan shine kamar bashin da kasashe suke ciyowa bisa yarjejeniyar zasu biya zuwa Shekarun da aka ayyana, idan lokacin yayi basu biya ba, sai kudin suyi ta karuwa gwargwadon tsowon lokacin da kasar tayi bata biyaba, sai aga kudin sun ninka kansu ninkin ba ninkin. To wannan itace Rubar da wannan aya take Magana akai.

Ruba mai daduwa don dogon Lokaci; Wannan itace Rubar da ake bada bashi da kari don bashin zai dauki dogon lokaci, misali: abada bashin naira Dubu daya amma za’a biya dubu da dari daya a tsawon kwanaki ishirin.
Ko sayen wani abu da kari kan asalin kudin sa don daukan dogon lokaci, misali sayen Sha’ir ko Dabino ko kwaya kamar wake, masara, gero da makamantansu, amma da Karin kudi in zai kai wani lokaci, misali: ana sayar da Masara Naira 300 a ko wacce kasuwa, sai abada ita bashi akan Naira 350 don za'a biya a watanni biyu, ko biya biyu ga ma’aikata, da makamantansu.

HUKUMCIN RUBA
Ita dai Ruba haramunce, sabo da fadin Ubangiji madaukakin sarki cikin suratul Bakara Ayata 275 cewa:
“Allah ya halatta ciniki ya haramta ruba”
Da fadinsa “YAKU WADANDA KUKAYI IMANI KADA KUCI RUBA NINKIN-BANINKIN: (Ali Imram Ayata 130).

Ga kuma fadin Annabi Alaihissalam cewa:

1. “Allah ya tsinewa mai cin Ruba da wakili akan Ruba da masu shaida akan Ruba da marubucin Ruba” (As-habu Sinan)

2. “Sisi na Ruba da mutum yake cinsa yana sani shi yafi tsananin Azaba da Zina Talatin da mutum zaiyi" (Ahmad da Hakim)

3. “Ruba kofa Saba’in da Uku ce mafi saukinsu shine mutum ya auri mahaifiyarsa" (Hakim)

4. "Ku nisanci abubuwa bakwai mafiya ukuba, sai akace yarasulullahi menene? Sai yace: Yin tarayya da Allah, da sihiri da kashe ran da Allah ya haramta da cin Ruba, da cin dukiyar marayu da juya baya (Guduwa) Ranar yaki, da yin kazafi ga mumina katangaggiya” (Buhari da Muslim) 

UKUBAR MASU CI RUBA
Ubangiji madaukakin sarki yafada cikin Suratul Bakara Ayata 275:

“Wadannan da suke cin Ruba basa tashi (yayin tashi daga kaburbura) sai kamar misalin wadanda shaidanu suke bubbugewa (tashin su kamar na masu fyarfyadiya) da shafa (ta Aljanu) wadannan don cewa su suna cewa shi ciniki kamar Ruba ne”.

Idan Ubangiji ya tashi mutane ranar Alkiyama zasu fita suna masu gaggawa, sai masu cin Ruba su zasu tashi suna faduwa kamar masu fyarfyadiya, don cewa su yayin da suke cin Ruba Ubangiji yana tarata a cukkunansu har ta rinjayesu ranar Alkiyama duk yayin da suka tashi sai su fadi, suna son suyi gaggawa kamar sauran mutane amma baza su iyaba.

Katadatu yace Mai cin Ruba za’a tasheshi ranar Alkiyama yana mahaukaci.
An karbo daga Abi Sa’idul Khudri (RTA) cewa Manzon Allah (SAW) yace yayin da akai Isra’i dani, na shude ga wasu Jama’a cukkunansu yana gabansu ko wane mutum cikinsa kamar katon gida, cikin nasu yana karkatar dasu suna masu kururuwa a bisa kwararowar azabar Jama’ar Fir’auna ana bijiro musu da azaba safe da yamma, sai yace: sai a bijiro musu da Azaba kamar misalin gudajjen Rakumi basaji basa gani, yayin da wadannan masu cukkunan sukajisu sai su tashi, amma sai cikkunansu su rinjayesu bazasu iya tashi ba, har sai jama’ar fir’auna sun samesu sai subi ta kansu, suyi gaba dasu suyi baya da su, haka za’ai ta yi musu wannan Azaba. Sai Ma’aikin Allah yace su wnene wadannan ya dan’uwa Jibrilu? Sai yace sune masu cin Ruba.

An karbo daga Ibn Mas’ud daga mahaifinsa cewa: Idan zina da Ruba suka bayyana a Alkarya, sai Ubangiji yayi izinin halakar da ita.

Manzon Allah (SAW) yace: Ruba bazata bayyana a al’umma ba face hauka ya bayyana  a cikinsu. Zina bazata bayyana ga Al’umma ba face Mutuwa ta bayyana a garesu, Al’umma baza su tauye ma’auni da mudu ba face Allah ya hana su ruwan sama.

Har ilayau Manzon Allah Alaihissalam yace: Jama’a hudu Allah bazai shigar dasu Aljanna ba, ba zasu dandani Ni’imarta ba.
i. Mai narka Giya
ii. Mai cin Ruba
iii. Mai cin dukiyar marayu bada hakki ba.
iv. Mai sabawa iyayen sa.

An karbo daga Abubakar Siddik (RTA) yace: Mai dadi da wanda aka dadawa yan wuta ne, (ma’ana Mai bada Ruba da mai karbarta)

Wadannan Ayoyi da Hadisai suna nuna girman laifin Ruba, da irin Azabar da zata riski masu mu’amala da ita, da kuma mahimmancin barinta.

HIKIMAR HARAMTA RUBA
Haramcin mu’amala da Ruba na dauke da hikima kamar sauran ibadu, an haramta ta ne sabo da jarraba imanin bawa don ganin yayi biyayya a cikin aikatawa ko cikin hani, sannan yana daga cikin haramcin Ruba:

* Kiyaye wa abisa dukiyar Musulmi, don kada yaci dukiya yana mai barna.
* Fuskantowar musulmi cikin yaduwar dukiyarsa cikin hali madaukaki ba tare da cutar da sauran musulmi ba, cikin sana’arsa da Moman sa da Kasuwancin sa da sauransu.
* Toshe hanyoyin masu sa kiyayya ga musulmi, domin kiyayya ga musulmi tana wahalshe shi, sababinta kuma abin hani ne.
* Tseratar da musulmi bisa ga abin da zai kaishi ga halaka don cin Ruba zalunci ne kuma halakane.
* Bude kofofin biyayya ga musulmi don suyi guzuri sabo da lahira.

KAMMALAWA
Kamar yadda muka karanta Ayoyi da Hadisan Manzo Alaihissalam masu hani ga yin mu’amala da Ruba, don haka ya zama lallai a garemu da mu barta, domin in har bamu barta ba abubuwan da Allah zai yiwa musu mu’amala da ita lallai zasu tabbata ga masu mu’amala da ita daga cikin mu, domin  a yau akasarin mu’amalarmu da Ruba a ciki, a Bankuna ne, ko a Kasuwanni, ko a wuraren ayyukanmu na yau da kullum, ada mutum sai dai shi da kansa yakai kansa wajen mu’amala da Ruba, Amma a yanzu biyoshi ake har wajen kasuwancinsa ko wajen aikinsa ana tura masa bashi mai dauke da Ruba, tare da yi mata kwaskwarima, don haka ya zama wajibi mu rika tantancewa tsakanin cinikayya (Kasuwanci) da Ruba.
Domin zakaji wasu suna cewa ai lalurace tasa ni karbar bashin Banki mai dauke da Ruba don babu yanda zanyi, ko a’a gidana zan karasa ginawa, ko abin hawa zan siya da makamantan haka, to shima Ubangiji a lalurar zai hukun ta shi sabi da mu;amalar da yayi da Rubar.

Dafatan Allah Ta’ala zai datar damu, ya tsarkake mana hanyoyin neman mu daga Ruba da makamantanta, ya shiryar damu ya karamana tsoronsa da biyayya agareshi, ya karamana Lafiya da zaman Lafiya da kwanciyar hankali a garunmu da sauran garuruwan musulmi. Allah ka kara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi Muhammad da ahalin gidansa da dukkan sahabbansa, da wadanda suka bishi da kyautatawa har zuwa ranar karshe.

Alhamdulillah.

Auwal Zakaria Ayagi

Takaitaccen Tarihin Salman Alfarisi Allah yakara Yarda a gareshi

Tarihin Sahabi Salman Farisi (RTA)
Daga Auwal Zakari Muhammad Ayagi
Shugaban kungiyar Alazmiyyah Islamic Foundation

Takaitaccen tarihin sahabin Manzon Allah (SAW) mai girma wato Salman Farisi, to wasu ruwayoyi na tarihi sun bayyana cewar an haifi Salman al-Farisi ne a shekara ta 568 miladiyya ko kuma kusa da haka a wani gari na kasar Farisa da ake kira Jiyye da a halin yanzu yake kusa da garin Isfahan (a Iran). Asalin sunansa shi ne Rozeba, sai dai daga baya, bayan musuluntarsa Manzon Allah (s.a.w.a) ya sauya masa suna zuwa Salman, an ce a wasu lokuta a kan kira shi da Abu Abdullah. Mahaifin Salman dai attajiri ne sanann kuma mai fadi a ji a garin nasu da kewayensa. To sai dai duk da arzikin da yake da shi, Salman shi ne dansa kawai, don haka yake tsananin kaunarsa. A wancan lokacin mafi yawan al'ummar Farisa suna bin addinin bautan wuta ne, don haka cikin wannan addini ne Salman ma ya taso, inda mahaifinsa ya ware wasu malamai don koyar da shi akidu da koyarwar wannan addini, ta amma sakamakon irin hazakar da yake da ita ya zamanto ya sami ilmi mai yawan gaske sama da malaman da suke koyar da shi. A wancan lokacin babban abin alfahari ne ace mutum ya zamanto daya daga cikin malaman addini kuma mai hidima wa daya daga cikin dakunan bautan wutan a kasar Farisan, hakan na kawo wa mutum daukaka da girmamawa. Don haka ne mahaifin Salman yayi kokarin ganin dansa ya zamanto daya daga cikin irin wadannan mutane tun yana dan shekara sha shida a duniya. Salman yayi shekaru uku yana aiki a dakin bautan wuta na Jiyye, to sai dai ba a jima ba sai ya fara kosawa da wannan aiki da malaman dake karantar da shi saboda kasantuwansu mutane masu karancin tunani da ilimi. A mafi yawan lokuta ba sa iya amsa tambayoyin da yake musu ko kuma su ba shi amsa maras gamsarwa. Don haka tun daga lokacin ya fara tunanin yadda zai sami wata mafita. Salman ya fara samun damar ficewa daga wannan addini ne lokacin da mahaifinsa ya tura shi wani gari don ya wakilce shi a wajen. A hanyarsa ta zuwa wannan gari ne ya ci karo da wasu ma'abota addinin kirista da suka fito daga kasar Siriya, inda suka yi masa bayanin akidun addininsu, daga karshe dai Salman ya zama Kirista. Bayan da ya dawo gida, Salman ya shaida wa mahaifinsa ganawarsa da wadannan kiristocin da kuma karbar addinin kiristancin da ya yi. Hankalin mahaifin Salman ya kara tashi kwarai, nan take ya bukaci ya yi da wannan sabon addini amma Salman yaki, don haka sai ya sa aka ta dukansa aka kuma tsare shi kwana da kwanaki ba tare da abinci ko ruwan sha ba. Bayan zama a gidan yari na wani lokaci, Salman ya samu nasarar tserewa daga inda ake tsare da shi ta hanyar taimakon daya daga cikin bayin babansa mai suna Mehran wanda yake tsananin kaunar Salman saboda shi yake kula da shi tun yana yaro. Bayan da ya gudu Salman ya koma wajen wadannan kiristocin inda su kuma suka tura shi kasar Siriya tare da wani ayari. A lokacin da ya isa kasar Siriyan a nan ma ya ci gaba da karatu da neman ilimi ta haka ne ya tara dimbin ilimi mai yawa. To sai dai a wannan karon ma ya sake shiga wata damuwar, yana jin cewa lalle abin da yake kai ba shi ne hakikanin gaskiya ba, akwai gaskiya ta hakika da har yanzu bai same ta ba. Lokacin da wannan tunani ya dame shi sosai sai ya mika komai ga Allah Madaukakin Sarki Yana mai addu'ar cewa Allah Ya nuna masa hakikanin gaskiya. Allah Mai karban, Salman bai san cewa ya kusa kai wa ga gaskiyar da yake bukata ba. . Bayan da ya bar garinsu Salman ya zauna a kimanin garuruwa guda hudu, gari na karshe da ya zauna shi ne Ammuriya dake karkashin daular Rumawa. A nan ne a karon farko ya sami labarin bayyanar wani Annabi a garin Makka da yazo da sakon bautan Allah Shi kadai da yin watsi da bautan gumaka. Nan take Salman ya fara tunanin cewa watakila wannan haske da ya bayyana a Makka shi ne shiriyar da yake bukata. Don haka ya fara shirye-shiryen tafiya Makka don ganawa da wannan sabon Annabi don jin ta bakinsa. To sai dai a hanyarsa ta tafiya Madina nan ya fuskanci matsala inda ayarin 'yan kasuwan da yake tare da su suka ha'ince suka sayar da shi ga wasu yahudawa. Su ma wadannan yahudawan sai suka sayar da shi ga wani attajiri mutumin Madina wanda yake zuwa wajen don kasuwanci. Duk da irin wahalhalun da ya fuskanta a matsayin bawa a Madina amma hakan bai hana shi ci gaba da binciken yadda zai sadu da Manzon Allah (s.a.w.a), duk da cewa a lokacin Manzo bai riga da ya yi hijira zuwa Madina ba. Wata rana Salman yana cikin aiki sai ya ji mai gidansa yana tattaunawa da wani mutum wanda yake bayyana masa cewa Manzon Allah (s.a.w.a) ya yi hijira zuwa garin Yathrib (Madina), nan take Salman ya fara tunanin yadda zai sami damar ganawa da wannan Annabin. Wata rana kuwa sai mai gidan nasa ya yi tafiya don haka sai ya nufi gidan Abu Ayyub al-Ansari (r.a) wanda Manzon Allah (s.a.w.a) yake zaune a gidansa a lokacin. Ko da suka yi ido biyu da Manzon Allah (s.a.w.a) nan take sai ya ji zuciyarsa ta cika da kaunar wannan Annabi yana gaya wa kansa cewa lalle wannan mutumi ba makaryaci ba ne. Bayan wani lokaci na tattaunawa a tsakaninsu, Salman ya karbi Musulunci, yayi imani da cewa babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Muhammadu bawansa ne kuma ManzonSa. A nan ne Manzon Allah (s.a.w.a) ya sake masa suna zuwa Salman, wanda da hakan ne aka sanshi tsawon tarihi. Tun daga wannan lokaci Salman ya ci gaba da zuwa wajen Ma'aiki (s.a.w.a) a kai a kai. Da haka ne Salman ya cimma burinsa, wato ya samu tafarkin da zai amsa masa tambayoyin da yake da su da magance masa matsalolin da yake fama da su, baya ga samun darajar kasancewa daya daga cikin sahabban Ma'aikin Allah (s.a.w.a). Matsala guda da Salman yake fama da ita, ita ce bautan da ya ke yi don shi bawa ne. Don haka wata rana Manzon Allah (s.a.w.a) ya bukaci mai gidan Salman ya sayar masa da shi don ya 'yantar da shi daga bauta. Mai gidan Salman ya kafa sharadin cewa wajibi ne Salman ya shuka masa bishiyar dabino 300 sannan kuma ya biya oza arba'in na zinare a matsayin kudin fansarsa. Lokacin da Salman ya gabatar wa Manzon Allah (s.a.w.a) da wannan bukata ta mai gidansa, sai Manzon Allah (s.a.w.a) ya juya ga sahabbansa ya ce musu: "ku taimaki dan'uwanku". Nan take Sahabbai suka mike suka hada wadannan bishiyoyi da bayahuden yake bukata, sannan Annabi (s.a.w.a) ya bukace su da su tona ramukan da za a shuka su, bayan da aka gama tona ramin sai Manzo (s) ya zo da kansa ya shuka bishiyar farko sannan sauran sahabbai suka biyo sahu. To an gama shuka bishiyoyi amma abu guda ya rage shi ne zinare, don haka har ya zuwa yanzu Salman yana a matsayin bawa. Bayan wani lokacin kuma Manzon Allah (s.a.w.a) ya tara wadanann zinare da ake bukata inda ya ba wa Salman don ya kai wa mai gidansa don cika wannan sharadi na 'yantar da shi. Ta haka ne Musulunci ya ‘yantar da Salman Al-Farisi. Daya daga cikin gagarumar hidimar da Salman yayi wa Musulunci shi ne lokacin da kafiran Makka suka shirya makircin kawo hari birnin Madina da mamaye shi gaba daya. A wannan lokaci ne Salman ya ba wa Ma'aiki (s.a.w.a) shawarar a tona rami mai zurfin gaske a kewaye garin Madina da shi don hana makiyan shigowa. Bayan gama tonun ramin sahabbai sun yi farin ciki da jinjina wa Salman kowani bangare naso ya janyo shi zuwa ga bangarensa, hakan ne ma ya sanya wani daga cikin Muhajirai (mutanen Makka da suka yi hijira zuwa Madina) ya ce: "Salman daya ne daga cikinmu mu Muhajirai", nan take sai wani Ba'ansare (mutumin Madina) ya yi caraf yace: ‘A'a Salmanu daya ne daga cikinmu, mu Ansarawa". Haka dai aka ci gaba da kace nace tsakanin bangarorin biyu. Bayan wani lokaci sai ga Manzon Allah (s.a.w.a) ya iso, yayin da yaji su suna wannan musu, sai yayi murmushi ya kawo karshen musun da cewa: "Salmanu ba Muhajiri ba ne ba kuma Ba'ansare ba ne, Salman yana daga cikin(mu) Ahlulbaiti". Wannan babban matsayi ne da Manzon Allah (s.a.w.a) bai taba ba wa wani mutum in ba Salman ba, wato Salmanu ya zamanto daga cikin Ahlulbaitin Manzon Allah (s.a.w.a), zababbiyar zuriya daga wajen Allah Madaukakin Sarki. A tarihin Musulunci babu wani mutum da ya taba samun irin wannan gagarumin matsayi in ba Salman al-Farisi ba. Salman al-Farisi ya bar duniya ne yana da shekaru 88 a duniya. Salman al-Farisi ya rasu ne a lokacin halifancin Sayyadina Ali (RTA) a garin Mada'in, wajen da Sayyadina Ali ya nada shi a matsayin gwamnan wajen.